Arziki Rabo Book One Complete Hausa Novel
By Khalisat Haidar★ Gold
Book Page

Arziki Rabo Book One Complete Hausa Novel

Author: Khalisat Haidar★ Gold
Paragraphs: 3953
Starting position: 1
Reading position: 1 / 3953
Listen Mode
Login and upgrade to premium to unlock listening.
Reader Top
Ad slot ready: reader_top

 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

*Assalamu Alaikum ,we met again a wannan sabon littafin nawa mey suna ARZI'KI RABO Allah ubangiji yasa na kammala lafiya,ina wa masoyana fatan alkairi we are together always and forever💕*

*Note:fiction*

   *Dedicated to our mothers*

         🅿 0⃣1⃣

     *Kano* 

Gidane madedeci d'aki biyu yake d'auke dashi tsakar gidan ma ba wani fad'i gareshi ba.Sede ba lefi gidan ya tsaru ga shafe da akai hakan ya nuna alamar ba a dad'e da tarewa ba.Cikin sitting room kuwa yanda aka ziba kujeru masu tsada ba za'ace a wannan gidan suke ba d'akin gado ma haka furnitures ne tsadaddu d'akin kansa da'kyar ya iya d'aukan gado ,wardrobe se a d'ayan d'akin aka sa.

      Wata mace na gani a d'akin wadda ke zaune kan kujerar mirror tana tsara d'auri ,mashaAllah kallo d'aya zakai ka gano kyau da take dashi ,fara ce amma ba irin tass d'innan ba gata da hanci dogo haka girarta ma sirira lips nata yasha maroon janbaki ga earings da necklace nata masu stones green,tana sanye da atamfa green me d'auke da ratsin orange da black .Kayan jikin nata sosai sun d'auketa chif a jikinta,koda ta mi'ke bayan ta kammala d'auri na lura da tsahonta medium ce domin baza a kirata gajeriya ba haka baza a kirata doguwa ba  gashi batada 'kiba .

     Wayarta ta d'akko dake kan gado ,call log naga ta shiga inda tayi dialing suna "My Dear".Ba jimawa akai answering ta d'ayan 'bangaren " My Azizaty" aka fad'a.

      "Dear naji shiru baka taho bane?" Ta tambaya murya 'kasa-'kasa.

      "Azizaty sorry! Umma ce ta tsayar dani kinga amma yanzunnan zaki ganni". Ya fad'a.

     " Toh shikenan kagaida min ita".Ta fad'a.

     "Yawwa my azizaty sena dawo".Ya fad'a.

     Bayan ta katse wayar ne tayi hanging tare da sakin murmushi ,fuskarta ta sake kalla jikin mirror d'in sannan ta fita daga d'akin.

     Bayan like 10minute tana zaune a sitting room ta jera tray da sauran jug da cup ga warmers a kai ,tana danne-danne a wayarta tajiyo knock. Ba 'bata lokaci ta tafi bud'e 'kofar ,koda ta isa soron ta jiyo muryarsa yana waya lalla'bawa tayi ta bud'e 'kofar da sauri ta la'be bayan 'kofar.

    Yana shigowa kafin yayi wani motsi yaji an rufe masa ido da tafin hannu ,jin 'kamshin turarenda ke sanyaya masa rai yasa yayi saurin sakin murmushi.

     " Azizaty! "Ya kira sunanta.

     " Na'am Dear sannu da dawowa".Ta fad'a bayan ta sauke hannunta.

        "Wow! Azizaty irin wannan kyan haka ai seki sa na kasa shiga ciki". Ya fad'a harda zaro ido.

      Wani murmushi ta saki wanda ya sake bayyana kyawunta." Toh ka taimaka mu shiga".Ta fad'a.

     Hannunsa cikin nata suka 'karasa har d'aki."Dear wanka zaka fara yi ko abinci zaka ci tukun?" Ta tambaya tana jiran amsarsa.

      "Duk wanda kika za'ba min Amarya ta" Ya amsa.

     "Toh na za'ba ,ka fara yin wanka".Ta amsa.

     Da kanta ta tayasa rage kayan ya shiga wankan,cikin 'yan mintina 'kalilan ya fito.Shirinsa yayi cikin T-shirts fara se jeans blue ,sosai yayi kyau.

    Ahmad mutum ne me tsaho gashi fari ne wanda yama d'ara ta, baida 'kiba sede ba siriri bane yana da murd'ewar jiki dede.Wajen kyau ma ba abarsa ba tsakanin shi da ita banga wanda zai nuna wa wani kyau ba sede fari daya d'areta.

      " Harka gama shirin?" Ta tambaya lokacinda ta shigo d'akin.

   "Iyye Azizaty baki taya niba ina kika shiga?"

    "Daga shigarka toilet nayi ba'ki" Ta amsasa.

    "Ba'ki? Toh yanzu ya za'ai dani?" Ya tambaya kamar wani yaro 'karami.

    Yadda yayi maganar ne yasata murmusa "Nasanki kina yin ba'ki zaki shareni". Ya fad'a.         " A'a bazan shareka ba bari na kawo ma abincin d'akin".Ta furta.

    Sitting room d'in ta shiga ta d'akko abincin ta mayar d'aki,su kuwa ba'kin ta d'ebo masu wani a kitchen. Koda yaga ta dawo d'akin ya tamabayeta"Ba'kin naki fa?"

    "Yara ne fah kuma na zuba masu abincinsu ". Ta amsa.

    " Ok ".Ya fad'a.         Zama yayi a kan sallayar data shimfid'a ,yana kallo ta gama zuba abinci tasa spoon." Dear na zuba ma".Ta fad'a.

     "Toh se yaya kenan?" Ya tambaya yana kallonta.

      "Se ci". Ta amsa.

      " Nikuma hannuna baze iya chiba".Ya fad'a.

    Yana fad'ar haka ta gane me yakeke nufi,da kanta ta d'auki spoon d'in ta fara basa. "Ke fah baza kici bane?"

    "Ni ai naci nawa". Ta amsa.

    " Kefa kika ce zaki jirani mici tare".

    "Toh ba kaine ba se 3 ka dawo". Ta fad'a cikeda shagwa'ba.

    Tana birgesa idan tayi hakan ,kallonta kawai ya tsaya yi " Ayya my Azizaty sorry nima nafiso mike ci tare ".Ya fad'a tare da tallafo ha'barta.

     "Yawwa dear shine baka bari minje wajen umma ba tare koh kayi min wayo". Ta fad'a.

      " Kinsan nikaina bansan zanje ba,ina makaranta umma tayi mini waya wasu 'yan uwanta daga zaria sunzo shine fa naje muka gaisa".Ya fad'a.

     "Ayya da ka kawosu nan mun gaisa".

     " Ai ba kwana zasi ba ba lokaci da na kawo su".Ya fad'a.

      A haka tana bashi suna hirarsu har ya 'koshi,bayan data gama had'a kwaninka takai kitchen ta koma wajen yaran da suka zo.

        Wannan ma'aurata Reyhana da Ahmad sun kasance masu 'kaunar junansu,kafin suyi aure seda aka kai ruwa rana.Mahaifiyar Reyhana fafur ta'ki yarda Ahmad ya auri 'yarta ,ba wani dalili bane illa saboda talaka ne ,da'kyar mahaifin Reyhana ya tsawatar mata haka bataso ta ha'kura akai auren.Ahmad  tun yana 'karami mahaifinsa ya rasu,se dangin mahaifiyarsa ne da'kyar suka d'auki nauyin karatunsa na secondary dan dangin mahaifinsa basuda hali sosai kuma duk cikinsa kowa ya'ki d'aukan nauyin sa.A haka bayan ya gama secondary school yana 'yan bige-bige ya shiga college yayi diploma.Kasancewar halin rayuwa da ake ciki da'kyar ya samu aiki a wata private yake teaching albashinsa ba yawa gareshi ba kunsan private school. Koda yazowa da umma mahaifiyarsa zancen auren Reyhana da farko bata goyi baya ba dan tasan Reyhana ta kere masa, yarinya ce data taso cikin gata ,iyayenta masu kud'i ne gasu 'yan boko. Haka yasa Umma ta tsorata,ganin Ahmad ya'ki ha'kura kuma taga irin son da Reyhana ke masa yasa ta ha'kura ta bisu da addu'a.Momyn Reyhana kuwa da danginta sun tsani auren ,Abbanta ne kawai ya goyi baya, toh wannan kenan.

   Around 8:18pm bayan ya dawo daga masjid ,a d'aki ya isketa ."Azizaty am back ".Ya fad'a tare da zama kan gadon gefenta.

     " Sannu da dawowa". Ta fad'a tana murmushi.

     "Yawwa ". Ya fad'a tare da d'ora kai a cinyarta ya kwanta.

      "Ya labarin school d'in?" Ta tambaya.

     "Azizaty d'alibai rashin ji suna chaza min kai".Ahmad ya fad'a tare da ri'ko hannunta ya d'ora kan cikinsa.

      " Allah Sarki dear gashi kaikuma baka son hayaniya".Reyhana ta fad'a d'ayan hannun nata tana shafa kan sumarsa dake d'auke da gashi yale-yale na Fulani d'innan gashi ba'ki.

     Hakan yasa ya rintse idanunsa kamar me barci."Yes Azizaty dad'inta ma ina dake kinga kece me kwantar min da hankali a kodayaushe that's why kullum position naki a 'kalbi na 'karuwa yake".

    Murmushi ta saki wanda hatta ha'korinta seda ya bayyana ,tana jin dad'in kasancewa da mijinta ita kad'ai tasan halin abinta se Umma kankat ,Reyhana tasan Ahmad d'inta da rashin magana cikin jama'a amma ita a gunta daban ne tasan yadda zata bi dashi.

     "Yaushe toh za'a tsayar da ranar zuwa wajen Umma mu gaisheta?" Ta tambayesa.

     Shiru taji be amsa ba,data kalli fuskarsa kuwa taga yayi bacci ma.D'an murmushi ta saki, wayar ta dake gefe ta d'auka tayi ta 'kyasta masa photo. Itama daga baya baccin ta soma ji ,a hankali ta shafa fuskarsa."Dear 9:30 yayi ka gyara kwanciyar kar wuyanka ya 'kage".Ta fad'a a hankali.

      Kasancewar baida nauyin bacci yasa ya farka"Azizaty amma de 'kafanki beyi tsami ba koh?"

      "Uhmm beba". Ta amsa.

Tashi yayi daga kwanciyar " Toh kema kiyi shirin kwanciya mu kwanta yanzu kema da wuri zaki kwanta".Ya fad'a.

     Tashi tayi ta fad'a toilet dake d'akin tayi wanka tukun bayan ta fito ta sanya sleeping dress,shima already yayi shirin kwanciya."Azizaty let sleep".Ya fad'a tare da mi'ka mata hannu.

     Mi'ka masa nata tayi ,yana sani ya janyo ta ta fad'o jikinsa."Kai Azizaty kinyi nauyi dayawa kinjiki kuwa".Ya fad'a cikeda tsokana.

      "Nid'in ce nayi nauyi". Ta furta tana gyara kwanciyarta.

      " To shiru a kwanta".Ya fad'a tare da kashe light d'in ya jawota jikinsa sannan ya jawo blanket ya rife.

       "Sleep tight". Ya fad'a.

        " Uhm". Ta furta.

     Ba dad'ewa bacci ya kwashesu duka.

                  ****

    Washegari kamar ko yaushe 5:30am sun tashi ,ko Reyhana tayi sallah bata komawa bacci seta ga fitarsa,ita take tayasa shiryawa tayi  breakfast.

       "Azizaty! " Ya kira sunanta .

     Tana kitchen ta taho"Dear kirana kake?"

       "Eh Azizaty kinga wani littafi ajje a kan drawer?" Ya tambayeta .

      Kad'a masa kai tayi tareda nufar inda drawer d'in yake. Jawo drawer d'in tayi  sanannan ta ciro littafin.

     "Gashinan". Ta mi'ka masa.

      " Thanks my wife". Ya fad'a yana murmushi.

       Tana birgeshi yadda take kula dashi haka property nashi ma bata bari ba.

       "Ka gama shirin kenan?" Ta tambaya.

     "Yes Azizaty". Ya amsa.

     " Toh ga breakfast is ready". Ta fad'a.

      "Wow! My wife hancina kina kasheshi da 'kamshi". Ya fad'a sanda ya bud'e sauce d'in ,plate kuma soyayyen dankali ne.

     Da kanta ta had'a masa tea d'in ,danma yayi late shiyasa sauri-sauri yaci.

     " Allah ya kiyaye hanya".Ta furta sanda ta rakoshi soro.

      Sunkuyowa yayi kad'an ya manna mata kiss a kumatu.

     "Sena dawo". Ya fad'a.

     " Bye".Ta fad'a tana waving hannu.

    Bayan data kammala nata breakfast d'in ta tattare kwanukan ta wanke ,se sauran gyaran data 'karasa,kan gado ta hau abinta ta koma barci.

AR²💖

Jasko💕     🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣2⃣

  Reyhana ba ita ta tashi ba se wajen 11:10am,wanka tayi tayi shirinta cikin material blue ya d'auketa sosai.Kitchen ta shiga ta d'ora tukunya tana canki-cankin me zatayi kuma tasan shi Ahmad ba ruwanshi ko ta kira ta tambayeshi ba za'ba zeba.Daga 'karshe de ta yanke shawarar yin tuwon semovita da miyan alayyahu.

     Around 12:00pm ta kirasa a waya,lokacin yana class ya fita tukun yayi picking.

     "Azizaty!" Ya kira sunanta.

    "My dear ya school d'in yau?"

    "Kinganni ina class ma na fito". Ahmad ya fad'a.

     " Ok, toh go back to your student seka dawo". Ta fad'a.

     "Toh my wifey sena dawo". Ya fad'a.

    Daga haka sukai sallama,komawa tayi kan girkinta dama miya ya rage ta gama.

               ***

   2:23pm Ahmad ya dawo gida,Reyhana kuwa tuni ta kammala komai ta sake dusting powder a fuskarta se lipgloss data 'kara a lips d'in.

       Tana jiyo knocking nasa tayi saurin fita,ba 'bata lokaci ta bud'e 'kofar.Bata ankara ba taga yayi hugging nata.

      " My dear mutanen waje zasu hangomu fa". Ta fad'a.         "Ina mutanen suke azizaty banga kowa ba". Ya fad'a dan unguwar ba hayaniya sosai.

     'Kofar ya tura ya rufa tukun yayi breaking hug d'in." Kinyi missing d'ina ma kuwa azizaty? " Ya tambaya.

     "Meyasa kace haka?" Ta tambaya.

     "Ehmana naga kamar baki missing d'ina ba".

     " I do mana".Ta fad'a tana turo baki.

     "OK if you miss me then". Ya fad'a tare da nuni da kumatunsa alamar tayi masa peck.

       Murmushi tayi tukun tayi d'age nan tayi masa peck.

      " That's my Azizaty ". Ya fad'a tare da tallafota jikinsa.

       Kamar koyaushe ta kai masa ruwan wanka toilet,bayan ya shirya kuma ta kawo masa abinci.Yau tare suke cin abincin dan itama bata ciba,suna ci suna hira.

       " Yawwa my d yaushe zami je gaida Umma?" Reyhana ta tambaya.

      "Kede kawai kina so kiji yaushe zaki wajen mommy". Ya fad'a yana mata dariya.

      " Laaa! Ni ba haka nake nufi ba". Ta fad'a.

      "Zaki wayence ba". Cewar Ahmad.

      "Toh shikenan baka amsan tambayata ba". Ta fad'a.

      " Reyhana yau har kwanakin nawa a gidannan ma tukun?"

      "Kwana fa kace? Ana maganar wata fa kenan". Ta amsa da sauri.

      " A'a azizaty baki kaiba de".

      "Toh na lissafa ma?" Ta tambaya.

      "Eh lissafa". Ya amsa tare da tattaro attention d'insa kanta.

      Reyhana kuwa sosai ta fara lissafi tiryan-tiryan hadda yatsu a lissafin nata,yadda take lissafin ya bashi dariya sekace 'yar yarinya." Toh my azizaty na yarda". Ya fad'a.

      "Kaga harna 'kara kwana biyu akai ma". Ta fad'a.

      " Gaskiyarki uwargida". Ya fad'a cikeda zolaya.

      Kallonsa kawai tayi tana jiran mey ze ce akai."To shikenan ki shirya a week d'innan".

     "Toh Allah ya kaimu". Ta fad'a dukda ba haka taso ba tafi so yace ga ranar.

     " Ko bakya so mu bari wani watan? " Ya fad'a yana kallon reaction nata.

      "A'a inaso". Ta fad'a da sauri.

      " Sorry,da wasa nake". Ya fad'a yana mata murmushi.

       Haka suka kammala cin abincin,koda zata d'auraye kwanukan tare suka wanke.Bayan daya je sallar asr ya dawo nan suka cigaba da hirarsu.

      "Nikam yau baza ka duba takardun d'aliban naka ba ?" Reyhana ta tambayeshi kanta akan cinyarsa.

       "Azizaty yau banyi musu test ba ai". Ya amsa ta.

      " Ok toh ya school da students naka?"

      "Ba sau'ki nake fad'a mini,thank god ina da gimbiya mey sani farinciki".Cewar Ahmad yana shafa girarta.

       " Ayya My dear ". Ta furta.

            ****

2days later

      Reyhana  wajen 4:12pm bayan ta idar da sallah tana zaune sitting room tana kallon Bollywood sega Ahmad ya dawo daga masjid.

      " Sannu da dawowa". Ta fad'a.              "Yawwa".

       "Azizaty ki shirya muje mu gaida mommy". Ya fad'a tare da zama gefenta.

     Da sauri ta kallo inda yake" Da gaske?"

       "Bakyaso ne?" Ya tambaya fuskarsa a sake.

       "Wane? Yanzu zan shirya". Ta fad'a tare da mi'kewa tsaye.

      D'aki ta shiga da sauri ta sauya kaya,lace tasa maroon da torches golden, se necklace nata golden me kyau,ta fesa turare me taushin 'kamshi gyalenta ta yafa golden ta zira flat shoe se purse data sa phone d'inta.Duk wannan shirin befi a 10min ba dan gani take lokacin kamar ze 'kare.

      " My dear am ready". Ta fad'a tana murmushi wanda har ha'koranta seda suka bayyana.

       "Iyye! Azizaty kamar wal'kiya har kin shirya?" Ya fad'a yana kallonta.

       "Eh na shirya". Ta amsa.

       " Zumud'i d'in kenan". Ahmad ya fad'a tare da mi'kewa.

    Bayan ya kashe TV d'in ya fito ,seda ta tabbata ta rufo ko ina tukun suka fito.

    Abin gwanin sha'awa da suka jero."Gaskiya next time zamu fita niqab zaki sa". Ya fad'a yana d'an 'bata rai.

     "Haba niqab ". Ta fad'a tana d'an turo baki.

     " Bakiga ana kallemin keba?" Ahmad ya furta.

     Shiru tayi bata ce komai ba ,napep ya tsarar masu suka hau.

      "Gaskiya na dad'e banga gari ba ji nake kamar na shekara". Reyhana ta fad'a tana kallon waje.

       " Just a month d'in ? Aiko ki saba ".Ahmad ya fad'a.

      A haka suna ta hirarsu har suka 'karasa gidan,Ahmad bayan ya sallami me napep d'in suka shiga ciki.Da Baba me gadi suka fara cin karo a gate ,ganin su ya washe baki dama shi mutum ne me barkwanci." Ahh yau Hajiya Amarya ce a gidan".Ya fad'a.

       "Baba ina wuni". Ta gaishesa.

     " Lafiya qalau Reyhana".Ya amsa.

     Ahmad hunnu ya mi'ka masa suka gaisa,daga nan suka shiga.Koda suka shiga makeken parlourn shiru kamar ba kowa,chan kuma bayan sunyi sallama sega Ikram 'kanwar Reyhana ta sakko "Laa! Yaya Reyhana dama kece ? "

     'Karasowa tayi da sauri inda take tana murnar ganin yayartata "Sannu da zuwa yaya". Ta fad'a tana murmushin jin dad'i.

     Itama Reyhana da farinciki fal a ranta take magana " Yawwa Ikram". Ta amsa.

      Tana ri'ke da hannunta suka zauna,Ahmad na d'ayan kujerar Reyhana kuma suna wata daban."Ya Ahmad ina yini". Ikram ta gaisheshi.

      "Lafiya lau Ikram, ya gidan?

      "Lafiya lau". Ta fad'a.

     " Bari na fad'a ma momy". Ikram ta fad'a tare da mi'kewa.

      Momy tana d'aki ta hakimce tana kallon TV Ikram ta shiga.

      "Mommy yaya tazo". Ikram ta fad'a.

       Mama da sauri ta d'ago kanta ta kalleta "Reyhana kuma da yammannan?" Mommy ta fad'a tana sake so ta tabbatar.

      "Da gaske Mommy tareda ya Ahmad ma take". Ikram ta amsata.

     Jin an ambaci Ahmad yasa Mommy ta had'e rai.Kamar bazata tashi ba ta mi'ke zuwa parlourn.         Ahmad yana ganin Mommy ta 'karaso yayi saurin sakkowa daga kujerar." Ina yini Mommy ". Ya gaisheta.

      " Lafiya lau". Ta amsa ba wani walwala tattare da ita.

      "Mommy ina yini". Reyhana ma ta sunkuya ta gaidata.

     Bakinta a ta'be ta amsa wanda duk cikinsu ba wanda ya kula.Tana me mamakin yadda 'yartata ta tsunduma kanta a wannan irin rayuwar dan gani take kamar a takure take.

     Reyhana ce ta katse shirun da d'akin ya d'auka da tambayar" Abba be dawo ba ?"

      "Eh be dawo ba". Ta amsa.

      Mommy ko 'kala bata cewa inba wai Reyhana ta tambayeta ba.Suna zaune a haka su Bassam da Walida('Kannen Reyhana) suka dawo daga islamiyya.Da gudu Walida ta 'karaso tana mata oyoyo.

      " Walida 'yan mata an dawo". Reyhana ta fad'a tana rungumo ta.

      "Eh yaya,dama zaki so?" Ta tambaya.

      "Eh gani na zo". Ta amsa tana murmushi.

     Bassam shima 'karasowa yayi ya gaida Ahmad sannan ya gaida ta,itama Walidan se lokacin ta lura da Ahmad ta gaisheshi.

       " Toh Walida aje a sauya kaya ".Ikram ta fad'a lokacinda ta 'karaso.

     Ma'ke kafad'a tayi wai bazata bar yaya ba." Good girl jeki ki cire uniform d'in kinji seki dawo ina nan".Reyhana ta fad'a tana lalla'bata.

      "Toh".Ta amsa sannan ta kyalla da sauri zuwa d'aki.

       Shima Bassam nashi d'akin ya wuce.Inno(me aikinsu) ce ta kawo musu abinsha bayan sun gaisa.Mommy tashi tayi ta koma d'aki dan zaman ya isheta,se Ikram da Walida suna zaune kusa da Reyhana.

        Reyhana itace 'yar fari a gidansu,su biyar ne duka.Maza biyu mata uku,daga Reyhana se sageer ,Ikram,Bassam then Walida auta.Reyhana nada shekara 1½ aka haifi sageer saboda haka basuda tazara sosai.Reyhana tana da shekara 22 a yanzu se shi 20½,Ikram tana da 18 yrs,Bassam 15 then Walida 9yrs suna da tazara.

      Reyhana tana kammala degree nata ta auri Ahmad dan karatunta yayi sauri ko secondary school da wuri ta gama,Bsc microbiology ta karanta.Sageer a yanzu haka yana level 2 MLT yake karanta,Ikram kuwa year d'innan tayi graduation na secondary se Bassam yana SS1 Walida kuma primary 3.

      Mommy kuwa business woman ce tayi-tayi Abba ya barta tayi aiki amma ya'ki ,shiyasa business ta du'kufa kuma dama a gidan su yawanci 'yan kasuwa ne.Abba kuwa babban professor ne a university Buk.

     Sun kasance happy family kuma yaran sunfi sabo da Abbansu musammman Reyhana da Sageer kasancewar Mommy mace me zafi ,Abba yafi ta sau'kin kai.Toh wannan kenan.

      Wajajen 6:00pm Abba ya shigo ,cikin rissinawa ya gaishe da Abba itama Reyhana haka."Kice yau kune a gidan".Abba ya fad'a fuskarsa a sake.

      "Eh Abba d'azunnan muka zo". Ta amsa.          " Toh mashaAllah yayi kyau Allah yayi albarka". Ya fad'a.

       "Ameen" .Suka amsa.

      Daga baya Reyhana d'akinsu ta wuce,sukuma mazan suka tafi masjid tare da Ahmad.

      Mommy seda taji fitarsu ta fito daga d'akinta ta shiga d'akin Ikram ,da tare suke kwana sanda Reyhana tananan yanzu kuwa ita kad'ai ta'ki bari Walida ta komo d'akin.

      "Ana san a had'u ayi ta hira da 'yan uwa amma baza a dinga waya dasu ba". Mommy ta fad'a sanda ta 'karaso.               " Laaa! Mommy ina fa kira". Reyhana ta fad'a.

      "Ba wani,kuma da kika san zaki zo ba seki fad'a ba". Cewar Mommy tana shirin zama kan wani kujera dake d'akin.

      " Nima bansan da zuwan ba jinai kawai yace na tazo muzo gida".Reyhana ta fad'a.

      "Toh seku tashi ai kuyi sallah". Mommy ta fad'a.

     " Mommy idan zasi tafi zan bisu". Walida ta fad'a kanta a cinyar Reyhana.

     "Base ki bisun ba,tashi ki wuce ki sallah!". Mommy tai mata tsawa.

      Ba Walida ba har Reyhana seda taji ba dad'i" Mommy meyai zafi haka ?" Reyhana ta furta.

      Mommy ko amsata batayi ba ta fice daga d'akin,Reyhana kallo kawai ta bita dashi a ranta tana fad'in Allah ya kawo ranar da zata dena jin haushin aurennan nata...

AR²💖

# Comment #  Vote

Jasko💕

    🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣3⃣

Bayan sun idar da sallah ne ikram ta d'akko mata wasu hotunan na bikin ta da bata gani ba.

     "Yaya kalleki a nan". Ikram ta nuna wani pic da Reyhana ta rife idanunta.

     Dariya dukansu sukai suka cigaba da kalla.Misalin 'karfe 7:08pm Inno ta gama abinci lokacin Abba suna parlour shida Ahmad suna 'yar hira.

     Bayan an kawo wa Ahmad abincin Abba ya tashi domin ya bashi waje dan ya kula ya kasa sake wa.Reyhana kuwa a d'aki suka ci tare da Ikram.

       Sageer shima lokacin ya shigo ,hannu ya mi'kawa Ahmad suka gaisa." Sageer ya school?" Ahmad ya tamabaya.

     "Alhamdulillah,kun shigo kenan?"

     "Eh d'azunnan". Ya amsa.

     " Ok,bari na watsa ruwa ". Sageer ya fad'a.

       D'akinsa ya wuce ,Reyhana kuwa ta shantake kamar bazata tafi ba hira ta'ki 'karewa.          Koda ya gama yana zaune shi kad'ai a parlour sega kuma Sageer harya fito.D'an hira suka soma yi har lokacin isha'i yayi.Suna dawowa daga masjid yayiwa Reyhana text.

    " Toh Azizaty se a fito dare yana yi"               Tana gama karancewa ta kalli agogo taga 8:13pm,nan take ta sauya fuska dan ji take kamar karta tafi sosai tayi kewar gida.

     "Ya de?" Ikram ta tambaya dan ta lura da chanjin fuskarta.

       "Ya Ahmad ne wai na fito mu tafi". Ta amsata.

       " Ayya! Yaya amaryar Ahmad ".Ikram ta fad'a cikeda tsokana.

      " Zan doke ki Ikram". Reyhana ta fad'a.

      "Sorry sister nice fa".

      " Toh ni ba wannan ba,yaushe zaki zo ki yinammin?"

       "Au wuni kad'ai zaki gayyaceni watoh banda kwana koh?" Ikram ta fad'a tana kallon Reyhana.

        "Ke dallah idan kwananma nace ai 'bata bakina zanyi". Ta fad'a.

       " InshaAllah zanzo bada dad'ewa ba yaya, yanzu de muje parlourn kar ya Ahmad yaji shiru". Ta fad'a.

     Parlour suka sauka se kuma suka iske Mommy ma tana parlourn gefe Abba da alama shiya kirata ta sakko da bazata zo siyi sallama ba."Reyhana kun fito kenan". Abba ya fad'a.

     "Eh". Ta amsa sanda ta 'karaso.

      " Sageer ashe ka dawo?" Cewar Reyhana.

       "Eh tun d'azu ,kina d'aki kunata hirarku". Ya amsata.

       " Toh ya school? "

       "Alhamdulillah". Ya amsa.

         Abba ne ya bawa Sageer key d'in motarsa yace akaisu gida,Mommy kuwa ta'be baki tayi taso yace akaisu a tata da anga tsiya.A haka sukai sallama itade Mommy fuskarta ba sakewa.

    Har 'kofar gida Sageer ya kaisu ,bayan sunyi sallama ya juya.Koda suka shiga gida ba light shiyasa da wuri suka kwanta tunda dama sunci abinci a gida.

                 ***

  Washegari 7:20am Ahmad ya gama shirinsa har breakfast ma ya kammala."Yau me za'a dafa da rana?"Reyhana ta tambayesa.

          " Ni duk abinda kika dafa yayi". Ya amsata yana zira takalmi.

         "OK dear seka dawo toh". Ta fad'a tare da mi'ka masa hularsa.

          " Wata'kila sena yi sallar juma'a zan dawo". Ya fad'a.

         "Ohh na tuna yau Friday koh". Ta fad'a.

         " Duk wannan kwalliyar danai baki tuna bama? Wait kinko ce nayi kyau ma?" Ahmad ya fad'a ya tsireta da ido.

        "Laa na fad'a abinda ma ko yaushe kyau kake, kawai de na sha'afa". Cewar Reyhana tana murmushi.

         " Au hakane ,toh sena dawo Azizaty karnayi late".

       "A dawo lafiya".Ta fad'a.

       " Ameen".Ya amsa daga nan ya fita.

     Kamar koyaushe nan da nan tayi aikin gida tayi wanka ta shirya tsaf cikin atamfa blue me ratsin fari da ba'ki.Ga turaren wuta daya turnu'ke ko ina Reyhana bade tsafta ba.

      Wayarta ta d'auka ta kira Saudat ('kawarta ) tare sukai secondary school.            "Amaryar Ahmad kin ya dani,daga kaiki gidanki se mijiki li'kwi bako flashing?"

        "Saudat da sharri yanzu gashi na kira ki ,kece ma kika manta dani baki zo ba". Reyhana ta fad'a.

         " Ina tafe ai ki shiryan kayan dad'i".Saudat ta fad'a.

        "Karki damu zaki zo ki kwashi girki na". Cewar Reyhana.

         Sun dad'e suna hira kafin daga baya siyi sallama.11:30am ta d'ora abinci ,a  hr d'aya da 'yan mintina ta kammala ,zo'bo ta had'a shima nan danan tasa a fridge.

             ***   Gidan Mommy..

         Tana d'akinta  ,wata yayarta(Anty asma'u),suna d'asawa kusan halinsu yazo d'aya.

        " Ya amarya a gidanta?" Anty Asma'u ta tambaya.

        "Uhmm! Tana gidanta jiya ta shigo ma". Cewar Mommy tana ta'be ba'ki.

         " Ita kad'ai ko harda Ahmad d'in?"

         "Ita dashi ne".Mommy ta amsa.

         "Toh ke yaushe zakije keda Abbansu?" Ta tambayi Mommy.

         "Sede shi yaje dan ba zuwa zan ba,wannan d'an 'kurbibin gidan". Cewar Mommy.

        "Toh ya za'ai ? Yaran yanzu ne bajin magana suke ba kana d'ora su a hanya suna kaucewa". Anty asma'u ta fad'a.

       " Ai du Abbanta ne wlhy badan shiba da ba abinda zesa na yarda da aurennan".Mommy ta fad'a.

      "Eyyi ita dad'i miji zata gane me ake nufi rabu da ita". Anty asma'u ta fad'a.

       " Ni abinda yake sake cimin rai shine ko a karatu ta masa nisa shekarun kansu befi uku  ya bata ba yaro ne shakaf amma ita ta rife ido seshi".

      "Allah de ya sawwa'ke". Anty asma'u ta fad'a.

     " Ameen ".Mommy ta amsa.

                  ***

1:45pm Ahmad ya dawo gida ,koda ya shiga d'aki bata ciki suitcase d'in ya ajje ya fita zuwa sitting room." Laa! Dear yaushe ka dawo banji ba?" Reyhana ta fad'a tare da 'karasowa inda yake.

         "Azizaty najiki shiru ne". Ya fad'a.               " Sannu da dawowa toh ".Ta fad'a.

        " Yawwa Azizaty".Cewar Ahmad tare da rungumota jikinsa.

        "Bari na  kawo abinci dan naga se hamma kake".Reyhana ta fad'a tare da yin dariya ta fita bata jira me zece ba.

       Girgirza kai kawai yayi yana murmushi dan kuwa bata yi 'karya ba tun daya baro school ya fara jin yunwa.A tray ta jero komai ta kawo.

     " Azizaty taya kiga gane ina jin yunwa?" Ahmad ya tambaya.

      "Naga kana ta hamma ne,gashi da'kyar kake magana". Reyhana ta fad'a ta 'kare da dariya dan ita kanta maganarta ta 'karshe ta bata dariya.

      " Azizaty da sharri kike,what ever de ziba min am grateful i have a special wife like you me gama abinci da wuri".Ahmad ya fad'a.

        A plate ta sa musu suka ci yana ta santi yana yaba girkinta,ita de kawai murmushi take a ranta tana jin dad'in yadda yake yaba girkinta da dad'ad'an kalamansa masu sanyaya zuciya.

          Bayan sun gama ci kuma suka tsiri yin photo ,kala-kala tayi ta selfawa sosai sunyi kyau (Naga su wa'e an le'ko 'yan ina ga selfie...lox bande fad'i suna ba😝).

                 ****    Rana Sunday da Asr Ahmad yace ta shirya suje gidan Umma.Ita kad'ai suka tarar gidan ko yaran ma'kobatan ma masu d'an le'ko mata basu shigo ba."Yau Reyhana ce a gidan,sannu da zuwa "Umma ta fad'a tana 'ko'karin shinfid'a tabarmar dake jingine a kusurwar d'akin.

      " Ina yini Umma"Reyhana ta gaisheta cikin rissinawa.

     "Lafiya lau Reyhana". Ta amsa.

      " Ya zaman shiru?"Umma ta tambayeta.

      "Alhamdulillah ". Reyhana ta amsa.           Shima Ahmad gaisawa sukai sannan Umma ta kawo mata ruwan sha da band'ashon gurasa." Sannu da 'ko'kari".Cewar Reyhana kanta a sunkuye tana wasa da yatsunta.

       "Kinga ki sake jikinki se wani ra'bewa kike".Ahmad ya fad'a mata 'kasa-'kasa ba tare da Umma taji me yace ba.

       Bayan 'yan mintina kad'an ya tashi" Umma bara na le'ka waje". Ahmad ya fad'a.

      "Toh seka dawo".Umma ta fad'a.

       Kad'an -kad'an suke hirarsu ,Reyhana ba sabawa tayi da ita ba tunda yau ne karo na farko tazo,sede su gaisa a waya shiyasa ta kasa sakin jikinta.

    " Kici band'ashon mana ai abin marmari ne".Umma ta fad'a.

         Itade Reyhana murmushi tayi sannan ta fara gutsura.

       "Ki saki jikinki nan ai gidane". Umma ta fad'a tana murmushi.

       Reyhana taji dad'in band'ashon kusan biyu da rabi taci(Nima naji dama..😋).

      Umma dama daga ita se d'anta Ahmad data haifa gashi yanzu ita kad'ai shiyasa ma wani d'an saurayin ma'kota yake kwana a shagon gidan na waje.Sunyi sabo da jam'ar unguwar sosai dan a nan aka haifi Ahmad abokanansa dayawa suna nan shiyasa a koda yaushe idan yana gida toh suna majalissarsu yanzun ma can ya tafi.Umma mace me ha'kuri ba sawa ba hanawa dattijuwa ce me son zaman lafiya ba ruwanta da ta'kurawa suruka..

      Har mahrib tayi bai shigo ba,tashi tayi tai sallah danma Allah yasa da wuta 'yar 'karamar TV dake d'akin  Umma ta kunna mata kallo.Haka yasa ta rage zaman shirun,Umma kuma ta koma kan girkinta.

       Ahmad bashi ya dawo ba se bayan isha'i ,a kitchen ya iske Umma.

      " Sannu da aiki girkin ne?" Ya fad'a yana shafa ciki.

       "Baka ci a majalissar ba?"

       "Ai nasan zan kwashi girkin ki shiyasa". Ya fad'a yana d'an dariya.

        " Ni banyi girki dakai ba,daga ni se Raihana". Umma ta fad'a tana kad'a miya.

      "Bafa Raihana ba Rey Reyhana ake cewa". Ya gyara mata.

      Dama tana sani tace Raihana tasan seya gyara mata,ko kafin yayi aure ma haka sike da ita.Reyhana tana jiyosu a d'aki tana dariya yanayin rayuwarsa da mahaifiyarsa yana birgeta.

        " Azizaty ina nawa bad'd'ashon?" Tajiyo maganar Ahmad.

        "Ga d'aya da rabi na rage ma". Ta fad'a tana jiran meze ce.

        " Lalle kinde cinye ,toh aiko tashi zaki mu tafi seki min abincin dare".Ya fad'a.

       "Abincin dare a wannan lokacin?"

        "Ehmana ba kin cinyen na Umma ba". Ya fad'a kamar d'an yaro.

    Dariya ya bata yanda yayi maganar,zata sake magana Umma ta shigo da abinci.

     " Reyhana ga tuwo fah".Umma ta fad'a tare da ajjewa.

      "Toh madallah Umma".Ahmad ya fad'a tare da janyo warmer d'in kusa dashi.

     Reyhana murmushi kawai tayi ta d'auke kai kamar bata gani ba tasani yana sane yayi haka ita kuwa ba kula shi zatai ba balle ma Umma tana wajen.

         " Bakya ci ne?" Ya tambayeta.

         "Niba kai na kawowa ba fah".Umma ta fad'a.

         "Haba Ummana ya dahaka ita d'azu taci band'asho nikuma yanzu se a barni naci tuwo ai koh".Ahmad ya fad'a yana bud'ewa.

      Tuwon dawa ne da miyar kuka ga wani 'kamshin daddawa dayake tashi (Kai wayyo dad'i 😋).

   " Hmmm! nayi missing d'in girkinnan fah". Ya fad'a yana kallon Reyhana. 

        Gani yayi bashi take kallo bama,yana gama zibawa a plate d'in ta faki ido Umma taga bata kallon wajen tayi sauri ta janyo plate d'in wajenta.Kafin ya ankara Umma ta waigo ,basarwa yayi ya sake zuba wani a plate dan yasan ba ci zatai dashi ba.

      Kowa shiru yayi yana sambad'ar tuwonsa har suka kammala.

       "Alhamdulillah se tafiya kuma". Ahmad ya fad'a bayan ya ajje cup d'in ruwa.

      " Ai ka bari abincin ya fad'a kuma".Umma ta fad'a.

        Seda suka 'kara kusan minti 20 suka tafi.

        Koda suka koma gida Ahmad be kwanta da wuri ba dan akwai test na students nashi da be 'karasa marking ba.Ita kuwa tuni tayi bacci bema lura ba dan a zaune yake kan gadon ya juya mata baya.

       Dayai magana yaji bata amsasa ba ya waiga yaga tayi bacci.Murmushi ya saki sannan ya gyara mata kwanciyar ya tofa mata addu'a....            AR²💖

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣4⃣

  Da asuba bayan ya dawo daga masjid Reyhana ta kai masa ruwan wanka toilet.

       Da kanta ta za'ba masa kayan sawa yana fitowa ya gansu ta ajje a kan gado ,T-shirt ce dark blue da ba'kin jeans ,da sauri ya saka ya shirya tsaf tukun ya fito.A kitchen ya taddata tana soya dankali.

      "Ina kwana". Ta gaisheshi.

       " Lafiya,ya bacci Azizaty jiya da wuri haka kika kwanta". Ahmad ya fad'a.             "Eh toh naga kana ta marking". Ta fad'a.

           " Toh me ake dafa wa?" Ya tambaya.

           "Hmm dankali ne". Ta amsa.

           " Sannunki da 'ko'kari".

           "Yawwa dear". Ta amsa.

       Bayan mintina ta kammala ta kawo masa." Azizaty ke ba yanzu zaki ci ba?"

      "Se anjima".Ta amsa.

     Ba jimawa ya gama breakfast d'in,takalmi ta d'akko masa a d'aki yasa sannan ya tafi ,ita kuwa ta koma baccinta.

              ***

     Haka abubuwa suka cigaba da gudana ,Ikram da Walida sunzo sun wuni sageer ma yazo, Abba ne har yanzu daya cewa mommy suje seta ce ba yanzu ba ,sede yana waya da ita.

      Yau aurensu wata uku kenan,Reyhana na kitchen tana girki yau Saudat zata zo.

        " Azizaty 'kawar taki bata karaso ba kenan".Ahmad ya fad'a sanda ya fito tsakar gidan.

        "Minyi waya tace ta taho". Reyhana ta fad'a.

         " OK,bara zan d'an le'ka waje ba dad'ewa zan ba".Ya fad'a yana zira takalma.

         "Toh shikenan seka dawo".

        'Yan mintina 'kalilan ta 'karasa dama couscous da miyan ne se lemon cucumber tun jiya dama tayi mata cake ga exotic guda biyu daya ragu ta had'a mata da d'aya.

        2:45pm Saudat ta 'karaso gidan ,Reyhana tana d'aki tajiyo knocking d'inta da sauri taje ta bud'e."Besty!" Reyhana ta fad'a tare da hugging Saudat.

     "K'awas kai nayi  missing d'inki sosai sosai". Saudat ta fad'a.

      " Toh mu 'karasa ciki". Reyhana ta fad'a tare da breaking hug d'in.

        Sitting room tayi mata jagora suka 'karasa kowacce farinciki ya mamayeta."Amarya ashe zan sake ganinki".Cewar Saudat sanda suka zauna a kujera.

       "Ke d'ince koyaushe sa rana kin kasa zuwa,ya su Mama". Reyhana ta tamaya.

       " Duk lafiya suke,sunce a gaisheki".Saudat ta amsata.

        "Bari ina zuwa". Reyhana ta fad'a tare da fita.

         Abincin da sauran kayayyakin ta jero a tray ta kawo mata." Sakko ki ci se ai hirar".Cewar Reyhana.

          "Ohni Saudat du ni kad'ai".

          " Ehyi ke kad'ai.Ta amsa.

       Sakkowa tayi ta fara da,suna d'an hira tana ci."Ya Mommy kuwa tazo". Saudat ta tamabaya.

       "Ai Mommy har na fiddaran zuwanta har yanzu bata zo ba kuma Abba yana so zuzo amma shiru de,su Ikram de sunzo amma ko sisters d'in Mommy basu zo ba,na fad'a maki nifa bana ba'ki shiyasa kika ga ina azar'ba'bi kizo". Reyhana ta fad'a fuskarta na nuna tsantsar damuwa da hakan.

      " Ayya 'kawata karki damu inshaAllah komai ze dedeta kiyi ta addu'a,amma kede kina waya da ita koh?" Saudat ta tambaya.

      "Eyyi ina wayo dasu".Ta amsa.

      " Toh hakan yayi kyau".Saudat ta fad'a.

       Bayan ta gama cin abincin sega Ahmad ya dawo ,suna gaisawa da ita ya shige d'aki.

     Ranar ta musu dad'i sunsha hira abinsu da selfie,se wajen 5:30pm  Saudat ta tafi.

              ***     Gidan Mommy..

          "Bafa inda zaki na fad'a maki". Mommy ta fad'a tana zaune kan sofa na parlour.

      Walida dake tsaye ta yafa mayafi ita a lalle seta je gidan Reyhana.

     " Mey ke faruwa ne?" Abba ya tamabaya sanda ya sakko 'kasa dan yajiyo d'aga muryarta.

        "Abba dan Allah kace Mommy ta barni naje gidan Yaya". Ta fad'a kamar zatai kuka.

      Abba Mommy ya kalla da ta 'kura wa TV ido kamar bata san suna gun ba." Mommyn Ikii ki barta taje mana".

      "Na fad'a mata ba inda zata gara ma ta ha'kura". Mommy ta fad'a ba tare da ta kallesa ba.

    Hakan da tayi ya 'kona masa rai." Walida jeki d'aki zan kira ki anjima".Abba ya fad'a.

       Ba musu ta haye steps da sauri, Abba kuwa takawa yai ya 'karasa wajen Mommy ba tare da ya zauna ba yace"Bana son abinda kike yi taya ina maki magana ki kauda kanki ,kuma wannan yarinyar gidan yayarta zata meye aibu a ciki tunda ke kin'ki zuwa seki barsu su dinga zuwa bafa kya kyautawa yarinyarnan duk abinda ze faru ya riga ya faru kowa da kika gani bada arzi'ki aka haifeshi ba a duniya ya samu ki duba mana".

        "Allah ya taimaka 'kofa ce a bud'e take sesi ta zuwa suke kwana ma". Mommy ta fad'a ta bar parlourn.

     Abba yana tsaye ya kasa ta'bika komai wani hali sena Mommy sam idan taso tsiya sede ya rabu da ita.Girgiza kai kawai yayi" Allah ya sawwa'ke".Ya furta tare da barin parlourn.

      Around 4:30pm Reyhana taji knock ya shigo,hijab ta zira ta tafi bud'ewa dan bata tunanin Ahmad ne.

      "Abba!" Reyhana ta kira tana me mamakin ganinsa.

      "Sannunku da zuwa ku 'karaso ". Reyhana ta fad'a ta bud'e'kofar widely.

       Walida da sauri taje ta rungumeta,itama Reyhana haka suka shiga ciki.

          "Ina yini Abba". Ta gaisheshi cikin rissinawa.

          " Lafiya lau Reyhana ". Ya amsata.

        Sageer dake gefe shima suka gaisa,se Walida dake manne da ita.

         Allah ya taimaka tana da ragowar cake dayai saura jiya se exotic d'aya ta kawo musu da ruwa." Ikram da Bassam fah?" Cewar Reyhana tana kallon Walida.

      "Suna gida su". Ta amsa.

    Ba jimawa sega Ahmad ya dawo suka gaisa ya d'an zauna a sitting room d'in suna hira da Abba.

         Da suka zo tafiya Walida tayi 'kememe baza ta bisu ba seta kwana.Ba yadda basi da ita ba " Walida ba'a taho da kayanki ba fah".Sageer ya fad'a.

         "Abba ku barta ta kwana mana na kawota d kaina". Reyhana ta fad'a.

       Haka suka ha'kura suka tafi ,Reyhana taji dad'i sosai ta samu 'yar hira.

             ***

Suna komawa gida Mommy tana parlour ita da su Bassam sun baje ice cream suna sha.

      " Abba sannu da dawowa".Yaran suka fad'a.

       "Ina Walidan kuma?" Bassam ya tambaya.

       "Mun barta can ta nace seta kwana". Sageer ya amsa.

                Mommy ko tanka musu batai ba,illa shan ice cream d'inta data cigaba.

       Suma shirin sukayi Abba ya wuce d'aki Sageer ma sashensa ya wuce.

               ***

    Walida kwai surutu har Maghreb tana hira da Reyhana daga baya ta 'karbi wayarta ta fara game. Reyhana se lokacin ta shiga kitchen girki dama kuma taliya zatayi jollof.

     Ahmad kuma ya tafi masjid har lokacin be dawo ba.Tana kammalawa ta ziba musu ,suna cikin ci ya dawo.

       " Sannu da dawowa".Reyhana ta fad'a.

       "Yawwa".ya amsa yana 'ko'karin zama kan kujera.

      Ita ma walidan sannu da dawowan tayi masa  ta cigaba da cin abincin.

      Reyhana tashi tayi ta zubo masa nashi shima tukun ta cigaba da ci tana mata labarin makaranta.

        Wajajen 9:30 Walida ta soma gyangyad'i ,d'akin gado ta kwantar da ita kamar yadda Ahmad ya bu'kata shi seya kwanta a sitting room.

      Chan cikin dare aka d'auke light gashi weather d'in da zafi kad'an Walida ba son zafi take ba tuni ta farka.

         Ga mosquito net shiyasa ta takura,Reyhana fifita ta hau yi mata sannan ta koma, ita kuwa Reyhana se wajen 4:14pm ta koma bacci.

        Ahmad koda ya tashi asubah kamar ko yaushe ya tashi Reyhana ya fita.Rashin bacci da bata samu ba yasa ta koma ba tare da ta ankare ba.

         Koda ya dawo 6:48am ya tarar bata tashi ba seda ya sake tayar da ita,da sauri ta mi'ke ganin hasken gari.

         " Ya salam!" Ta furta.              "Tabb! Kice baccin kika koma har 7 ya kusa fa". Ahmad ya fad'a.

         Da sauri ta shige toilet tayi alwala sannan tayi sallah,nan ta yaye net d'in ta tashi Walida da 'kyar dan akwaita da nauyin bacci.

       Kafin nan 7:15am yayi, data fito ta tarar ya d'ora ruwan tea hakan ya nuna ya sauke ma na wankan.

        Kitchen d'in ta shiga tana tunanin abin breakfast dan potatoes ya 'kare gashi doya ma baze ishesu ba dan kad'an ya ragu ,tuna tana da flour kawai ta fere doyan nan da nan ta soya da ragowar egg dan shima yazo 'karshe.

        Flour d'in kuwa ta kwa'ba fanke nan da nan tunda garin da d'an rana.

       Doyar ta d'iban masa ta had'a tea ta kaimasa ,sauri-sauri yayi breakfast d'in dan yayi late 7:39am ya fita.

       Ragowar doyar ta bawa Walida ta had'a mata tea tasha, ita kuwa seda ta jira ya tashi fanken ta soya taci. Kafin tayi breakfast tayi shara ya rage wanke-wanke da sauran ayyuka.

         " Walida a ajje game d'in ga ruwan wanka na had'a maki".Reyhana ta fad'a sanda ta shigo sitting room taga tana ri'ke da wayarta.

        "Yaya bari na fad'i sena ajje". Walida ta fad'a hankalinta na kan wayar.

     Reyhana murmushi kawai tayi a ranta tana fad'in" Yarinya baki da damuwa".

      Wajen 12:00pm ta gama shirinta gida yayi tsaf,saura girkin rana kuma.

     Shinkafa da miya ta dafa dan kayan abinci sunyi 'kasa shinkafa ce ta ragu da taliya rabin carton ,se sauran kayan alatun d'and'ano dama kayan gara ne da aka had'ota dasu yanzu kuwa sun kusa 'karewa,gashi har wata ya 'kare ba'a biya albashi ba.

                   ***

    Yau Anty Asma'u tazo gidan Mommy nan take fad'a mata Walida tana gidan Reyhana.

      "Ai yau d'innan Sageer ze d'akko ta". Mommy ta fad'a.

     " Tana wani d'okin gidan Amarya ba uwadda zasu bata se shinkafa".Mommy ta fad'a.

       "Hmm yaro kenan ita a jinta za'a had'ota da kayan 'kwalama.Anty asma'u ta fad'a.

        Sageer yana jinsu shi haushi hirar take bashi ,besan lokacin da zasi dena aibata Ahmad ba sam basa ta'ba yabarsa.

        " Sageer anjima kaje ka d'auko yarinyar nan kajini ko".Mommy ta fad'a.

       "Mommy ku barta mana". Ya fad'a.

       "An'ki d'in kana kallo yau da akwai school amma Abbanka ya 'kyaleta saboda sangarta". Mommy ta fad'a cikin fad'a.

        " Toh ai gobe Saturday ".

         " Seta je islamiyya ,na fad'a maka anjima zaka d'aukota".Ta fad'a.

     Daga haka be sake cewa komai ba sema d'akinsa daya koma.

                ***

     Reyhana wajen Asr suna zaune da Walida akai knocking.Walida da sauri ta tashi ta bud'e 'kofar."Kai ya Sageer meye na zuwa d'in". Ta fad'a tana turo baki.

     Ciki ya 'karaso ita kuwa Walida kamar zatai kuka nan danan ta zauna gefe guda tana turo baki.

      "Kai Sageer da wuri haka, ni na zaci koh kayanta ta kawo". Cewar Reyhana tana d'aga labilen d'akin.

         " Mommy ce ta takura sena d'akkota". Sageer ya fad'a.

        "Kaji Mommy, wai dan Allah meyasa ta'ki zuwa ko su Anty Asma'u ai sa zo sekace banida dangi har kunya nake ji". Reyhana ta fad'a tana nuna alamar damuwa.

      " Tana gida na barota ma Anty Asma'un".Sageer ya fad'a.

       Tashi tayi ta kawo masa ruwa da zo'bon data had'a d'azu.

        Yana zaune Ahmad ya shigo, shiru tayi batace komai ba dan taji ba dad'i be dawo da wuri ba kuma be kirata ba.

         Koda suka gaisa da Sageer d'aki ya bita dan yaga mood nata ya sauya.

        "Azizaty mey nayi". Ya tambaya.

         Shiru tayi masa harta d'auki abinda zata d'auka saboda haka ya shige toilet ya watsa ruwa.

          A sitting room kuwa alewoyi da chewing gum da Saudat ta kawo mata ta bawa Walida. Ba dad'ewa yasa kaya ya fito.

      " Sageer bade tafiya ba". Cewar Ahmad.

        "Gobe da islamiyya ne". Ya amsa.

      " OK".Cewar Ahmad.

     Har mota Reyhana suka rakasu sannan suka dawo ciki.

AR²💖

*Need you warm comments,vote and shares.*

Jasko💕                     🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣5⃣

Koda suka komo ciki bata yi masa magana ba illa zama a kan kujera data yi ta shiga latsa waya.

Zama yayi kusa da ita yace "Azizaty mey nayi?" Ya tambaya.

Shiru tayi bata ce komai ba.

"Please say something ko naji sanyi my Azizaty".

Yanda yayi maganar yasa ta kusa dariya amma seta maze ta cigaba da kallon waya.

" Ayya azizaty inde dan ban dawo da wuri bane ina me neman afuwa ,dubiya muka je da abokaina wayata kuma ba charge shiyasa ban kira ki ba". Ahmad ya fad'a.

"Toh amma kasan zan damu dayawa aikoh da seka kirani da wata wayar". Cewar Reyhana cikin shagwaba.

" Sorry my Azizaty next time haka bazata faru ba kinji".

Kai kawai ta kad'a bata ce komai ba.

"Kin ha'kura?" Ya tambaya tare da tallafo ha'barta.

"Smile my one and only always and forever". Ya fad'a.

Hakan yasa ta saki murmushi ,shi kuwa hugging d'inta yayi tightly " I love you Azizaty.Ya furta

"I love you too dear". Ta fad'a itama ta sake 'kan'kameshi.

***

Ta 'bangaren Mommy kuwa Walida bayan sun koma take nuna wa Ikram alewar da Reyhana ta bata.Mommy ta'ba baki tayi dan tana zaune a palour.

" Wai sunan gidan Amarya aka je shine aka 'kare da wannan mtchhwww!" Mommy ta fad'a tare da tsaki.

Ita Walida bata ji me Mommy tace ba amma Ikram taji tayi gum da bakinta.

Washegari...

Kasancewar weekend Ahmad yana gida throughout be fita ba ,suna sitting room abunsu suna kallo a TV Reyhana ta d'ora kanta a cinyarsa.

Wayar Reyhana ce tayi ringing hakan yasa ta tashi,koda ta duba taga Mommy bayan sun gaisa Mommy take fad'a mata bikin wata cousin tasu Reyhana da za'ai.

"Mommy kisa Ikram ta kawo min invitation dan Allah". Reyhana ta fad'a.

" Idan ba'a kawo ba kenan bazaki jeba?" Mommy ta tambaya.

"A'a ba haka nake nufi ba wai da sena bawa ya Ahmad na d'aurin aure".Reyhana ta fad'a a sanyaye

" Bikin danginki ake ko nashi? dole seya je?" Mommy ta tambaya cikin fad'a.

Allah yasa lokacin Ahmad ya fita daga d'akin da ze iya ji.

"Eyyi baki amsan ba". Cewar Mommy.

"A'a ,toh Mommy Allah ya kaimu"Reyhana ta fad'a kwalla na cika a idanunta.

Daga haka sukai sallama gefe ta ajje wayar takaici ya isheta.Furucin Mommy ya bugi zuciyarta sosai taji ba dad'i koyaushe bata da buri irin Mommy ta dena tsanar mijinta ita da danginta."ko su Mommy basu kawo IV ba ai gidansu Amaryar sa kawo".Abinda ta fad'a a ranta kenan.

Tana cikin wannan batunne sega Ahmad ya shigo da sauri tayi 'ko'karin saita kanta karya gano wani abun.

" Da Mommy kikai waya?" Ya tambaya.

"Eh tana gaisheka".Reyhana ta fad'a.

Toh ina amsawa". Ya fad'a.

" Dama maganar biki ce ranar alhamis za'a fara". Reyhana ta fad'a.

"Ok toh Allah ya kaimu". Ahmad ya fad'a ba tare da ya sake cewa komai ba.

" Ranar friday d'aurin aure kuma". Ta fad'a.

Nan ma Allah ya kaimu yace.Reyhana a zuciyarta haushi ya mamaye dabadan ba da ba abinda zesa ta fad'a masa zancen d'aurin auren dande karya fuskanci ko da wani abun.

Haka abubuwa suka cigaba da gudana an biya Ahmad albashi ya d'anyi musu 'yar siyayya ta kayan tea da sauran 'yan abubuwa haka Umma ma.

Yau take alhamis ranar kamu,Reyhana ba ita ta shirya ba se 4:30pm ,su Mommy kuwa su ajinsu ko zata je da wuri gidansu Amarya idan yaso lokacin kamun yayi se a rankaya a tafi amma suka ji shiru.

Da Ikram tace zata kirata Mommy ta hana ta.Wajajen 5 kowa ya hallara hatta Amarya tazo waje ya cika ana shagali mutane dayawa suna tambayar Reyhana Mommy har ta gaji da cewa tana hanya.

Reyhana ba ita ta 'karaso ba se 5:35pm saboda yanayin hanya.Walida ce ta hangota da sauri ta 'karasa gunta.

Mommy tana zaune kan kujera suna gaisawa da wasu ta hangesu suna 'karasowa.Tun daga nesa Mommy take hararar Reyhana har ta 'karaso.

Seat ta samu ta zauna ta gaisheda mutanen wajen sannan Mommy da ta gama 'kulewa.

"Ina wuni Mommy". Ta gaisheta.

" Bansani ba,sannunki da 'ko'kari kowa ya gama hallara banda ke se tambayarki ake harna gaji da yin magana,kin kyauta kenan?" Mommy ta fad'a rai a 'bace.

"Mommy naga wai da yamma ne". Cewar Reyhana.

" Ke a matsayinki yaci ace se yamma zaki zo sekace ba 'yar uwakki ba".

Ai Mommy tana cikin yi mata fad'a sega Anty Asma'u itama ta fara zazzaga mata nata,Reyhana jitai bikin dama bata zo ba gashi ba abinda ya sake ci mata rai irin yadda rashin zuwan nata ya shafi Ahmad. Shi suka koma blaming suna cewa "Watoh shi kulle yake seya ga dama zaki fito". Mommy ta fad'a.

'Kila ma seda ta gama yi masa girki". Anty Asma'u ma ta fad'a.

Wani zazzafan hawaye ne ya sakko mata ,Allah sarki Ahmad abinda shi ke ta tuna mata tayi sauri ta shirya yamma nayi shine aka la'kaya masa abinda beba.

Ganin ta fara hawaye yasa suka rabu da ita karta tara musu dangi dan idan ta fara kuka ba kanta,kowa seya san tana yi.

Reyhana ko hoto da Amarya batai ba tana zaune gu d'aya Ikram ce daga baya tazo take bata ha'kuri dan su Mommy sun tashi daga gun.

Ganin Maghreb na shirin yi yasa ta tashi,zuwa tayi har inda su Mommy suke tayi musu sallama ta tafi duk cikinsu ba wanda yai maganar tafiyarta da wuri.

Mommy basu suka tafi ba se wajen 9:00pm.Aiko Walida bayan sun koma gida suna shiga ta nufi Abba da suka tarar zaune parlour.

" Abba kasan mey Mommy sukai wa yaya?" Cewar Walida.

"A'a Walida sekin fad'a". Abba ya fad'a tare da tattaro attention kanta.

" Wlhy kuka tayi suna mata fad'a". Ta fad'a harda zaro ido.

Mommy kuwa da tin shigowarsu suka haye sama ita da Ikram dan a gajiye suke.

"Da gaske Babyna?" Abba ya tambaya yana son sake tambatarwa.

"Da gaske nake Abba ka tambayi Ikram ma kaji hadda Anty Asma'u sukai ta mata.." Bata 'karasa ba Abba ya katseta.

"Ya isa aje a kwanta dare yayi kinji". Cewar Abba yana lalla'bata.

Kan kice me ta haye sama abinta Abba kuwa ya shiga tunanin abinda sukaima Reyhana.

Ita kuwa Reyhana sanda ta koma gida Ahmad ya kula da yanayinta amma seta ce ciwon kai take ji.Ko abincin dare bata iya girkawa ba dama akwai ragowar na rana suka ci suka kwanta.

Washegari da safe kasancewar d'aurin auren 11am ne Reyhana da kanta tace wa Ahmad ya ha'kura da zuwa tinda yana da makaranta,ko ba dan haka ba dama bata so yaje dan tana gudun kar a wula'kantashi.

Ita kuwa sunyi dashi zata tafi gidan bikin 12pm amma yana fita ta dawo tayi kwanciyarta koda ta farka aikace-aikacen gidanta tayi ta d'ora girkinta.           Mommy kuwa suna can ana ta hotunan d'aurin aure ,gefe guda ta ware tayi dialing number Reyhana.

      " Reyhana lafiya baki zo ba?"Mommy ta tambaya.

      "Na tashi banda lafiya ne".Tayi 'karya harda narke murya.

      " Bakida lafiya? Har ankon dinner gashi kuma anyi miki".Mommy ta fad'a.

      "Idan na samu sau'ki sena shigo anjima". Reyhana ta fad'a.

       " Toh Allah ya sawwa'ke".Mommy ta fad'a sannan ta katse wayar.

      Reyhana kuwa koda rana tayi bacci ta koma abinta dama Ahmad ze biya gidan Umma daga makaranta.

    Haka aka gama biki bako d'uriyarta ,Ahmad daya dawo ya tamabayeta tace masa ciwonkan be dena ba.

    Mommy dama ta fidda ran zuwanta,akayi dinner ba ita.Washehari ma yini bata jeba haka aka 'kare biki ba ita.

     Ranar sunday da safe Abba yana gida yayi kiran Mommy, ita bata kawo akan Reyhana bane bama.

       "Mommyn Walida me Reyhana tayi miki?" Ya tamabayeta bayan ta zauna.

      "Bangane ba". Mommy ta fad'a tana neman 'karin bayani.

       " A biki mana an fad'amin kun saka tayi kuka a dalilin mey?"

       "Ita Reyhanan ce kenan ta fad'a maka ,amma meyasa bata fad'a maka dalili ba?" Cewar Mommy.

       "Sam ba ita bace and tambayarki nayi ba canayi ki tambayan ba". Abba ya fad'a ba watsa cikin lamarin.

    D'an  gyara murya tayi Mommy kafin tace." Fad'a ne bata so,dan me zata zo biki kusan to 6 kowa yana tambayarta amma shiru abinda tutuni an fad'a mata".

     "Yanzu akan bikin shine kuka rifeta da fad'a? Yayi kyau Maryam kece da ita ko mijinta idan yayi niyyar hanata zuwa ya zakiyi? Dole fa ki ha'kura wannan yaran mijinta ne ko ki yarda ko karki yadda ,kuma bana so haka ya sake faruwa idan ba haka ba rai ze 'baci walhy". Abba ya fad'a cikin fushi.

    Mommy da ta gama 'kuluwa yana gama maganar ta tashi ta fita bako bada ha'kuri.

     Ai d'akin Ikram ta wuce direct,bacci ma take taji ana d'ala mata duka a cinya.

      " Tashi zaune nace!" Mommy ta fad'a.

     A zabure ta mi'ke dan dukan ya shigeta"Mommy !"Ta kira kamar zatai kuka.

       "Kece kika fad'a wa Abbanku nayi wa Reyhana fad'a a gidan biki?" Mommy ta tambaya.

     "A'a bani bace". Ta amsa.

      " Waye idan bake ba?"

       "Sede Walida". Ikram ta fad'a.

      Mommy kai ta kad'a ta wuce d'akin Walida,itama tana bacci ta tasheta.

      " Kece kika fad'a wa Abbanki nayi wa yayarki fad'a koh?"

      "A'a canai tayi kuka de". Walida ta amsa tana murza ido.

     Rankwashi taji akanta wanda batayi tsammani ba,da sauri ta dafe gun tana shirin kuka taji dundu a bayanta 'kwarara uku.        " Sarkin surutu manya suna magana kina zuba musu ido shashasha na sake ji kin fad'a masa wani abun".Mommy ta fad'a ta dungure mata kai ta fita.

     Walida kuwa kai ta cusa cikin fulo ta fara rera kuka wanda baza a jiyota ba.

             ****     Reyhana yau baccinsu suka sha se wajen 10 am suka tashi ,nan tayi musu abincin breakfast bayan sunci sukai wanka.

      Kayan wankinsu ya taru saboda haka koda Ahmad yace ze kai mata nata tunda shi dama baya kai wanki da kansa yake yi.Reyhana tace ya bari kawai sayi wankin tare yau tunda yana gida sesiyi ba yadda be da ita ba tace a'a dole ya ha'kura.Ganin baida isassun kud'i yasata yin haka dan kusan duka salary d'in a abinci ya 'kare.          Turyan turyan suka fara kusan shine 'karfin wankin daga baya jagab sukai da ruwa dukansu wannan ya she'kawa wannan haka sukayi tayi har suka 'kare wankin.

              'Bagaren Mommy kuwa koda suka fito breakfast dinning table, Abba ya lura da jan da kumbura da idanuwan Walida sukai.

     "Walida meya sami idanki? Ko kuka kikai?" Abba ya tamabayeta.

     Kowa kallonsa ya dawo kanta bare Mommy da take jira taji me zata ce.Wuri-wuri tayi da ido tana tsoron Mommy karta fad'a ta sake dukanta idan ta kalli Abba seta kalli Mommy ta rasa ya zatai.

      "Fad'a min kinji meya sami idon?" Abba ya sake tambaya.

AR²💖     *Please comment,vote and share, love you all💕*

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣6⃣

Walida da ganin irin kallon da Mommy keyi mata yasa tace"Abune ya shigemin idon shine na sosa yayi ja".

"Ayya ya fita yanzu?" Abba ya tamabaya.

"Eh". Ta amsa.

Mommy kallonta tayi alamar kin ceci kanki d'innan.

*** Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa yau da dad'i gobe babu.

Reyhana tana d'aki tana nikke jera kayan data goge a wardrobe. Sallamar yaya Ahmad yasa ta fitowa dan wataran dama yana fita da key idan ya dawo ya bud'e base yayi knocking ba.

A sanyaye ya 'karaso d'akin." Sannu da dawowa".Reyhana ta fad'a.

"Yawwa". Ya amsa a sanyaye.

"Yaya wani abune?" Reyhana ta tambaya.

"Ahnn...kainane yake ciwo". Ya amsa.

" Ayya sannu kayi wanka sena zubo maka abinci kasha magani".Ta fad'a.

Tashi yayi ya rage kayan jikinsa ya shiga toilet,Reyhana kuma ta fita had'o abinci.

Sitting room d'in ya zauna yaci abincin kad'an -kad'an yake amsata.Paracetamol ta 'ballo masa ta bashi ya watsa,kan kujera ya samu ya haye yayi rigingine hannunsa ya d'ora kan goshi kamar me bacci amma ba baccin yake ba.

Reyhana kuwa bayan data kwashe kwanikan d'aki ta koma ta cigaba da abinda take dan tana tunanin ko gajiya ce tasa shiyasa ta bashi space.

Shikuwa ba abinda yake tunani se ta yadda ze 'bullo mata da wannan al'amari daya faru dashi.

Da asr ya tashi yaje masallaci bayan ya dawo kuma ya tarar tana kitchen had'a abincin dare saboda haka ya koma d'aki yana jiran anjima ya sanar mata.

Se bayan da suka kammala cin abincin dare sannan ya zauna da ita.

"Reyhana bansan ya zaki d'auki wannan abun da zan fad'a maki ba,ina me baki ha'kuri". Ahmad ya fad'a.

" Yaya mene ka fad'amin du na tsorata".Ta fad'a.

"Reyhana.. aa..an sallameni daga makarantar da nake teaching". Ya fad'a da 'kyar.

"Subhanallahi yaya meya faru? Meyasa?" Reyhana ta fad'a hankalinta a tashe.

"Director na school d'in ya fad'a mana cewa malaman school d'in sunyi masa yawa kuma biyan salary yana nema ya gagareshi and kuma yanzu sunfi son masu degree certificate".

Shiru tayi Reyhana hannunsa biyu ta ru'ko." Yaya addu'a kawai itace mafita ba damuwa ba jarabawace garemu,Allah ya musayya maka da wanda yafi wannan Yaya".

"Ameen". Ya amsa.

Sosai ta damu amma ta danne irin damuwar data shiga,ranar kusan dukansu basi cikakken bacci ba musamman Ahmad.

Ko washegari daya tashi yana d'aki ko breakfast d'in arzi'ki beba ya kwanta yana tunane-tunane.Reyhana ce ma take d'an kwantar masa da hankali da taga yana tunani seta zauna ta fara yi masa hirarraki kota kunna masu kallo da rana,haka da daddare dukansu tashi sike sallah.

Ko Umma be fad'a mata ba bayaso ta shiga damuwa,yanzu fafutukar neman abinyi ya tsindima.A rana seya fita yafi so uku,a haka har ya samu wajen aiki,sunayin sliding window.

A kullum ake biyansa kud'in ba masu yawa bana sede addu'a kawai.

Yau bayan fitarsa wajen 9am ko karyawa beba dan tashi sukai gas d'inma ya 'kare gashi ba kud'in refilling danma Allah yasa da 'yan wasu kud'i a hannunsa da Abba ya aiko mata sanda Sageer yazo.

Ragowar 3k ne dan haka da kanta ta fita bata da me aike.Ganin kayan abincin su sun 'ka'kkare ta sissiyo wasu abubuwan se ragowar ta d'uro gas.

Ahmad ba shi ya dawo ba se 3pm,bayan watsa ruwa ya fito sitting room be ganta ba dan haka ya le'ka kitchen.

"Azizaty ina kika samu kud'in gas?" Ya tambaya.

"Hmm karka damu akwai wasu 'yan kud'ine a guna shine nayi amfani dasu nayi siyayya". Reyhana ta amsa.

" Meyasa kikai haka Reyhana? Kud'inki ne na amfanin kanki kuma shine..."

"Is ok wannan ba wani abu bane me zanyi dasu idan banyi hakan ba?karka damu mana".

Shiru yayi yana kallonta a ransa yana jin sonta na sake ha'baka a zuciyarsa,ta wani side d'in kuma tausayinta dan bata taso cikin irin wannan rayuwarba.

*** Mommy kuwa batasan halin da Reyhana ke ciki ba dan bata fad'awa Mommy ba.

Gobe zasije wata dubiya dan haka tasa Ikram ta sanar wa Reyhana.

Ahmad yana zaune ta amsa kiran Ikram d'in saboda haka bayan ta gama wayar ta sanar masa.

Washegari around 2pm ta isa gida,Walida da gudu ta tarota dan ta hango shigowarta.

" Yaya oyoyo!" Ta fad'a .

"Walidandan 'yan matan Mommy".Reyhana ta fad'a tare da rugumota.

Hannunta a nata suka 'karasa ciki ,Mommy tana d'aki ta fito.

" Mommy ina yini ".Reyhana ta gaisheta.

" Lafiya lau".Ta amsa.

Yau ba kamar rannan ba fuskarta a sake take ko dan ganin ba Ahmad..

"Ina Ikram da Bassam?" Ta tambaya.

"Suna d'aki". Mommy ta amsa.

" Walida maza jeki ce inno ta kawo mata masa(wainar shinkafa)".Mommy ta fad'a.

Tashi tayi kamar yadda Mommy ta umarta,inno ta kawo mata wainar Walida ta taho da juice.

Kad'an taci wainar tace ta 'koshi,bayan sunyi sallar asr suka fita,Mommy ce da kanta ta jasu a motarta.

Kasancewar dubiyane basu dad'e ba sosai,Mommy ta biya dasu gidan Anty Asma'u.Reyhana sam bata so zuwansu chan ba dan tasan halin Anty Asma'u gashi Ahmad's besan da wani biyawa gidan Anty Asma'u ba ,tana kallo har suka isa bata iya cewa komai ba.

"Ahh! Yau harda Reyhana lalle irin wannan ba zatan". Cewar Anty Asma'u.

D'akinta ta jasu kamar yadda suka saba da hakan,ita de Reyhana jikinta a sanyaye.

" Anty ina yini". Ta gaisheta bayan sun zauna.

"Lafiya lau Reyhana yau an samu de an fito". Ta fad'a.

" Atoh na tusota a gaba da baza ki ganta ba". Mommy ta fad'a.

Yaran Anty Asma'u ne suka shigo suma suka gaggaisa dasu,a ciki akwai 'yan mata biyu kusan sa'annin Reyhana ne shine suka soma d'an hira.

Me aiki tasa ta kawo musu abinsha,suna zaune har maghrib ita de Reyhana hankalinta ya fara yin gida.

Gashi tana tsoro tayi wa Mommy magana tace ta fiya zumud'in gidan miji dan haka tayi shiru.

"Reyhana de ta gaji naga tayi shiru". Cewar Anty Asma'u.

" Toh ai nima yanzun nake so mu tafi".Mommy ta fad'a.

Seda sukai sallah tukunnan lokacin har 7:25pm tukun suka fito ,har bakin gate ta rakosu sukai sallama.

A mota suna tafiya sega kiran Ahmad.

"Hello yaya". Reyhana ta fad'a bayan data d'aga.

" Azizaty naji ki shiru".Cewar Ahmad.

"Gani ina hanya ba dad'ewa zan 'karaso". Ta fad'a.

" Toh sekin dawo"

Yana katse wayar ta kalli Mommy a ranta tana fad'in Allah yasa ba gidan Mommy zasi wuce ba.

Tana wannan tunanin taji Mommy tace "chan zami koh?"

"Eh". Ta amsa da saurinta.

Mommy har 'kofar gida ta kaita,tana fita daga motar sega Ahmad yana fitowa daga gida zaije masjid.

Reyhana ce ta fad'a masa Mommy ce ta kawota.'Karasawa yayi har k'ofar mota Mommy ta sauke glass d'in motar ya gaisheta cikin rissinawa.

Mommy tana tafiya ya wuce majid karya makara Reyhana ta shiga gida.

Reyhana wani dad'i taji lokacin da ta le'ka kitchen taga ya siyo gurasa saboda haka miya kawai zatayi.

Tana dire bag d'inta da mayafi ta shiga kitchen had'a miyar a d'an 'kan'kanin lokaci ta kusan kammalawa.

Ahmad daya shigo ya tarar da ita a kitchen.

" Uwargida daga dawowa se girki kuma".

Murmushi tayi tare dayi masa sannu da zuwa.

"Ai naga ka siyo gurasa kaga miyace kawai zanyi nama kusa gamawa". Ta fad'a.

" Toh sannu da aiki".Ya fad'a.

"Yawwa". Ta amsa.

Tana gama miyar ta turara gurasan ta sako musu.

" Azizaty ai baki ci dayawa ba". Ya fad'a.

"Ya isheni naci waina a gida". Ta fad'a.

" Mun biya gidan Anty Asma'u fah".Reyhana ta fad'a dan bata so ta kasance me 'boye-'boye.

"Haba,daga gidan dubiyar kuka biya?"

"Eh". Ta amsa.

" Toh ya suke?"Ya tamabya ba tare da ya nuna komai ba.

"Lafiya lau". Ta amsa.

Haka suka cigaba da hirarrakinsu kafin lokacin kwanciya yayi suka kwanta.

*** Washgari Reyhana ta farka jikinta li'kis dan zazza'bi daya rufeta da'kyar tayi sallah.

" Azizaty ko asibiti zamu?"Ahmad ya tambayeta.

"A'a mu bari ze sauka".Ta fad'a.

Goshinta ya ta'ba yaji da zafi amma ba kamar da asuba ba.

Da kanshi ya had'a mata breakfast ya kawo mata.

" Azizaty ki daure ki sha tea seki sha magani".Ahmad ya fad'a.

Da taimakonsa ta mi'ke daga kwance,tea d'in ta d'an kur'ba.

"Kici doyan ko kad'anne". Ahmad ya fad'a.

'Kwaya d'aya tasa a baki da'kyar ta iya had'iyewa ta kora da tea.

Sede tunda ta had'iye ta kasa sukuni saboda tashin zuciya da ya tunkaro mata.

Ahmad yana mata sannu kai kawai take kad'awa ta kasa ko magana.

" Azizaty ki 'kara ci ko kad'an ne".

Kai ta girgiza masa alamar a'a.

"Azizaty ki...." Be 'kare maganar ba yaga ta tashi da hanzari ta nufi toilet.

Seda ta amayar da abunda ke cikinta kaf,Ahmad ne ya wanke wurin ya taimaka ta koma d'aki.

Kan gadon ta zauna ta jingina Ahmad yana mata sannu.Daya ta'ba goshinta yaji ba zafin.

"Kin dena jin sanyin?" Ya tambayeta.

"Eh". Ta amsasa.

Kwanto da kanta jikinsa yayi yana shafa bayanta,a haka bacci yayi gaba da ita.

AR²💖

*Need your comments, votes and share.Love u all😘*

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣7⃣        Ranar Reyhana wuni tayi a kwance ,Ahmad se ha'kura yayi da fita. Jollof taliya ya dafa musu taci kad'an ,shima be iya yaci dayawa ba.

Washegari da safe ya taimaka mata tayi wanka ta shirya.

"Reyhana tashi fa zaki mu tafi asibiti". Ahmad ya fad'a.

" Mu bari ze fa sauka zazza'bin".Reyhana ta fad'a murya tana rawa.

"Ba shawararki fa nake nema ba tashi zaki nace mu tafi yanzu". Ahmad ya fad'a in serious turn.

Tana turo baki ta tashi ta zira hijab da takalmi.A hanya yana mata hira ta'ki ko tanka sa.

Reyhana ba wani abu yasa bata son asibiti ba sedan tana tsoron allura(kamar ni😂).

Suna isa asibitin zuciyarta na sake tsorata a sanyaye ta shiga gun likita.

Koda ta gama zayyane masa abunda yake damunta test na mp da PT ya rubuta mata.

Data fito Ahmad yana tamabayarta takardar kawai ta mi'ka masa, nan suka tafi laboratory. Wajen blood collection da'kyar ta yarda aka d'auka jininta tund PT d'in serum ne.

Bayan kamar 20min aka bata result tana fitowa ko ta kansa bata bi ba.Yana mata magana amma ta'ki kula sa illa hannunta data ri'ke kamar wacce ta karye. Hakan yasa kamar yayi dariya amma dan kar ya had'a mata zafi biyu ya maze kawai.

Koda ta bawa doctor result d'in daya duba wasu 'yan magungunan ya rubuta kad'an sannan yace.

" Congratulation".

Kallonsa ta soma yi cikeda rashin fahimta.

"Kina d'auke da juna biyu,zaki je yanzu wajen scanning ga wasu maguguna da na rubuta maki Allah ya 'kara lafiya". Doctor d'in ya fad'a.

      " Ameen nagode".Reyhana ta fad'a bayan ta kar'bi katin.         Lokaci guda tsoro da farinciki ya ziyarce ta,tana fitowa Ahmad ya 'karaso inda take "Azizaty me doc yace?"

       Mi'ka masa katin tayi ba tare da tace komai ba.

       "Azizaty wannan kike 'boyewa daman?" Ahmad ya fad'a fuskarsa d'auke da murmushi hatta ha'koransa seda suka fito.

     D'an waigar da fuska tayi tace"Nima ai d'azun ban duba ba ".

       " Maman baby me tsoro".Ahmad ya fad'a.

      Tafin hannunta ta d'ora a bakinta tana murmushi amma har lokacin bata waigo ba.

      Wajen scanning d'in suka 'karasa ba dad'ewa akai mata ya nuna 5weeks.

       Dad'i gun Ahmad baze misaltu ba itade Reyhana kawai takardan ta zubawa ido dukda kuma cikin ranta itama farincikinne.

      A hanyar dawowa ya sayi fruit da balangu suka komo gida a napep yana ta mata hira itade uhm da a'a ne amsarta.           Suna shiga gida Ahmad ya sata a gaba seta sha fruit da naman.Kad'an ta samu taci tace ta 'koshi.

       "Kina so ki bar Babynmu da yunwa ne?Ahmad ya fad'a.        " Nafa 'koshi anjima na sake ci".Reyhana ta fad'a.

    "Toh yanzu me kike so?" Ya tamabyeta.

     "Bacci"Ta amsa.

     " Laa! Azizaty yau bacci kike so ba niba".Ahmad ya fad'a dan so dayawa ya saba tamabayarta haka seta ce masa shi.

      "Toh nima shikenan ,babynmu nake so". Cewar Ahmad.

     Reyhana murmushi kawai tayi ,tashi tayi da niyyar tattare kayan gun da sauri Ahmad ya ri'ke hannun.

     " Azizaty rufan asiri mey ta kaikai yin aiki a wannan lokacin kwantawa zaki ki bacci ba abinda zaki ta'ba".Ahmad ya fad'a.

       Hannunta ya ri'ke suka nufi d'aki ,kan gado ya kwantar da ita ya saisaita mata fankar d'akin ,yana zaune gefen gadon har seda tayi bacci tukun ya koma sitting room.

      Kayan wajen ya tattare da kwanukan da suke ba a wanke ba ya d'aurayesu.

       Reyhana baccinta tayi ta 'koshi se wajen 2 ta farka tayi sallah nan ta tarar da abinci shinkafa da miya koda ta tambayeshi shi waya dafa yace ai umma ce ta turo yaro ya kawo.

      "Kenan fad'a mata kai bani da lafiya". Cewar Reyhana.

      " Ehyi ta kira kina bacci ma".Ahmad ya fad'a.

      "Ya babynmu ya tashi?" Ya tambayeta tare da d'ora hannunsa ya shafa cikinta dayake a shafe.

       Dariya tayi tana kallonsa "Taya zansani nikam?" Ta fad'a.

     "Kinjiki tun yaushe ma ni ai yanzu naji tunda ke baki sani ba". Ahmad ya fad'a.

      " Hmm!"Abinda kawai ta fad'a tare da girgiza kai tana murmushi.

       Da kansa yayi ta bata abincin kuma taci da yawa ba kamar jiya ba ,maganin ya 'ballan mata tasha.Zazza'bin ma ya sauka yanzu se kasala de gashi baccinma ba dika ya tafi ba.

               ***

     Se washegari ya koma aikinsa ,itama Reyhana ta samu sau'ki zazza'bin yawanci se da dare takeyi kad'an se bacci ba wuyar tayi bacci.

        A 'yan kwanakinnan haka take daga shingi'da se bacci ya kwasheta ,idan kuwa ya fita tana d'an yin abunda zatai se bacci wani sa'in ko shigowar Ahmad bata ji.

        Umma ma tazo ta duba ta har gida ,su Ikram ma sunzo  lokacin da bata jin dad'i.

         Yau tana zaune bayan tayi wanka ta shirya ,haka kawai taji tana son cin d'ata.

      Da farko tayi tunanin ko ta kira Ahmad idan ze dawo ya taho mata da ita,ganin bazata iya jiran har tsahon wannan lokacin ba ta yafa mayafi wasu 'yan chanjin dake wajenta ta d'auka ta le'ka 'kofar gida Allah yasa ta hangi wani yaron ma'kwafta nan tayi kiransa ta basa kud'in ya sayo mata.

      Bayan 'yan mintina ya dawo Reyhana ana rawar jiki aka amsa ta shige gida nan danan ta d'aureye ta fara gutsurar kayanta.

     Taci kusan uku jin amai ze tunkaro ta ta ha'kura.Ta kunna TV tajiyo knocking, hijab ta zira ta tafi bud'ewa.

     Tasha mamaki ganin Mommy a tsaye gefenta Anty Asma'u.

       "Laa! Ashe kune, sannunku da zuwa". Ta fad'a.

       " Yawwa".Suka amsata.

       Ciki ta 'karaso dasu,har 'kasa ta dur'kusa ta gaishesu.

       "Ina yini".

       " Lafiya lau".Suka amsa.

         Tashi tayi ta  had'o musu zo'bo da yake a fridge se ruwa ta jero musu a tray.

       "Ya jikin naki su Ikram sunce kinyi zazza'bi". Mommy ta fad'a.

        " Na samu sau'ki".Cewar Reyhana tana ajje tray d'in.

      "Toh Alhandulillah". Suka amsa.

      " Sageer ne ya kawo ku?" Ta tamabaya bayan ta zauna a kujera.

      "A'a shi ya tafi makaranta ma ,nina tu'komu". Mommy ta amsa.

     " Ya Ahmad d'in?" Anty Asma'u ta tambaya dan Mommy ba tamabaya zatai ba.                    "Reyhana inci?" Anty Asma'u ta  tambayeta lokacin da ta d'auki d'atar dake hannun kujera.

        Dariya tayi Reyhana sannan tace "Laa kici mana Anty".

      Anty Asma'u dama tana son d'ata inde ta hangeta a hanya takan tsaya ta siya.

      Mommy kuwa ganin d'atar yasa hankalinta ya kasa kwanciya ,a sanyaye ta kalli Reyhana ta lura da sauyin da tai.

       Ta 'kara fari ga ta d'an murje.

         Kitchen ta shiga ta had'a miya dan tattasan dama a soye yake.A 'yan mintina ta 'karasa ta zubo musu couscous d'in.

         Mommy idanta na kan abincin da Reyhana take zuba musu a plate so take taga koda nama ko babu.

     Aiko de babun ta gani a take ta ta'be baki.

      D'an kad'an taci tace ta 'koshi gara Anty Asma'u ta d'an ci dayawa.            Reyhana ganin d'atarta biyu ne ya ragu yasa ta tashi ta shige d'akinta ta kira Ahmad.

      " Yaya ya aiki?" Reyhana ta tambaya.

        "Lafiya my Azizaty, ya babynmu?"

        "Lafiya lau". Ta amsa.

        " Yaya d'ata nake so".Reyhana ta fad'a.               "Iye! Babyn mu zeci d'ata,kunyar first born kike koh".Ahmad ya fad'a.

          " Kunya kuma?" Reyhana ta fad'a tana turo baki.

           "Ehyi idan ba kunya kike ba  repeat what i will say".

           " Babynmu zeci d'ata".Ya fad'a.

           Shiru tayi a hankali tace "Babynmu zeci d'ata ".

         " Banjiba".Ahmad ya fad'a.

         "Kafa jini".Ta fad'a kamar zatai kuka.

         " Azizatyn Ahmad karki kuka shikenan zan taho maki dashi".

         "Mommy fa sunzo suna parlor ma". Ta fad'a.

         " Ki gaida min dasu kafin na dawo".Ya fad'a.

         "Toh seka dawo".

         " OK bye I love u two ki shafamin babynmu".

         Dariya tayi sannan tayi hanging ,komawa tayi wajensu Mommy suka cigaba da hira.

         Wajen 4:30pm suka tafi Ahmad be samu ganinsu ba.

       Reyhana shikenan kuma yanzu bata zama ba d'ata koyaushe cin d'ata wani sa'in ma ta gwammace taci d'ata da abinci abun har ya ishi Ahmad.

       "Yau fa ba cin d'ata ni babynmu ya gaji". Ahmad ya fad'a yana zira takalmansa.

       " Dan Allah Yaya ka taho min da ita yau bansan inda zansa kaina ba idan ban ci ba".Reyhana ta fad'a cikin shagwa'ba.

     "Shikenan amma yau sekin ci abinci sosai zaki ci kin yarda?"

      Kai ta d'aga alamar eh ,daga haka  sukai sallama ya fita.

        Haka rayuwa ta cigaba a kwana a tashi yau cikinta wata biyar ya fito.Ta fannin aikin sa de se addu'a inda Allah ya taimaka Reyhana mace me ha'kuri so da dama Mommy seta tayiwa Abba complain akan zaman Reyhana a gidanta dan yanzu ta gano baya teaching d'in.

      Abba idan ya kira ya tambayi Reyhana koda wata matsalar seta ce a'a,wani sa'in yakan tura Sageer ya kai mata kud'i ko kuma idan tazo ya bata. Sede kwana biyunnan 'kwaras suke basuda kud'i gashi Umma bata jin dad'i ana ta zarwar kaita chemist amma ciwo seya dawo,a kaita asibiti abu ya gagara.

      Reyhana tana zaune tayi nisa cikin tunani wani idea d'inne ya fad'o mata aikam da sauri ta kira sageer a waya tace yazo gidanta.

      Daga school ya samu ya biyo.

     "Sageer kaga dama phone d'ina nake so ka sayar mini seka sama min ko 'karama ce amma fa promise me bazaka fad'awa Mommy ba". Reyhana ta fad'a.

      " Kai yaya ya zaki sayar da phone naki ki fad'awa Abba mana idan kud'i kike so".Sageer ya fad'a.

       "A'a bazan fad'a masa ba kana kallo ko sati ba'ayi ba ya bani 10k kuma sannan na sake tamabyarsa,nide kawai inda zaka sayar mini". Reyhana ta fad'a.

      " Toh shikenan kawo wayar".Ya fad'a.

         "Promise baza ka fad'a mata ba".

         " Bazan fad'a mata ba ".

         " Good".Cewar Reyhana tana zare sim d'inta da mcard.

          Wayar ta mi'ka masa ya tafi,dama tuntuni bata jin dad'i taga Ahmad yana ri'ke 'karamar waya ita kuma babba(Allah sarki Reyhana).

        Later wajen 4pm ya dawo ,an sayeta 16k ya saya mata 'karama 5k saura 11kya bata.

      Ahmad sanda ya dawo gida bayan yaci abinci ta d'akko kud'in.

     "Yaya kaga nace wannan kid'in me ze hana akai umma asibiti dasu".Ta fad'a tare da mi'ka masa.

       " Ina kika sami wannan d'in?"Ahmad ya tambayeta.

       "Uh..wayata ". Ta amsa.

        " Wayarki".Ya kalleta cike da mamaki.             "Dama fa ta fara samun matsala shine na sayar na sayi wata wannan kuma sauran kud'inne". Tayi 'karya dan ba wani matsala da wayar ta samu.

       " A'a bazan kar'ba ba meyasa kikai haka ,taya zaki sayar da wayarki".Ahmad ya fad'a dan beji dad'i ba.

        "Lefi ne idan nayi hakan?" Reyhana ta fad'a kamar zatai kuka.

        "Nide na fad'a maki bazan kar'ba ba".

       Nan take Reyhana ta fara zubar da hawaye hadda shishshi'ka.

       " Kukan kuma na miye daga nace bazan kar'ba ba".Ahmad ya fad'a duk ya damu dan baya son kuka.

       "Toh kafi so mu cigaba da kallon umma a haka?"Ta fad'a cikin kuka.

        "No amma..." Be 'karasa ba ta katse sa.

      "Dan Allah Yaya ka kar'ba ,naji wataran ka bani amma yanzu ka kar'ba". Ta fad'a duk da kuwa ko wataran ya bayar ba kar'ban zatai ba tayi hakan ne dan ya kar'ba.

         Shiru yayi bece komai ba ya tafi tunanin halin da umma me ciki dan ko yanzu daya barota tana kwance.

        " Ok naji zan kar'ba,shikenan?"

       Reyhana kai ta kad'a tana murmushi,shikuwa kallonta yai  a ransa yana jin 'kaunarta ,jawota jikinsa yayi yana shi mata albarka.

         Washegari da safe yaje gidan umma ya tafi da ita asibiti, malaria ne yaci 'karfinta har ruwa aka 'kara mata se allurai da magunguna da aka rubuto mata,se yamma suka komo gida ,har 'yan siya-siye yayi mata bashi ya komo gida ba se bayan maghrib ya komo gida dama akwai wata 'yar uwassu da take a kano ita take kula da ita.

        "Ya jikin umman ?" Reyhana ta tambaya.

         "Ta samu sau'ki ammata 'karin ruwa sai maguguna da allurai dasuka bata".            " Allah ya 'kara sau'ki,Yaya gobe zani fa na sake dubata".Reyhana ta fad'a.

         "Toh Allah ya kaimu Azizaty ta,ya babynmu?" Ahmad ya fad'a yana shafa cikin.

    Reyhana murmushi tayi itama ta d'ora hannunta kan nasa.

                 ***

    Mommy de an samu Abba ya tisata a gaba sunje duba umma ,Abba yayi mata siyayya ta dubiya suka kai.

     Hakan ba 'karamin yima Reyhana dad'i yayi ba.               Cikin ikon Allah Umma taji sau'ki sosai.Akwai wani biki daya taso a Zaria Umma datace zata je Ahmad ya'ki yace ta ha'kura ai bata jin dad'i.

     Reyhana kuwa yana fad'a mata tace su suje mana,ba yadda beyi da ita ba ta'ki ha'kura har umma ta fad'awa ita kuwa ta goyi bayanta dole ya ha'kura.

      Reyhana se d'oki ake tun ana washegari ta gama had'a kayanta shi Ahmad dariya ma yake mata.

       "Maman baby kwana nawa za'ayi ne irin wannan shiri haka".

        " Kwana uku mana".Ta amsa.

       "Uku ? Babynmu kuma yace d'aya". Ahmad ya fad'a.             " D'aya haba de zami fa ziyara".

       "Ziyara? Toh ai duk wa'anda za'a je gidan nasu zaki gansu gurin bikin".Ahmad ya fad'a.

         " Toh naga gari".Ta fad'a.

         "Maman baby yawo de ,babynmu baya son yawo".

      Haka sukai ta  fafatawa har sukai bacci ,ita a lalle kwana uku.

        Washegari wajen 10am suka nufi Zaria tunda 12pm za'ai d'aurin auren.

       Kafin su isa 'kafarta tayi tsami,an tarbesu cikin mitintawa sun gaisa da 'yan uwa da abokan arzi'ki,gidan wani yayan umma suka kwana washegari aka rarrakasu gidajen wasu 'yan uwan kowa yana murnar ganin matar Ahmad ,around 3:30pm yace su tafi Reyhana haushi ya kamata dan ita sam bata gaji ba.

       Wata 'yar'kanwar umma ana ce mata Zainab tare suka dawo kano da ita tunda ana hutun makaranta ,bata fi 13yrs ba wasu lokutan dama tana zuwa hutu gidan umma.

            ***    Mommy suna zaune da Ikram tana so a turawa Reyhana wasu necklace sample ta za'ba Abba ze siya musu.Ikram koda ta duba  last seen nata taga an dad'e.

        " Mommy anya kuwa zata gani naga bata hawa fa yanzu".Ikram ta fad'a.

         "Ni ayya bata ma siyar da wayarta ba da rannan da muka je duba sirikarta 'karama ce a hannunta". Mommy ta fad'a.

        " Anya kuwa bara de na kira".Cewar Ikram.              Bayan Reyhana tayi picking da Ikram ta tambayeta seta ce wayar ta samu matsala be.

        "Mommy wayarce wai ta samu matsala".Ikram ta fad'a still wayar na kunnenta.

            " Toh anjima Sageer zezo ya kai mata gyara ".Mommy ta fad'a.

     " Yaya sageer zezo ya kai miki gyara".Ikram ta fad'a.

        Reyhana jin haka yasa ta hau inda-inda "Uhmm..ai..ai yanzu na siyar da phone d'in dan ya 'baci sosai" .

         "OK toh dama sar'kane zaki za'ba Abba ze saya mana".

            " Toh kawai ki za'ba min ba damuwa".Reyhana ta fad'a.

        Daga haka sukai sallama,Mommy kuwa ko ba'a fad'a ba ta riga da ta gano.

           4:17pm Ahmad ya koma gida daga wajen aiki sede yau ba key a wajen gashi yana ta knocking bata bud'e ba.

         Reyhana kuwa bacci take lakadan,Ahmad har d'an 'karamin dutse ya d'auka ya bubbuga amma shiru.

       Ransa har ya fara 'baci dama a yunwace yake ga gajiya daya kwaso.

      Seda yai kusan 20min a tsaye kunnanta ya jiyo ,sede Reyhana tashi daga baccin da tai jikinta har rawa yake dan be isheta ba.

        "Mtchww!" Ta buga tsaki jin an sake yin knocking,hijab ta zira ranta a 'bace ta bud'e.....

AR²💖             *Ha! Long page koh,i just enjoyed typing it A&R🔥*

      *Please comment,vote and shares love u all wallah😘*

  Jasko💕

*ARZI'KI RABO*

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿-0⃣8⃣

Cikeda takaici yake kallonta a ciki-ciki yai sallama itama a hankali ta amsa ta matsa ya wuce.

     Shi ba abinda ya sake bashi haushi kamar yadda itama ta wani shareshi bako sannu da dawowa sema turo baki dayaga tanayi wanda besan dalili ba.

         Kayan jikinsa ya rage seda ya watsa ruwa tukun ya fito  da ba'kar T-shirt da blue jeans.Kitchen ya nufa ya zubo abincinsa da kansa, tana kallo ya shiga sitting room.

      Ta kula da yadda yake ta cin magani haka yasa ta shige d'aki abinta .

      "Kajimin mutum ya tashe ni a bacci da bugun 'kofa kuma yana cimin magani". Reyhana ta fad'a a  a hankali.

     Ita sam bata san ya dad'e yana bugu ba.

        Har ya gama cin abincin be nemi inda take ba illa shingid'a kan kujera da yayi.           " Instead ta bani ha'kuri shine zata shige d'aki aiko naga meyiwa wani magana".Ya fad'a a ransa.

        A haka har akai maghrib ya tafi masallaci be dawo ba har seda yayi isha'i tukun ya komo gida dama ya fita da key d'insa.

       Sanda ya shiga cikin d'aki yaga bata ciki ,waje ya samu ya zauna.

      Reyhana lokacin tana sitting room cin abinci,taji shigowarsa sarai amma ta share dan haryanzu bata huce ba gashi dama ba wuyar yanzu tayi fushi abinka masu ciki.

      Around 9:30pm Reyhana ta fito daga sitting room, koda ta shiga d'akin.                Yana kwance a kan gadon kuma bawai bacci yake ba.Ita kuwa toilet ta fad'a ta shiga ta watsa ruwa sannan ta zira sleeping dress nata ta hawo gadon.

      Duk abinda take yan kallonta,itama tana jin idonsa a kanta amma tayi burus kamar bata gani ba ,juya masa baya tayi tai kwanciyarta bayan tayi addu'ointa.

      Hakan ba 'karamin sake sashi tunzura yayi ba ,shima kwanciyar yayi ya juya baya.Kowa a cikin zuciyarsa da abinda yake tunani.

               *** Washegari da asubah bayan tayi sallah yunwa ta hanata komawa ,seda ta zubawa cikinta tukun ta komo d'akin.

     "Ina kwana". Ta gaisheshi.

      " Lafiya".Ya amsa ciki-ciki.

       "Wai yaya laifi nayi koh meh?" Reyhana ta tambaya dan yadda ya amsa mata yasa taji hasushi tund ita ba haka ta gaidashi ba.

        "Bakisan mey kikai ba kenan?" Ahmad ya fad'a.

          "Kamarya ? Nifa kayiwa laifin ma,gafa yadda ka tasheni ina bacci jikina yana kyarma na bud'e amma kayi biris kamar bakasan ina gunba". Cewar Reyhana.

       " Lalle kuwa nida kika ajje a waje na shafe kusan rabin awa baki ko damu ba illa damuwa da bacci kawai".

       "Amma de ai kasani kullum da key naka kake fita, kuma ai da idona biyu bazan'ki bud'ewa ba". Reyhana ta fad'a.

     "Au haka ma zaki ce ?"             "Toh Allah ya huci zuciyarka". Reyhana ta fad'a.

       Shi hakan ma sake 'kona masa rai yayi ,bece komai ba sakamakon kiransa da akai a waya.Koda yai picking yaji daga wurin aiki ne ogansu yana nemansa,dan haka ya mi'ke da sauri yayi wanka ya fito.

       Reyhana tana kallo ya sanya kayansa be ce mata ko 'kala ba.

      " Na tafi". Abinda yace mata kenan sanda ya zira takalmi.

      Shiru tayi har ya fice tabi bayansa da kallo.Ba abinda ta tsana irin taga ya fita beyi breakfast ba.

       Reyhana agogon d'akin ta kalla taga 7:17am ,mi'kewa tayi kan gadon ta koma baccinta.

      Reyhana se wajen 10:34am ta farka, tashi tayi ta gyara gidan yayi tsaf se lokacin ta tuna da walima ta graduation d'in saudat 'kawarta data kammala university.

     Gashi bata da isassun kud'i hannunta,tunani tayi 'kila ma da biyu yayi hakan dan ya rama shiyasa yai ficewarsa.

      Koda rana data kira wayarsa beyi picking ba kusan 2missed call,daga baya ma jitayi wayar a kashe ba mamaki kashewa yayi.Abinda tayi tunani kenan a ranta.

       Tana zaune 3,4:30 har 5 lokacin ta gama fiddarai ranta yayi matu'kar 'baci.

        Dama ta had'a wani leman tsamiyarta ,saboda haka ta tashi ta d'auko a fridge yayi sanyi gwanin sh'awa sitting room ta kai ta ajje.

     Bayan data ajje ta shige toilet, ba jimawa sega shigowar Ahmad ganin da akwai light yayi saurin shiga sitting room dan saka charge a wayarsa,a garin hakane 'kafarsa ta shura center carpet d'in lemo ya kelaye 'kasa😱

       Reyhana dede lokacin take shigowa d'akin.

      "Ya salam!" Ya furta.

   Jug d'in ya d'aga gashi tuni carpet d'in ya kusan tsotse  lemon dan haka ya mi'ke zai d'akko mopper.              Nan fa ya lura da Reyhana dake tsaye a bakin 'kofa ko ba'a fad'a ba yasan ta hau sama(up up🔥).

      Lemanta dako sha bata yi ba tana azar'ba'bin tasha ko taji sanyi shine ya zubar mata duka goma da ashirin(😀bani nace ba Reyhana ta fad'a).

     Kan kice me hawaye tarr ya fara kwaranyowa dama tuntuni ya tsaya a ma'koshinta kawai dama ce bata samu ba yanzu kuwa tana da dalili.

     Da sauri ya 'karasa inda take ya fara lallashinta"Reyhana please am sorry bada sani na bane ban lura ba kinji".

    Ai kamar zigata yake, hannunsa ta tankwa'be ta juya zuwa d'aki.Kan gadon ta fad'a tayita rera kukanta.

     "Dan Allah kiyi shiru Reyhana please am sorry". Ahmad ya fad'a sanda ya zauna a gefenta.

       " Kana sani kayi kuma dama haushina kake ji tuntuni".Ta fad'a cikin kuka.

       "Meyasa zanji haushinki ,ki tashi komai ya wuce please bana son wannan kukan".

          " Ba haushina kake ba ka'ki d'aga kirana kasan zan fita yau".Cewar Reyhana.

           Shi se yanzu ma ya tuna da wata fita unguwa."Reyhana ai na manta sam, meyasa baki tunan ba? Kinsan bazanyi haka ina sane ba ko na 'kuntata maki".

    "Kuma wayata ba charge d'azu da kika kirani ,sanda naga missed call d'inki zanyi calling back wayar ta mutu please kiyi ha'kuri".               Shiru Reyhana tayi bata sake cewa komai ba amma ta tsagaita da kukan.

    " Azizaty".Ya kira sunanta.

     Reyhana bata amsa ba ,jin tayi shiru ya sake kira.

     "Azizaty".

     " Uhmm".Ta amsa a ciki.

     "Kin ha'kura yanzu?" Ya tambayeta.

     Kai ta kad'a ba tare da tace komai ba.

      "Toh kinci abinci ?"

  Nan ma kai ta kad'a,hannu yasa ya d'ago ta a hankali.Fuskarta tayi sha'be-sha'be da hawaye.

     Idanta ta sauke 'kasa ,hannunsa  yasa ya goge mata hawayen ya d'ago da ha'barta.

     "Please look at me". Ya fad'a.

       A hankali ta kallesa sannan ta sake sauke idanuwanta.

       " Am sorry kinji".Ya sake fad'a.

        A hankali ta kad'a kai alamar ta ha'kura.

      "Ok smile".Ya fad'a.

       D'an guntun murmushi ta saki ba tare da ta kallesa ba.

       " Maman Baby saura na baby baki masa murmishi ba ko bakisan tana kallonki ba duk abinda kike"?"

     Jin ya ambaci haka ta d'ago da sauri "Tana kallona kuma? Yana de kallo na".

       " Auu! Naki choice d'in kenan ? Nide itace ba shi ba".Ahmad ya fad'a.

      "Toh nikuma ba haka ba ". Cewar Reyhana.

     "Ok then we shall see ,nan bada dad'ewa ba". Ahmad ya fad'a tare da jawota jikinsa yana shafa bayanta.

          Nan take suka mance da fad'an kamar basu ne ba.

               ***     Mommy sautin muryarta ne yake tashi a part d'inta kana doso wajen zaka jiyo muryarta.

    Waya take da Anty Asma'u kuma hira duk bata wuce ta Reyhana ba.

      " Yanzu wayar tata ta siyar ta bashi kud'in kenan?" Cewar Anty Asma'u bayan da Mommy ta labarta mata komai.

    "Eyyi taga zata iya se tai tayi". Mommy ta fad'a.

     " Ni yarinyarnan ma gani nake ciki gareta ".Mommy ta fad'a.          " Ahaf ai na ayyana ,yanzu a wannan 'kuntacaccen gidan zata bari ta samu ciki".Cewar Anty Asma'u.          "Eyyi bata da tunani ai ,ni naga d'an 'beran da za'a haifa gafa yadda take d'ura abincin lami a cikinta ko kifi babu a abinci ya kike tunani yaro ze kasance". Mommy ta fad'a tana kumfar baki.

     " Hmm Allah de ya sawwa'ke ,amma fa baza ki barta ta haihu a gidanta ba" Anty Asma'u ta fad'a.

      "Ahh dama yaushe ai dolensa ta dawo gida idan ba so yake jininta ya 'kafe ba kuma". Cewar Mommy.

       Sageer tun shigowarsa yake jin d'aga muryar Mommy ,kan wata kujerar d'akin ya zauna zaman jira ta gama wayar.

        " Mommy ku baku da zance se maganar Reyhana koyaushe Reyhana kubarta mana"Sageer ya fad'a bayan data gama wayar.

      "Dalla rufen baki, kai haryau yarone baza ka gane mey muke nufi ba daga kai har Reyhana d'in". Mommy ta fad'a.

       " Kuka san gaba mey ze faru".Sageer ya fad'a.         "Koh? A hakan da certificate d'in diplomar zeyi arzi'ki?" Cewar Mommy.

       "ARZI'KI RABO de". Ya fad'a.

       " Kai kasani nide ina sa'kona dana aikeka idan bashi ya kawo ka ba ka iya bani space".Mommy ta fad'a.       "Gashi". Ya mi'ka mata kud'in daya ciro mata a ATM.

             Yana bata ya fita ya koma sashensa...

  AR²💖

     Please Read,comment and vote. Luv u all😘😘

Jasko💕  🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 0⃣9⃣

    Yau Reyhana tun 10:30am ta gama komai dan yau gida zata da wuri Ahmad dama yau alhamis  yana azimi shiyasa ko girkin rana batayi ba wajen 11:37am ta gama shiryawa.

      Sanda ta shiga gida Abba ze fita nan ya tsaya suka gaisa tukun ya fita.

       Tana shiga ciki inno ta gani tana goge-gige a parlour.            "Ina kwana inno".Reyhana ta gaidata.

       " Reyhana kece a gidan? Lafiya lau ".Ta amsa.

        " Su Mommy suna d'aki ne?" Ta tambaya dan taga bakowa a parlourn.

        "Eh Walida ce bata da lafiya suna d'akinta dan basu jima da dawowa daga aibiti ba". Inno ta fad'a.

       " Tohh! Allah ya sawwa'ke bara na hau saman".Reyhana ta fad'a.

      A kwance ta isketa a gado se fad'a ake da ita wajen shan magani.

       Tana ganin Reyhana ta fara 'ko'karin tashi zaune.

      "Yi zamanki keda bakida lafiya". Reyhana ta fad'a.

         " Mommy ina kwana".Reyhana ta gaisheta bayan ta zauna a wata kujera dake d'akin.

        "Lafiya ". Mommy ta amsa.

         " Ya jikinnata ?"Reyhana ta tambaya.

        "Da sau'ki,tashi tayi da zazza'bi seda aka kaita asibiti". Cewar Mommy.

       Su Ikram da Sageer ma suka gaisa da ita.

  Bassam kuwa yana makaranta." Walida kisha magani kinji koh bakya so ki warke?" Reyhana ta fad'a.

     Kai ta girgiza alamar "A'a".

      " Toh maza tashi kisha".Ta fad'a.         Da 'kyar aka samu tasha maganin sannan ta samu ta sake shan tea daga baya tayi bacci.Se lokacin ta barsu suka sarara dan Walida bade raki ba.

       Sageer ya wuce d'akinsa haka Ikram ma.Reyhana kuma d'akin Mommy.

       "Reyhana meyasa kike cutar rayuwarki?" Mommy ta fad'a .

        "Yanzu har takai ga kin fara sayar da abubuwanki ,wannan shine rayuwar da kika za'bawa kanki?" Cewar Mommy ranta a 'bace.

         "Mommy fa daman ta fara bani matsala wayar". Reyhana ta fad'a.

        " Bawani nan 'karya kike,nasan mijinki kika bawa kud'in".Mommy ta fad'a.

        Reyhana shiru tayi ta sunkuyar da kai dan ta rasa abin fad'a.

          "Ke bazaki ta'ba gane mey nake nufi ba ,ki duba kiga tun ba aje ko ina ba kun fara shiga cikin wannan halin ina ga kun fara yara,Ahmad sam ba tsaran aurenki bane baki dace dashi ba baze iya ciyar dake ba a haka kuma kike tunanin kuyi 'ya'ya dashi".

         Reyhana kwallar da take ma'kale take ta zubo kalaman Mommy suna tsorata ta.

      " Mommy umma ce fa bata da lafiya shine na siyar dan akaita asibiti".Reyhana ta fad'a murya na rawa.

        "Ummansa ce ba lafiya? Yanzu kinzamo kece mijin kenan". Cewar Mommy.

        " Reyhana ina tausaya maki amma ke gani kike kamar na matsawa rayuwarki ki".

       Sallamar Ikram ce tasa suka katse maganar da suke ,da sauri Reyhana ta goge hawayen idanuwanta.

        Mommy tashi tayi ta bassu suna ta hirarsu.Daga bisani suka shiga kitchen Ikram da Reyhana suka soya wainar flour dama gashi Walida tana so.

        Kasancewar Ahmad yana azumi yasa ta koma gida wajen 4pm saboda had'a masa abin shan ruwa.

         Mommy da hankalinta ya kasa kwanciya da al'amarin Reyhana yasa Abba yana dawowa ta zauna dashi ta zayyane masa komai.

       "Toh ke yanzu mey kike so nayi?" Abba ya tambaya.

       "Haba Abban Reyhana taya zaka fad'i haka kai da kanka ya kamata ka nemo abun yi". Mommy ta fad'a.

      " Nide na fad'a maki ba ruwana a cikin wannan zancen,ki bar yarinya kin'ki ke kullum complain tunda mike da ita bata ta'ba kawomin 'karar yarannan ba suna zaman lafiya kuma sena sa baki".Abba ya fad'a.

      "Aikuwa ni ina da abinyi tunda kai baza kace komai akai ba". Mommy ta fad'a.

      " Mey kike tunanin yi?" Abba ya tambaya yana jiran amsarta.

      "Ya sawwa'ke mata ,bazan bari ina kallo 'yata ta zauna a 'kuntatacciyar rayuwa ba". Mommy ta fad'a.

        " Ya sawwa'ke mata fa kika ce? Anya kuwa kina da tunani ?" Cewar Abba yana mamakin kalaman Mommy.

      "Toh wani abune? Ai gaskiya na fad'a baze iya ri'ke mana 'ya ba dan haka seya rabu da ita bamu gaji da ita ba".

      " Kinga kunnena baze iya d'aukan wannan abun ke iya fita ko kiyi shiru".Abba ya fad'a.

      Mommy bata sake cewa komai ba ta mi'ke tai ficewarta.Abba bayanta yabi da kallo kawai ya girgiza kai.                            ***            Akwai lokacin da Mommy ana wani suna koda aka fad'a wa Reyhana ba ta samu zuwa ba saboda kud'in transport kuma bawai ta fad'a wa Ahmad ba yace baida kud'i,kawai ta san baida isassun kud'i shiyasa batai masa maganar sunan bama.Mommy kuwa tasha haushi nanma haka bata gaji ba seda ta fad'a wa Abba ita a lalle seya d'au action akai.

      Tun Abba baya biye zancen har shima abun ya fara damunsa kuma bawai ya fara 'kin Ahmad bane kawai de 'yar tasa ya fara tausayawa amma kuma sam be nuna wa Mommy hakan ba balle Reyhana.

      Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa da dad'i ba dad'i, Reyhana cikinta ya cika wata 8,zama da 'kyar tashi da 'kyar.Yanzu ta dena cin d'ata, mitimis da albishir ta tusa a gaba.

        Mommy kuwa tana kan bakatta na dawowar Reyhana gida,ita kuwa Reyhana ko Ahmad ma batayi wa maganar ba ta san baida ra'ayin mace ta koma gida wanka.

         Reyhana tana d'aki tajiyo 'karar wayarta a sitting room, koda taje dubawa taga wanda ke kira taga Mommy ce.Se a karo na biyu ta d'aga kiran.

         "Ina yini Mommy". Reyhana ta gaisheta.

         " Lafiya lau,bakya kusa da wayar koh?"

         "Eh". Reyhana ta amsa.

          " Toh ya maganar komowarki ,ko har yanzu baki fad'a masa ba?" Mommy ta tambaya.

        "Eh amma yau zan fad'a masa". Reyhana ta amsa.

         " Toh kide fad'a masa dan ba ruwana kika haihu a gida dan kinsan ni bani da wacce zan kawo maki atoh".Mommy ta fad'a.

     "InshAllah zan fad'a masa". Ta amsa.

    Daga haka sukai sallama ,Reyhana tunanin yadda zata 'bullo masa da wannan maganar take.

            ***

Ahmad kuwa a gurin aiki Umma ta kirasa take fad'a masa ya biyo ta gidanta.

    Dama lokacin tashinsa yayi dan haka ya biya gidanta.

     Bayan sun gaisa take ce masa Mommy ta kirata d'azu.

      " Mommy ce ta kiraki?"

      "Ehyi ta fad'a min Reyhana gida zata koma". Umma ta fad'a.

      " Gida kuma?" Ya tambaya cikeda mamaki.

      "Ehyi a can zata haihu". Ta amsa sa.

       " Toh ai ni bata fad'a min ba".Cewar Ahmad ransa a d'an 'bace.

      "Toh gashi mahaifiyarta ta fad'a".

      " Nifa bana son komawa gidannan fa".Ahmad ya fad'a.

      "Toh ai na lokaci ne kuma bayan haihuwar fari ce". Umma ta fad'a.

       " Sekace da yanzu fa an dena wannan".

       "Toh sekayi ha'kuri da hakan".

       " Sede bayan ta haihu".Ya fad'a.

      "Toh meye banbancin du d'aya ne fa kwana nawane"

     Ahmad badan yaso ba ya ha'kura, ko abincin Umman ma be ciba.

      Reyhana a gida tana ta tunanin yadda zata fad'a ma, koda ya shigo gida bayan yaci abinci yayi maghrib suna zaune kawai tunani take.

     Ana cikin haka taji yace "Meyasa baki fad'a min ba?"

     "Mey?" Ta tambaya.

     "Zaki koma gida". Ya amsata.

     " Dama yau nake son fad'a maka".Ta fad'a.

     "Amma waya fad'a ma?" Ta tambaya a ranta tana Allah yasa ba Mommy bace.

     "Umma ce ta fad'a wa Mommy". Ya amsa ta.

      " Azizaty haka mukai dake?" Ya tambaya.

      "Yaya kaga idan na zauna a gida ba a da wacce zata kawon ta zauna shiyasa zan koma ". Ta fad'a.

       " Ni kad'ai kike so ki barni?" Ya fad'a kamar d'an yaro.

      "No am always with you forever and where ever you are". Ta fad'a tana murmushi.

     " Dad'in baki koh? " Ya fad'a.

     "No hakane ai". Reyhana ta fad'a.

     " Ok, but zanyi missing d'inku keda baby ".

      " Muma".Ta fad'a.

      "Yawwa an samo mana sunan?"

      "Eyi amma bazan fad'a ba that's surprise". Cewar Reyhana.

       " Ko d'an hint?"Ya tambaya.

       "Wayo when the time zan fad'a ma".

        " Ok we are waiting ".Ahmad ya fad'a yana dariya.

        " Yau ba tausa?"Ya tambaya.

        "Anjima". Ta amsa.

         " Ok Azizaty ".

                    ****        Seda Reyhana ta 'kara kusan 2weeks sannan ta koma gida ,kayan baby da Ahmad ya sayawa baby ta tafi dasu ,su towel ne haka da saitin sauran kayan wanka na baby.Mommy a hakan ma seda ta kushe kayan Reyhana sede kawai ta kawar da kanta.

      Yau kwananta uku da komowa Ahmad yazo sau biyu.Tunda ta dawo gida ba wani aiki take ba tana d'aki idan yara sunje makaranta inko suka dawo sesi zauna suyi ta hirarsu da yamma kuma Ikram ko Walida ta raka ta fita waje dan tattakawa.

          Mommy kuwa yanzu dad'i take ji Reyhananta a kusa da ita yanzu 'yarta zata ci me kyau(Mommy ta fad'a not me wooo!)

        8:12pm,suna zaune yaran harda Reyhana a parlour sun kunna TV suna kallon Bollywood".

      " Yaya ni a chanja channel d'innan akai MBC 3" Walida ta fad'a.         "Baza a chanja ba!". Ikram ta fad'a a tsawace.

      " Meyai zafi kiyi ha'kuri Ikram ki batta ta kalli cartoon ko d'aya ne".Reyhana ta fad'a.

       "Nikuma fa na katse nawa kallon?" Ikram ta fad'a ranta a 'bace.

     "Yaya ki rabu da walidannan idan baza ta kalla ba taje ta kwanta". Bassam ya fad'a dama shi kullum kishiyanta ne.

       "Dukanku ha'kura za'kwi dan yanzu zan kai wrestling". Sageer ya fad'a.

       " Chabb! Lalle kuwa ashe bame kalla".Ikram ta fad'a harda harara.

      "Ke! dawa kike?" Sageer ya fad'a yana 'ko'karin mi'kewa.

     "A'a Sageer kaifa yaya ne ka cigaba da chat d'inka de". Reyhana ta fad'a.

     " Mey yake faruwa neh?" Abba ya tambaya yana 'karasowa inda suke.

     "Abba sannu da zuwa". suka fad'a.

     " Abba rashin kunya ya Ikram takewa yaya Sageer ".Walida ta fad'a tana kallon idan Ikram taga ya zatai.

       " Abba 'karya take".Ikram ta fad'a.

     "Toh ya isa". Abba ya fad'a.

      Mommy dede lokacin itama se gata ta sakko.

      " Abban Reyhana ka dawo kenan".Cewar Mommy.

      "Shigowata kenan". Ya amsa.

        Abba d'aki ya nufa bayan 'yan mintina daya sakko suka nufi dinning dukansu domin cin abincin dare.Gwanin sha'awa full house ,sunayi suna hira har suka kammala ,daga nan kuma aka zo aka zauna a parlour shan ice cream ana hira.Sun zirfafa suna hira wayar Reyhana tayi ringing Allah yasa tana kusa da ita da bazata jiyo ba.Koda ta duba taga Dear❤ zame jiki tayi tabar musu parlourn ta haye sama amsa wayar habibinta.

      Mommy kuwa tana kallon sanda Reyhana ta tashi ,ta'be baki tayi ta cigaba  da hirarta.

AR²💖

      Hmm! Mommy mey kike nufi? 🙊         Please vote,comment and share,love u all😘

Jasko💕

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣0⃣  

   "Azizaty kin manta dani". Ahmad ya fad'a.

      " Ashe zan iya mantawa da kaina ,kana raina dear ".Reyhana ta fad'a cikin sanyayyar murya.

        " Toh ya kike ya babynmu?" Ahmad ya tambaya.

       "Lafiya but we miss you much".

      " Nima Azizaty tun d'azu ku nake tunani".Ahmad ya fad'a.

      "Kaci abinci?" Ta tambayeshi.

       "Na kasa ci Azizaty,ba dad'i".

       " Ayya! Ka daure kaci kaji".Reyhana ta fad'a.

        "Toh zanci amma ba yawa".

       " Yafi de ka'ki ci".

       Sun d'au tsawon lokaci suna waya kafin daga bisani suyi sallama sannan tayi kwanciyarta dama da wuri take baccinta.

        Washegari da asubah kiran Ahmad ne ya tasheta ,bayan sun gaisa ta tashi tayi sallah tayi azkar d'inta.

      Da safe kafin ya fita seda ya  sake kiranta a waya.

       Kamar koyaushe Reyhana ta shiga kitchen ta had'a tea tasha da cake dan yunwa take tashi da ita.

     Koda ta koma d'aki jin baccin ya'ki zuwa ta had'a ruwan wanka a kettle,'yan  minute kad'an ta shiga tayi wankanta ta zira doguwar riga dan kusan duka rigunanta basa shigarta sede tayi ta fama da dogayen rigunan.

      Jin zaman d'akin ya isheta ta fito parlour ta kunnaTV ta soma kallo.Se chan bayan wasu 'yan lokuta suka tashi Mommy ta sakko 'kasa inno kuma tana kitchen ta fara had'a musu abun breakfast.

       "Mommy ina kwana". Reyhana ta gaisheta.

      " Lafiya lao,ke kuma baki koma baccin bane ?" Mommy ta tambayeta.

      "Eh". Ta amsa.

      " Toh ki sha tea d'in?" Ta tamabaya.

      "Eh nasha". Ta amsa.

      " Yawwa ya jikin Walidan ? "Ta tambaya.

     " Walida taji sau'ki d'azu ta farka tasha tea sannan aka bata magani".Mommy ta amsa.

     "Bari na shiga kitchen na duba inno".Mommy ta fad'a.

     " Toh".Reyhana ta amsa ta cigaba da kallonta.

       Se around 9:30am suka hallara a dinning dukansu Ikram a haka ma bacci be isheta Reyhana ce ta tasota.

      "Yarinya kwanan zaki dena baccin safe". Reyhana ta fad'a dan nan bada dad'ewa ba zata fara zuwa university tunda ta samu admission.

     " Abinda nake fad'a mata kenan ai".Cewar Abba.

    "Gara ma yarinya ki soma 'koluwa kyaji yadda nake ji". Sageer ya fad'a.

     Dariya sukai ,ita kuwa harara ta watsa masa.

    " Toh kai ai dole kasha wuya tunda kake namiji ita ai mace koh".Mommy ta fad'a dan ta kare ta.

      "Atoh kuma dole a kaini school". Ikram ta fad'a tana masa gwalo.

     Shikuwa sageer baki ya ta'be ya cigaba da cin abinci,Walida kuwa ana d'aki ana bacci.

         ***

Da asr sega su Anty Asma'u da sauran sisters na Mommy ,Reyhana tana parlour tajiyo muryarsu kuma dama taji inno tana musu sannu da zuwa a waje.        Da sauri Reyhana ta bar parlourn wai kunya take ji kar su ganta.

      Aikam basu dad'e da shigowar ba suka tambayeta.

     " Ai tana jin muryarku ta ruga d'aki wai kunyar ku ganta take".Mommy ta fad'a.

     Reyhana da take d'aki ta kasa kunne ta jiyo Mommy ta fad'i haka ji tayi dama tuntuni ta fita kafin ta fallasa ta.

     Gabad'ayansu dariya suka sa, Anty ummi (autar su Mommy) tace "Aiko ki dena kika sani ko mu zami kar'bi haihuwar".

     Nan ma dariyar sukai mata ,Reyhana jitake kamar ta nuste.

     Seda ta gama 'bata lokaci ta shiga d'akin Walida da tun d'azu ta tashi amma bata sakko 'kasa ba.Lalla'bata tayi suka fito tare banda hijab d'inda ta zinbila tasa ta a gaba wai ta kare cikin.

       " Ina yini ta gaidasu".Tana daga gefe-gefe se wani raku'bewa take.

     "Lafiya lao". Suka amsa.

     " Maman boy ce ko maman girl?"Anty ummi ta fad'a.

     Shiru tayi bata ce komai ba,sede idan kai magana ta amsa da eh ko aa,daga baya ma sulalewa tayi ta koma d'aki.

       Wayarta ta d'auka ta kira Ahmad suka sha hirarsu ba jimawa sega kiran umma itama ta kira taji ya take.

       Seda za su tafi tukun ta koma sukai sallama,itama ba jimawa suka itada Ikram tattaki.

                ***

    Idan kuwa su Mommy duka zasi je unguwa ita kad'ai suke bari dukda de ma yanzu Mommy ta rage fita d'in saboda tsaro...

      Ahmad a week d'innan ma ya sake zuwa amma baya dad'ewa idan yazo dan yawanci bayan maghrib yake zuwa.

       A kwana a tashi Reyhana cikinta ya shiga 9month,Abba ya 'kara mata wasu siya-siyen akan na Ahmad haihuwa yanzu ake jira yau ko gobe.

       Ahmad daga wajen aiki gidan Umma ya wuce koda suka gaisa ya fita majalissarsu ,Sadiq(kusan shine babban abokinsa ,beyi aure ba) se tsokanarsa yake wai ya zama gauro.

       "Aiko 'karyarka ka kirani da gauro ko ba komai nasan ina da mata kaikuwa fa babu baka ma tunanin yin auren". Ahmad ya fad'a.

      " Zaka sha mamaki lokaci guda sede ka ganni nazo gidanka da matata".Sadiq ya fad'a.

       "Haka de kace dan banga alama ba".

      " Ka zuba ido kawai".Cewar Sadiq.

      Suna cikin hira sega kiran Reyhana, ganin haka Ahmad ya matsa daga gun.

       "Maman biyu". Ya kirata.

       " Niba maman biyu bace".Reyhana ta fad'a.

       "Au bakyaso?"

       "Chabb! Kana so nasha wuya kenan".Ta fad'a.

       " A'a ai kullum ina yi miki addu'a".

      "D'ayan de a yanzu is enough". Ta fad'a.            " Azizaty kidena tsoro fah,inshaAllah komai zezo da sau'ki".

        "Ameen". Ta amsa.

     Hira kad'an suka ta'ba sannan sukai sallama.

       Walida ta samu sau'ki har ta koma makaranta,Ikram ma satinta biyu da fara zuwa school amma har an fara rigima da Sageer wai shi tana makarar dashi a tafiya kenan,a dawowa kuwa wataran har tahowarsa yake ya barta sede ta hau d'an sahu.

       Yau wajen7:43am ita Ikram tana da lecture na safe shikuma bashida ,da'kyar seda Mommy ta taso shi ya fito ko wanka beba kayan jikinsa ma wandan kawai ya sauya rigar kuwa T shirt d'in jiyace.

      A cukule ya fito fuskarsa ba annuri ,Ikram kuwa tun-tuni ta gama shiryawa shi take jira,ada taso yi masa tsiwa amma ganin yanayin annurinsa tayi shiru.

     Bayansa tabi tana masa gwalo har seda suka shiga mota ta nutsu.

      Koda suka hau titi Sageer ya fara wani tu'kin wula'kanci ,motar kamar bata tafiya se horn ake musu kowace mota sede tayi overtaken. Ikram kamar ta rusa ihu.

     " Wai matsala ta samu ne motar?" Ta tambaya.

      "Bansaniba kuma yarinya zaki dakinsani". Ya fad'a tare da makirin murmushi.

      Kafin tayi magana taji ya zugi motar kamar wani mey gudun race.

        " Wayyo dan Allah ka bari rannan d'aya garemu".Ikram ta fad'a a rikice.

       Kamar ma zigashi tayi  haka ya sake fyallarsu kafin a shiga school fuskarta ta cika da hawaye.

       "Gobe ki sake taso ni, kuma ki fad'a wa Abba kiga". Ya fad'a lokacin da yayi parking a cikin school.

      Abinda ya guda shi ya faru,'yan click d'insu ya gani sun nufo inda yake,gashi Ikram bata fita ba dole suka taddashi.

      Yana zuge glass d'in suka fara." Wanka(sunan da ake kiransa dashi) yane da matsalane muka ganka haka".

     Se yanzu ya sake kallon rigarsa da yayi bacci da ita,haushi ya kamasa.Sageer akwai son gayu,haka yasa aka sa masa wanka.

       "Nayi dropping yarinyarnan ne se anjima zan shigo lecture". Ya fad'a.

       Fitowa tayi ta wuce ko kallan inda suke batai ba.

      " A haba kazo mu zagaya makarantar mana".D'aya daga cikinsu ya fad'a.

      "No se anjima". Ya fad'a .

     Ba yadda basi dashi ba ya tsaya amma ya'ki ,shikuwa baya so 'yan mata su ganshi a haka su raina sa.

           ***

   Wajajen 5:27pm Reyhana suka dawo daga waje ita da Walida.

       Koda suka dawo d'aki ta shige tayi zamanta dan bata jin normal cikinta se hautsinawa yake kad'an-kad'an tana jin suka.

      Shiru tayi bata tafiya wa Mommy ba har aka bayan sallar maghrib ,koda aka zubo abinci ma kad'an taci.

     Suna parlour dukansu banda ita da tana d'aki tsoro ya kamata kuma ta'ki fad'a wa Mommy, kuma ita Mommy tayi zatan ko waya take shiyasa bata nemeta ba.

      Ahmad kuwa around 6 ya koma gida koda jona phone d'insa a charge se ta 'ki hawa,da alama ko charging point ne.

        Hakannan ya fita masjid amma yana ta tunanin Reyhana dan yau tun safe basi sake waya ba wayarsa ta mutu.

      Reyhana kam har da Mommy ta shigo d'akinta data tambayeta lafiya bata sakko 'kasa ba tace ba komai.

      Mommy ganin haka tai wucewarta d'aki,kowa ya koma d'akinsa.10:24pm kuma tana trying number na Ahmad a kashe,abi gaba yake 'karayi ciwo se 'karuwa yake.

      Tun tana daurewa ganin yin hakan ba mafita bane ta d'auki wayarta ta kira Mommy.

      Seda ta kira kusan 3× Mommy ta farka ganin Reyhana yasa da sauri ta mi'ke.

     D'akinta ta shiga ta ganta se mur'kususu take.

       "Reyhana jikinne? "

         "Cikina washh! Mommy". Abinda take fad'a kenan.

       Agogon d'akin ta kalla taga 12:05am." Tun d'azu Reyhana na tambayeki kika ce ba komai, bari na fad'a wa Abbanki".Mommy ta fad'a tare da fita.

      Mommy ce ta taimaka mata suka sakko ,Abba ya fito da mota aka sata a ciki Mommy ta d'akko kayan da za'a bu'kata.

      Inno Mommy ta tasa tace ta lura da yaran ,su Ikram baccinsu ma suke.

        Suna isa nurses suka shiga da ita d'akin haihuwa koda suka dubata suka ce da saura,amma de zasu iya zama  a asibitin.

       Wayar Reyhana Mommy ta d'auka ta lalubo number na Ahmad. Koda ta kira aka she taji tsaki tayi,instead ta kira na umma ta'ki.

      "Ya kin kira Ahmad d'in?" Abba ya tambaya.

    "Gashi na kira switched off". Mommy ta fad'a ranta a 'bace.

        Reyhana tana ciki se mur'kususu." Ku kirawon Mommy ". Ta fad'a ma nurses d'in.

       " Hajiya kizo yarinyarki tana kiranki". D'ayan nurse ta fad'a wa Mommy.

      Mommy a tsorace ta shiga ciki dan tausayin 'yartata ya kamata.

      "Sannu kinji". Ta fad'a.

      Kai kawai take kad'awa bakinta ya bushe.

      Idan ta fara salati seta koma addu'a kafin ta gama seta kamo wata, Mommy ma addu'ar take taya tayi Abba ma yana daga waje yana yi.

       " Mommy kin sake kiransa?" Ta tambaya murya na rawa         "Na kira a kashe wayar". Ta amsata.

    Kai kawai ta kad'a tana tapping cinya dan azaba.

      " Wayyo Allah Mommy !" Ta kurma ihu har Abba seda ya jiyo.

       "Sannu Reyhana". Abinda Mommy take fad'a kenan.

         (Allah sarki mata😭)

      Daga baya nurses d'in suka fita guda d'aya ce ta tsaya akan Reyhana.

      An d'au  tsahon lokuta ana abu d'aya ,daga baya ya lafa tana maida numfashi hannunta ri'keda Mommy.

      Reyhana har gari ya waye tana na'kuda ta fita daga hayyacinta.

        Yanzu ihun ma ta bari se addu'oi iri-iri ,Mommy da'kyar ta iya barinta tayi sallah ta fito wajen Abba suka gaisa.

          Su Ikram da asubah Inno take fad'a musu,nan da nan jikinsu yayi sanyi ko baccin sun kasa komawa dama lecture d'aya take dashi aiko ta fasa zuwa.

      Koda suka kira Mommy take fad'a musu bata haihu ba.

     Mommy bata dad'e da ajje wayar ba Reyhana ta 'kwala mata kira,da sauri ta koma d'akin.

          Na'kuda ce ta dawo fiya da baya ,gam ta ri'ke Mommy suna haka nurse d'in suka shigo,Mommy jikinta sake sanyi yayi ganin yadda Reyhana tayi firkai firkai ,Mommy bata doguwar na'kuda shiyasa ta tsorata.

       Mommy fita tayi daga d'akin tabar nurses d'in akan Reyhana.

         Mommy ta kasa zama Abba ma yana tsaye."Addu'a kawai zami mata Mommyn Walida ". Abba ya fad'a.

         Lokaci guda suka jiyo ta kwalla 'kara daga bisani tayi shiru sega kukan baby daya biyo baya.

       " Kaji kamar kukan baby nake ji". Mommy ta fad'a tana sake kasa kunne.

      "Eyyi nima de.." Be 'kare ba nurse ta fito.

       "Hajiya congratulation ta haihu yarinyarki..."

     AR²💖         Please share ,comment and vote. Love u all😘

Jasko💕   

🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣1⃣

      *Dayawa suna cewa Ahmad abun yayi masa yawa. I want to remind you this is just the beginning,kude ku cigaba da gashi🔥*

   Mommy da Abba a tare suka furta"Alhamdulillah".

       Bayan an gyaggyara maman baby da babyn kanta su Mommy suka shiga.Su kansu nurses admiring kyan babyn suke, Reyhana kuwa kallonsu kawai take a zuciyarta tana godewa Allah.

     "Mey aka samu?" Mommy ta tambaya.

     "An haifi mace". Suka amsata.

     " Toh mashaAllah ,Reyhana sannu ko".Abba ya fad'a yana kallonta.

     D'an wahalallan murmushi ta saki ta maida kallonta wajen babyn.

     "Sannu koh". Mommy ma ta fad'a".

      Babyn tana hannun Abba Mommy tana daga gefe itama hannunta nakan towel d'in da aka nad'e 'yar.

         " MashaAllah".Mommy ta fad'a.

        Mommy  wayarta ta d'auka ta kira su Ikram take fad'a musu,murna suka shiga yi.

       Bayan ta katse kiran ta kuma kiran Ahmad amma shiru kake ji.Mommy kuwa a ranta tace bazata sake kira ba.

      "Kin sake kiran Ahmad d'in ne?" Abba ya tambaya.

      Kai kawai Mommy ta kad'a fuskarta ta nuna alamar rashin jin dad'i.

      Reyhana tana kallonsu kanta kawai ta kawar ita kanta Ahmad ya bata haushi.

      "Taya za'ai ace ta haihu uban yarinyar ma baya gun? Kuma why not be nemesu ba tun jiya gashi har yanzu" Ta fad'a a ranta.

      Anty Asma'u ma an sanar mata da sauran sisters.

             ***

Shikuwa Ahmad koda gari ya waye da wuri ya shirya ya fita wajen aiki,sunyi da ogansa yau zasu je kasuwa dan haka suka tafi.Amma Reyhana tana ransa dan so yake idan sun dawo ya biya gidan Umma yai waya da ita kafin a gyara wayarsa.

       Wajen 11:00am aka sallamesu daga asibiti,kafin su koma gida dama inno ta d'orawa mey jego ruwa.

       Suna isa Walida ce the first d'in kallon baby har wani rawar jiki take a d'ora mata ita a cinya.

       "Walida baza ki iya ri'keta ba". Abba ya fad'a.

       " A'a zan iya ".

       D'an d'osana mata ita akai kafin Ikram da Sageer su kar'beta suma.

      " Wow! Mommy kalli hancinta da lips d'inta".Ikram ta fad'a.

       "Dani take kama". Cewar Bassam.

      Daga Mommy har Abba seda suka dara,banda Reyhana da tunaninta baya gun ,rashin zuwan Ahmad shi ya tsaya mata a rai.

      " Tabb! Ka cuceta amma ka kalli kanka  ka kalli yarinya  kace kuna kama hhh kade duba(😀 nima nace..).

      Haka suka cigaba da kalleta suna yaba kyanta da farinta (Nide dana kalleta naga copy d'in Ahmad😛).

        Gashinta ma irin nasa ne,kamanninsa sun fito a fuskarta sosai.

         Ruwan wanka Inno ta kai mata toilet,harda hawaye ita wai yayi zafi banda Mommy ta sata a gaba ba da seta surka.

          A cikin atamfofinta ta samu doguwar riga mara nauyi tasa,tea mey kauri Mommy ta had'a mata tasha,se farfesun kaza da inno ta dafo mata taci kad'an.

          Kwanciyarta tayi dan bacci ne a idonta ,babynma bacci take dan haka aka rufo musu d'akin suka fito parlour.

         Ahmad basu suka dawo daga kasuwa ba se 1:20pm dan sunsha yawo a kasuwar shi kanshi ya 'kosa ya komo.Koda suka dawo wajen aikin nasu yana tunanin ko ogan nasu ze barshi ya tafi amma seya bar masa wajen shi ya tafi gida Ahmad kuma ya tsaya akan sauran yaran.Duk haushi ya isheshi ,gashi sam idea d'in ya ari waya be zo masa ba.

       Anty Asma'u wajen 4pm suka zo da sauran sisters, lokacin Reyhana ta tashi daga bacci babynma haka.           "Me jego da babynta mashaAllah Allah ya raya".Suka fad'a.

         Faten dankali Mommy tasa inno ta dafo mata da'kyar taci rabi hakan ma dan su Anty sunsa baki.

        Baby ta fara kukan yunwa gashi mama be zo ba.Reyhana dama ko gwada bata batayi ba ,se dabino ta tauna ta samata a baki ta lasa.

       Da'kyar tayi shiru ta koma bacci.

        Anty Asma'u dasu ka d'an ke'be take tanbayarta Ahmad." Kinsan kuwa besan ta haihu bama?" Cewar Mommy.

     "Kamarya? Baku kirashi bane?" Anty ta tambaya.

     "An kira kusan sau nawa amma a kashe ". Ta amsa.

     " Shine kuma be kira ba har yanzu".

      "Ai yanzu ta fara gani kinga abinda nake fad'a tun ba aje ko ina ba ya fara wula'kantata,ace tun jiya bazaka nemi matarka ba kaji yaya take ciki". Mommy ta fad'a.

     Kai kawai Anty ta kad'a" Aiko shima se an gwanya mashi rabi da d'an banza ai ze nemeta ko ba dad'e ko ba jima lokacin za'a nuna masa kuskuransa".

      "Abbanta ma ai bece komai ba yasan yaran be kyauta ba itama Reyhana haka zata fara gane me nake nufi". Mommy ta fad'a.

    Parlour suka koma suka cigaba da harkarsu,ita kuma Reyhana lokacin ta samu damar kiran friends nata.

      Ahmad se 6pm ya tashi daga gun aiki,gidan umma ya wuce direct kan ya 'karasa maghrib tayi.Suna gaisawa ya tafi masjid se bayan ya dawo ya d'auki wayarta yasa credit tukun yayi dialing numbern Reyhana.

       Number busy yaji, har kusan sau uku number busy.Reyhana lokacin tana waya da sauran family and friends tana sanar musu.

     " Meya sami wayar taka?" Umma ta tambaya.

     "Wajen charging tana ya samu matsala".Ya amsa.

     " Toh bakuyi waya dasu ba kenan?" Umma ta fad'a.

     "Tun jiya fa yau kuma aiki ya mini yawa shiyasa ban biyo nan d'in da wuri ba". Ya fad'a.

      " Yanzu bata d'aga wayar ba ne?"

      "A'a a busy". Ya amsa.

       " Sede ko anjima". Ta fad'a.

       "Eh". Ya amsa.

     Reyhana kuwa koda ta ajje wayar Inno ta kai mata ruwa toilet.Yanzu ma tana kwazazo wai ruwan zafi sukai ta drama a toilet.

       Mommy ta rigata fitowa daga toilet d'in tana kallo wayarta tana haske ana kira ,koda ta duba taga umma.

     Wani murmushin mugunta tayi ta d'auka wayar seda taga kiran ya katse tasa  a black list.

      Ya kirata ba adadi waya  busy har ya damu sosai.Hakannan ya ha'kura ya koma gida yana ta shawarar ko yaje gidan su se kuma ya fasa yace gobe.

         Reyhana tana expecting call nashi amma shiru taga gashi Mommy ta goge kiran umma saboda haka bata gani ba.

         Da daddare Abba ya sake shigowa ya dubasu ita da baby.

                  ***      Cikin dare baby bata barsu sunyi barci ba tayi ta kuka Reyhana kuwa ta'ki bata mama wai ba komai a ciki.

       Washegari da safe 'yar baby tayi ta bacci abinta jiya bata barsu ba, Reyhana tayi ba itama bacci tayi tayi.

     " Reyhana tashi zaki ga ruwan wanka".Mommy ta fad'a.

     Reyhana a cikin bacci taji muryar Mommy, da'kyar ta tashi.

      "Ance ki bata mama kin'ki ba dole ta hanaki barci ba ,bari kici abinci sekin bata dolenki so kike ki barta da yunwa ne".

      Reyhana tana yamitsa fuska ta tashi,yau ruwan yayi mata dad'i dukda kuwa da zafi.Bayan ta fito aka had'o mata breakfast taci.           Su Ikram lokacin suka shigo ,Walida dake d'aga murya Mommy ta sata yin shiru karta tashi baby.

      Ba'a jima ba ta farka Mommy ta had'a mata ruwan wanka.Walida tunda aka fara yiwa babyn wanka bata tashi ba har seda aka gama se data makara a school tayi tayi Mommy ta barta ta zauna wai yau ai friday amma Mommy ta'ki bari.

        Ikram ma suka tafi ita da Sageer, Abba ma ya fita aiki bayan ya shigo sun gaisa.

    Mommy da Reyhana suna ta drama akan seta bawa baby mama.

       "Mommy zafi fa". Reyhana ta fad'a.

        " Kowa da haka yayi raino ,zaki barta da yunwa ne".Mommy ta fad'a.

        Seda tai da gaske tukun ta bata tana ta 'yar 'kara.

       "Ba gashi tana sha ba zaki wa yarinya azaba".Mommy ta fad'a.

     Reyhana kuwa ta turo baki se hararar babyn take kamar tasan abinda ake(😂).

       Mommy se yanzu ta d'auka wayar Reyhana dake chaji da dabara tayi removing daga black list.

   Du wannan abun Reyhana bata lura ba hankalinta na kan baby.

     Ahmad koda ya tashi da sauri-sauri ya shirya ko breakfast beyi ba.Wajen daya kai wayarsa gyara ya tafi ya kar'bo,a take yayi dialing number na Reyhana.

        Mommy ta fita daga d'akin itako Reyhana ta kwantar da baby tana lalla'bata tayi bacci sega kiran Ahmad.

       Dama a vibration tasa ta ,koda ta duba taga Dear❤ wani sabon jin haushinsa ta sake yi.

       Seda ya kira sau uku tukun tayi picking.

       " Hello Azizaty meya faru da wayanki tun jiya bana samunki?" Ya fad'a.

        A zuciyarta tace"Rainin hankali a ina ya kira ni jiya?"

       "Tawa wayar ko taka da tun shekaranjiya bana samunka". Reyhana ta fad'a rai a 'bace.

      " Azizaty charging point ne ya samu matsala kuma aiki yayi min yawa shiyasa kika jini shiru".Ya fad'a.

        "Aiki?" Ta fad'a cikeda rainin wayo.

        "Au baki yarda ba?" Ahmad ya fad'a.

         Yana so ya sake wata maganar ya jiyo kukan baby. Hakan yasa ya tsaya da maganar da zeyi.

      "Reyhana don't tell me kin haihu bansani ba". Ya fad'a cikeda mamaki.

      " Uhmm".Ta fad'a a ciki-ciki...

AR²💖

Please share

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣2⃣

     Ahmad jin amsar ta yasa ya kasa sake cewa komai ,shiru dukansu sukai credit na tafiya.

       Mommy data ke tsaye a jikin 'kofar d'akin 'karasowa tayi kusa da Reyhanan.Wayar ta kar'ba daga hannun Reyhana ma'kale a kunnenta.

       "Ahmad yanzu abinda kayi ka kyauta kenan? Reyhana ta cancanci kayi mata haka?" Mommy ta fad'a.

       Ahmad jin muryar Mommy kamar daga sama yasa ya gyara tsaiwarsa da yana jingine a garu amma jin muryarta yasa ya mi'ke tsam.

       "Eyyi? Activities naka sunfi lafiyarta,ace tun shekaran jiya rabon da kayi waya da ita rashin damuwa da ita ne komey?" Mommy ta d'ora akai.                  "Mommy wlh wayata ce ta samu matsala se d'azu na kar'bo daga gyara jiya na kira a wayar umma bana samun ta". Ahmad ya fad'a.

      " Mommy dan Allah kiyi ha'kuri".Ahmad ya fad'a.                 "Kiyi ha'kuri". Ya sake bata ha'kuri.

      Mommy bata sake cewa komai ba wayar ta katse sakamakon credit daya 'kare.

      " Matalauci". Mommy ta fad'a.

         Reyhana taji abinda Mommy tace amma tayi kamar ba sauraro take ba.

     Ahmad kuwa ba tare da ya 'bata lokaci ba ya taho izuwa gidansu Reyhana.

     Seda yayi kusan 5min ya iya shiga gidan dan nauyin had'a ido da Mommy yaji balle Abba.

         Yana shiga tun a harabar gidan ya had'u da Sageer.Bayan sun gaisa ya 'karasa dashi ciki.

     A parlour suka tarar ba kowo dan haka Sageer ya hau sama ya sanarwa da Mommy.

        Babyn na hannu Mommy lokacin Sageer ya isketa.

      "Mommy gafa ya Ahmad yazo". Sageer ya fad'a.

      "Shine yazo?" Cewar Mommy.

      "Eh yana parlour". Ya amsa.

        " Toh ungo ta kai masa ". Mommy ta fad'a tare da mi'ka masa babyn.

         Hannu yasa ya amsa sannan ya fice.

          Itade Reyhana ko " a" batace ba kuma bata tashi ba .

       A parlour Ahmad yana tsammanin ganin Mommy amma yaga Sageer tafe da baby,bawai be damu da yaga babyn ba amma a yanzu Reyhanansa yake son gani.

      A sanyaye ya kar'beta daga hannun Sageer daya mi'ko masa.

       Yana mi'ka masa ya fita daga parlourn dan school ze koma, Ahmad daga shi se baby a hannunsa.Ji yake kamar ba 'yarsa ba saboda mamaki.Daya kalli fuskarta da idanuwanta suke a rufe a ziciyarsa yana me godewa Allah.

       Sunan da za'a saka wa babyn ne ya fad'o masa dan,tuna Reyhana data ce zata fad'a masa sunan da take so a saka wa babynsu ya shiga yi.

      A zuciyarsa kuwa yana fad'in ina ma yana nan ta haihu.

      Addu'oi yayi ma babyn ya 'kura mata ido yana sake ganin kammaninsa a fuskarta.

      Sakkowar Mommy ce tasa yayi saurin d'ago da kansa.So yake ya sakko 'kasa daga kan kujerar amma kuma ga baby a hannunsa,hakannan ya 'kwantar da ita a kan kujerar daga gefe ya sakko 'kasa.

      "Ina kwana ". Ya gaisheta.

      " Lafiya". Ta amsa.

       "Mun samu 'karuwa kuma ,Allah ya raya ". Mommy ta fad'a.

       " Ameen".Ya amsa a hankali.

       Yana so ya tamabayeta jikin Reyhana amma ya kasa, Mommy ta gano hakan kuma dama haka  take so shiyasa bata cewa Reyhana ta sakko ba.

       "Kaci gidanku bazaka ganta ba"Mommy ta fad'a a zuciyarta.

       Inno tasa ta kawo masa abin sha har lokacin Reyhana bata fito ba Mommy kuma ta bar parlourn.

      Wayarsa ya d'auka yayi dialing numbern Reyhana yaji ba kud'i dan haka yayi rance ya kirata.

      Tana jin wayarta tana ringing tasan shine,ya kira kusan 3× amma bata d'aga ba.

      Please pick my call am sorry.

      Ya tura mata,tana karantawa taji tausayinsa ya kamata ta sani haka kawai baze kashe wayarsa ba dole sede da dalili.

     Tana cikin wannan tunaninne tajiyo kukan baby da alama ta tashi.Sosai take tsala ihu Mommy kuma tana d'akinta ta shiga toilet inno ma tana sashen d'akinta bata jiyo ba.

      Reyhana jin shiru Mommy bata shigo da baby ba yasa ta sauka dan ta kasa jure kukan da babynta take😜

    Wani sanyi Ahmad yaji a ransa ganin Reyhana kukan babyn ma be damesa ba.

     'Karfin hali tayi bata ce komai ba se tsayawa datai tana jira ya mi'ka mata.

       Mi'ka mata yayi idanuwansa yana kanta,ita kuwa bata bari sun had'a ido ba ta kar'ba.

      Ya kula da yanayin kumburin fuskarta da idanuwanta take yaji tausayinta.

     "Reyhana please kiyi ha'kuri kiyi min magana dan Allah". Ya fad'a a raunane.

     "Reyhana baki yarda da abinda na fad'a maki bane ? kinsan bazan barki ba ina sani koh please ki amsa min i am sorry".

        " Please ka barni yanzu de kaga kuka take".Ta fad'a.

       "Toh ki zauna mana anan ki..."

      Be 'kare ba sega wasu ba'kin suna shigowa parlourn,dan haka dole ya basu guri ya fita haraba ya zauna a kujera dake wajen.

      Umma ya kira yake fad'a mata tayi masa fad'a ,tace laifinsa ne.

     Reyhana zama tayi ta bata mama tasha tukun ta mi'ka musu.Mommy ta fito suka gaisa da ba'kin.              Ahmad kuwa yana waje har lokaci ya sake ja ,kiran wayarta ya sake yi again shiru kuma tana d'aki ta lura da kiran ta'ki picking.

         "Am very sorry please forgive me" Ya sake tura mata text.

       Tana karance text d'in ya sake kira seda ta kusa tsinkewa tayi picking.

     "Azizaty kina son kasheni ne?"

     "Mey kuma nayi?" Cewar Reyhana.

     "Baki sani bama? Please ki saurareni dan Allah kiyi ha'kuri". Ya fad'a.

      " Kin ha'kura?"Ya tamabaya.

       Shiru tayi bata ce komai ba.

       "Please badan ni ba". Ahmad ya fad'a.

       " Toh naji".Reyhana ta fad'a.

       "Thank you so much Azizaty ,toh ya jikinki?". Ya tamabaya.

       " Da sau'ki".Ta amsa.

       "Are you sure?"

       "Sure". Ta amsa.

       " Sannu my Azizaty nasan babynmu ta baki wahala".

       "Maman baby wane sunan aka sama mana?" Ya tambaya.

      "Uh...sunan Umma". Ta amsa.

      " Are you serious? "Ya tambaya yana me mamaki dan sam be kawo hakan ba.

     " Yes".Ta amsa.

      "Nagode sosai,zan kira Umma yanzu na fad'a mata".Ahmad ya fad'a.

      " Kaga ma tana kirana".Reyhana ta fad'a.

      "Ok toh bara na katse ki amsa i will call u back". Ya fad'a.

       Bayan tayi picking call na umma tayi mata barka sannan ta sake bata ha'kuri.

       Suna gama waya da umma Ahmad ya sake kira.

       " Azizaty ban gaji da ganinki ba fa keda baby ya za'ayi ne?"

        "Ga baki basu tafi ba".Ta fad'a.

        " Azizaty kinsan ya za'ai?"

        "A'a". Ta fad'a.

         " Anjima da maghrib zan dawo tare da umma ma zamu zo kinga lokacin Abba ma ya dawo koh?"

          "Eh". Ta amsa.

          " Toh yanzu de kiyi wa Mommy magana zan tafi se miyi sallama".Ahmad ya fad'a.

       "Toh". Ta amsa.

        Tana gama wayar ne ma sega Mommy ta shigo.

      " Mommy ga Ahmad ze tafi yace zakuyi sallama"Reyhana ta fad'a.

     "Uhm waya kukayi kenan". Mommy ta fad'a tare da ta'be baki.

      " Yaran yanzu baku da zuciya".Mommy ta fad'a.

      "Mommy kuka fa take shine naje kar'barta".Cewar Reyhana.

      "Rabu dani ". Mommy ta fad'a.

      Daga haka ta fita sukai sallama dashi.Wajen aiki ya wuce se wajen 4pm ya tashi kafin yaje gidan umma ya tsaya a store yayi wa Reyhana 'yan siyayyan mey jego dede halin sa.

               ***    Around 6:40pm suka je gidan su Reyhana,har da'ki Mommy tayi mata iso shima Ahmad d'in tare da ita ya shigo.

        Bayan sun gaggaisa Mommy ta fita ,Reyhana ce ta rage a d'akin sesu Umma.

       "Umma Reyhana ta miki ta'kwara fah". Ahmad ya fad'a.

      " Toh!  mashaAllah an gode Allah, Allah ya raya mana AISHA".           "Ameen ". Suka amsa.

      Suna zaune Abba ya dawo shima ya shigo suka gaisa dasu,lokacin da zasu tafi ya ajje kayan da ya siyo.

        A waje Ahmad ya ke'be da Abba ya bashi ha'kuri akan abinda ya faru Abba yace komai ya wuce.

        Mommy bayan sun tafi da ta shigo taga kayan kawai ta'be baki tayi bata ce komai ba.

        Se lokacin Reyhana ta samu tayi wanka akaiwa baby ma ,nan su Ikram sukai ta rangad'a mata pic iri-iri.

          Kusan kullum Ahmad seya zo ya dubasu idan ya tashi daga aiki,a haka kwanaki suka ja har ranar suna tazo.

        Anyi shirye-shirye sosai komai Mommy sun tanada Ahmad ya aiko da ragon suna aka yanka yarinya taci suna AISHA Mommy taji ba dad'i sede bata nuna ba.

      Nasreen za'a ke kiranta dashi,tasha ado daga ita har mey jego Reyhana  swiss lace purple me white torches tasa se necklace silver Ikram ta rangad'a mata d'auri sekace amarya.

      Ansha hotuna 'yan uwa da abokan arz'iki sun hallara,Ahmad da yamma shida abokansa uku suka zo se Umma da wasu sisters daga zaria.

       Reyhana dama ta tanadar musu abinci da sauran lemuna ta ajje dan haka da suka zo ta basu,sukai hotuna suma.

       Bayan an watse daga Nasreen har Reyhana sun gaji sosai ana wa Nasreen wanka tayi bacci Reyhana ma wannan tayi tasha tea ta kwanta.

       *Nima pen d'ina na ajje na kwanta😀*

AR²💖

    Please share...

Jasko💕         

     🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣3⃣

  Washegari gajiyar da dama-dama sede Nasreen tasha bacci dan har lokacin bata farka ba.

      Har tayi wanka tayi breakfast Nasreen bata tashi ba,koda ta duba wayarta taga missed call na Ahmad ya kira tana bacci dan haka tayi calling ba.

      Kira d'aya tayi masa yayi picking.

       "Ummu Nasreen". Ahmad ya kira.

       "Abu Nasreen". Reyhana ta fad'a itama.

       " Ina kwana ".Ta gaisheshi.

       " Lafiya lao Azizaty,ya gajiyarku?"Ahmad ya amsa.

      "Gajiya ansha ta,har yanzu bacci take". Ta fad'a.

      "Allah sarki babyna du mutane sun wahalar min da ita".Ahmad ya fad'a.

      " Sannu mey baby".Reyhana ta fad'a cikin zolaya.

      "Ha! Toh ai gaskiya na fad'a". Cewar Ahmad yana dariya.

      " Toh nikuma fa banfita gajiya ba?" Reyhana ta fad'a.

     "Iyye! Kishi" Ahmad ya fad'a.

      "Haba kinsan da ina kusa da nayi maki tausa".Ahmad ya fad'a.

      " Nayi missing Azizaty ta ,your cooking pretty face everything yours Ummu Nasreen ".

      " Me too".Reyhana ta fad'a.

      "Toh yanzu kayi breakfast?" Ta tambaya.

      "Tea kawai nasha,yanzu zan fita ma". Ahmad ya fad'a.

      " Please ka samu kaci wani abun ko a wajen aikin ne".Cewar Reyhana tana mey nuna damuwa.

      "Ok Azizaty i will". Ya fad'a.

      " Toh bari na barka ka shirya".Ta fad'a.

      "Ok ki shafamin kan babyna i love you all". Ya fad'a.

     " Love you too,Allah ya kare mana kai".

     "Ameen". Ya amsa.

     Daga haka sukai sallama kowannensu fuskarsa d'auke da murmushi cikin ransu suna 'kara jin son junansu".

      Ba jimawa Nasreen ta tashi ,da kuka ta farka dan yunwa da take ji.Ta ded'e tana shan nono tukun aka yi mata wanka.

        Komai ya cigaba da gudana, Nasreen har bayan suna ana zuwa barka ga kayan gudumawa da ake bawa Reyhana yarinyar tayi goshi sosai banda kayan da Abba ya 'karo mata akan wanda su Umma suka kawo na barka.

        Ikram idan suna gida itace me d'aukan Nasreen Reyhana hutawarta take ,yarinyar ana ji da ita a gidannan Ahmad ma yana yawan zuwa baya kwana uku beje ba.

        Umma ma tana yawan kiransu su gaisa taji ya ta'kwararta.

      3weeks later,Ahmad yana ta irga musu kwanakinsu bashida buri su cika kwana 40 su dawo baya jin dad'in gidan kusan koyaushe yana unguwarsu wajen abokansa.

                  ***       Mommy yau tai shirinta na zuwa gidan Anty Asma'u dan tunda Reyhana ta haihu bata samu ta fita ba.

         " Mommy dan Allah ku dawo da wuri saboda wankan Nasreen".Reyhana ta fad'a.

      "Yau ke zaki mata da kanki ai gara ki koya". Mommy ta fad'a.

       " Cabb! Kina so nasa mata sabulu a hanci". Reyhana ta fad'a.

      "Gaki gata kika samata kyasan yadda kikai". Mommy ta fad'a.

      Walida da tun tuni ta gama shiryawa Mommy take jira kawai su tafi.

        " lala Yaya baby Nasreen tayi pupu".Walida ta fad'a tana toshe hanci.

       "Ga babarta ta wanke mata danni na gama nawa". Mommy ta fad'a.

       " Kai Mommy nifa ban iya ba".Reyhana ta fad'a.

      "Zaki iya ne, ga inno can kice ta cire mata danni nayi nan,Walida taho mi tafi". Mommy ta fad'a tana sa'kala Jakarta.

      " Se kun dawo".Ta fad'a.

       "Muhmm! Me d'oyin kashi". Reyhana ta fad'a lokacinda  Nasreen ta kalleta.

       Haka nan ta tashi ta cire mata tana yi tana toshe hanci.

                  ***

      Mommy a d'an 'kan'kanin lokaci ta isa gidan Anty Asma'un.

        Suna parlour ita da yaranta." Oyoyo Walida".Anty ta fad'a tare da nufo inda suke.

       Walida tana gaisheta ta nufi inda Ameera take,kusan itace sa'arta sukuwa Mommy suka tafi d'aki.

        "Ya masu jego ?"Anty ta tambaya.

        " Mey jego tana nan qalau ita da baby".Mommy ta amsa.

        "Saura 'yan satittika su koma koh?" Cewar Anty.

        "Hmm!" Mommy ta furta .

         "Ya hmm! da wani abune?" Anty ta tambaya tana neman 'karin bayani.

        "Kusan de". Cewar Mommy.

        " Mey fah?" Anty ta tambaya.

        "Nifa ba maganar komawa da yarinyar nan zatai". Mommy ta fad'a.

        " Toh! dalili?" Ta tambaya.

         "Nifa bazan yarda da irin wannan rayuwar ba ta gidan Ahmad Reyhana ba class d'insa bace ki duba kiga nauyi ya 'karu a kansa idan da yana kula da mace d'aya toh yanzu ga nauyin babynnan abin is not easy". Mommy ta fad'a.

       " Amma fa kin matsa dayawa kina tunanin Abbanta ze bar faruwar hakan?"Cewar Anty Asma'u.

       "Barni dashi nasan ta inda zan 'bullo masa". Mommy ta fad'a.

       "Su kuma ya zaki dasu?" Anty ta tambaya.

        "Wannan bame wuya bane Reyhana ba kamar Ikram take ba,taimakon rayuwarta zanyi ita bata san kanta ba ita so ya rufe mata ido bazan zuba ido ta sake samun cikin na biyu ba gara tun wuri na dakatar dama rabon 'yace ya had'asu".Mommy ta fad'a.

      "Maryam kenan ,toh Allah ya saww'ake deh". Anty ta fad'a.

       " Yanzu Toh yaushe zaki fad'a ma Reyhana d'in?" Ta tambaya.

     "Nan bada jimawa ba". Mommy ta fad'a.

       Daga nan suka tsindima wata hirar ta daban.

        Reyhana kuwa a gida tana ta fama da Nasreen dan ta'ki komawa bacci gashi ta barta a d'aki ita d'ai tasa ihu Ikram bata dawo ba balle ta taya ta ,inno kuma ta fita.

        Ahmad daga wajen aiki ya tashi da wuri,wajen 4pm yazo gidansu Reyhana. Har lokacin Mommy bata dawo ba ,kiranta yayi a waya ya fad'a mata yana haraba tace ya shigo.

       A parlour ya zauna chan ba dad'ewa ta fito Nasreen a hannunta.

       Murmushi ya sakar mata me 'kayatarwa itama ta mayar masa,be jira ta zauna ba ya mi'ke domin kar'bar Nasreen.

            " Ummu Nasreen irin wannan kyau haka".Ahmad ya fad'a.

       Kuma powder ne da lipstick kawai ko kwalli bata sa ba,tayi kyau sosai cikin green d'in atamfar.

       "Babyna ta gane ni kinga tana mini murmushi". Ahmad ya fad'a yana 'ko'karin zama.

      Itama Reyhana zama tayi a kujerar dayake three seater ce.

       " Watoh har ta fara gane ka?"Cewar Reyhana.

      "Ehmana baki gani ba taga mey kama da ita". Ya fad'a.

      " Sonkai koh".Ta fad'a.

      "Mommy bata nan?" Ya tamabaya.

      "Ta fita d'azu". Ta amsa.

      " Yau ke aka bari da babyn tamu,karfa kice zaki mata wanka karki sa mata ruwa a hanci".Ahmad ya fad'a.

      "Aiko na iya". Reyhana ta fad'a.

      " No sekun dawo zaki dinga yi mata".Ya fad'a.

      "Kin fara had'a muku kayan ku de koh?"

      "Wane kaya ana zaune lau,sekace gobe zamu komo". Reyhana ta fad'a.

     " Lalle just kwanaki ne fah,gara ma ki fara shiri dan kun kusa komo wa keda baby Nasreen ".

       Tashi tayi ta tafi kitchen ta had'o masa abunsha da snacks ta kawo masa.Hira sosai sukai tayi har Ikram ta dawo Nasreen tayi bacci ta kaita d'aki,se kusan maghrib ya tafi har lokacin Mommy bata dawo ba.

      Se to 8pm tukun ,ba dad'ewa Abba ya dawo.Mommy se lokacin akai wa Nasreen wanka,Reyhana kuwa bayan tafiyar Ahmad.

        Mommy maganar tana cinta amma ta kasa fad'a wa Abba,a kwana a tashi Reyhana sunyi kwana 37 Mommy bata yi wa Reyhana maganar komawa ba.

     Shikuwa Ahmad kullum cikin lissafi dan yanzu a tunaninsa baza suyi 5days basu dawo ba,dan har siyayyar 'yan kayan stuffs yayi musu jiran dawowarsu kawai yake.

     Mommy yau de ta d'au alwashin fad'a wa Abba duk abinda ke ranta,around 8:32pm bayan sun gama dinner ta shiga d'akinsa lokacin yana 'yan danne-danne a phone d'insa.

       " Abban Reyhana ina so zami magana ne".Mommy ta fad'a tana tsaye.

     "Toh shigo ina jinki". Ya fad'a tare da ajje wayar gefe.

    Mommy waje ta samu ta zauna a kan gadon tana tunanin ta inda zata fara.

        " Dama akan Reyhana ne,ina nufin komawarta".Mommy ta fad'a.

       "Toh ina sauraro". Ya fad'a yana 'kara tattaro hankalinsa gareta.

      " A gaskiya nifa bazan yadda yarinyar nan ta koma gidanta ba".Mommy ta fad'a.

       Kuma yadda take maganar zaka gane da gaske take.Abba zama ya gyara yana kallon ikon Allah.

       "Toh bazata koma ba a gidanki zata cigaba da zaman auren kokuwa mey kike nufi?" Abba ya tambaya.

      "Ina nufin Ahmad ya sawwa'ke mata". Ta amsa ba tare da ta nuna alamar damuwa ba.

      " What!" Abba yayi exclaiming cikeda nuna damuwa.

     AR²💖

     *Oh! ni Dijensy mey yake shirin faruwa neh??*

     *Readers your comment is what will keep this story survive remember your vote,comment are needed.Love you all, sis feezoh😘*

Jasko💕

     

     

      

     

             *ARZI'KI RABO*

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣4⃣

   Sis feezoh tnx for ur concern, Allah ya bar zumunci we are always together😘

  Mommy da ganin yanayin reaction na Abba yasa ta sake zage dantse.

      "Eh sakinta zeyi".Ta fad'a babu alamar damuwa tare da ita.         " Kina da hankali kuwa Maryam? Ina tunaninki? Ina iliminkii ? Kina abu kamar wata 'karamar yarinya wannan ai shirmene!"Abba ya 'kare maganar  cikin d'aga murya dan ransa ya 'baci.

      "Ba zancen rashin hankali,nide da raina bazan bari 'yata tashiga wani hali na rayuwa ba,wannan yaran baze iya ciyar da Reyhana ba balle bata sittira kana gani wani nauyin ya sake hawa kansa".

       " Maryam arz'ikinnan kece mey bayarwa neh? Kada ki manta bada arzi'kina kika aureni ba".Abba ya fad'a.

      "Da daban yanzu daban,shikenan kafiso kadinga ciyar da ita tana gidan auren nata ? Haka ake rayuwa?"

       "Maryam bana son sakarci fah,ke yanzu  ba abun kunya bane a gareki ace d'iyarki daga zuwa wanka gida aure ya mutu yaran da koh shekara biyu da aure basi ba".Cewar Abba.

      " Du kai ka janyo mah yarinyarnan ta aureshi tun farko seda nace maka kada ayi ka'ki jina, yanzu kaga irin halin 'yarka data shiga kuma wai a haka kake so ta cigaba da rayuwa,kafiso sede kullum ka dinga yafita mata kud'i tana cida kanta da mijin koh? "

     "Maryam ke meyasa bakya jin magana neh a rayuwarki?" Abba y fad'a tare da mi'kewa tsaye.

    Itama Mommy tashi tayi daga zaunen."Kasan Allah bazan ziba ido Reyhana ta shiga cikin rayuwar 'kunci ba ,yarinyar da bata taso a wahala ba kawai rana d'aya ta shiga 'kuncin rayuwar da bata san ranar barinta ba".Mommy ta fad'a.

      "Baza a raba masu aure ba na fad'a maki ,wannan haukar baza ayi dani ba". Abba ya fad'a.

      " Shikenan idan kai bazaka d'au mataki ba ni zan d'auka".Mommy ta fad'a.

     Ba tare da ta jira Abba ya sake magana ba ta fita daga d'akin fuuuu.Yana kiranta amma tayi banza dashi ta koma d'akinta.

       Daga yara har Reyhana ba wanda yasan meyake faruwa sede sunji ba Mommy a parlor ba Abba dan ko alamar su babu ,dukansu kowa d'akinsa ya koma Reyhana itama haka.

     Tunanin komawarta gidanta ta shiga yi ,sede kuma abin da yake bata mamaki shine haryanzu Mommy bata yi mata maganar hakan ba.

    Tana cikin wannan batunne kiran Ahmad ya shigo.

     "Ummu Nasreen". Ya kira sunanta.

      Bayan sun gaisa yake tamabayarta ya batin dawowarsu.

       " Azizaty ana ta shiri?"Ya tamabaya.

       "Uhmm".Ta amsa.

       " Kin jiki ,gara ma ki bud'e baki ki magana kin shagwa'be da zaman gida koh toh aiko ki shirya ina nan ina jiranku".Ahmad ya fad'a.

       "Se mun 'kara sati biyu".Ta fad'a cikin zolaya.

       " No shekara".Yayi gatse.

      Haka suka sha hirarsu lokaci har yaja ta fara jin bacci dan haka sukai sallama ta kwanta.

             ***      Washegari da safe koda Reyhana ta tashi taga Mommy bata ma shigo ba,Nasreen  ta lura taga itama ta tashi dan haka ta d'auketa.

       Tana bata mama sega Walida ta shigo d'akin dama  yau Saturday.

       "Mommyn Nasreen ina kwana". Walida ta gaisheta.

       " Au yau kuma sunan da aka samun kenan".Reyhana ta fad'a bayan ta amsa.

       "Mommy bata fito ba?" Reyhana ta tamabaya.

       "Eh nima ban ganta ba". Ta amsa tare da zama kusa da Reyhana tana shafa gashin Nasreen.

          Abba around 8:30am ya sakko 'kasa, Walida ya tarar da Ikram a 'kasa yake tambayarsu Mommy suka ce bata sakko ba.

       Abba kai kawai ya kad'a ya koma sama dan yasan dalilinta na 'kin fitowa.Koda yaje a bakin d'akinta ya tsaya yana knocking tare da kiran sunanta amma tayi burus.

        " Maryam ki fito na fad'a maki".

        "Na fito na muku mey?" Mommy ta fad'a.

          "A'a kamarya ? Da haka kike yi ga yara nan suna jiranki a 'kasa,ki fito kiyi breakfast".Abba ya fad'a cikin sanyin murya.

       Haka ya rabi da ita ya sakko daga shi se yaran sukai breakfast ,Reyhana ma se daga baya tayi nata breakfast d'in.

       Abin ya fara damun yaran dan Mommy bata saba haka ba.Suna cikin  wannan batun ta sakko.           " Mommy ina kwana ".A tare suka gaidata.

      Sun lura mood d'in Mommy hakan yasa suka d'an yi shiru.

       " Lafiya".Ta amsa muryarta a ciki-ciki.

        Kitchen ta nufa ba tare da ta sake cewa komai ba.

       Abba kuwa yana d'akinsa,Reyhana tana d'aki itama basu jima da yin waya da Ahmad ba.

       Mommy a kitchen tayi breakfast d'inta ta shiga d'akin Reyhana.

        "Mommy ina kwana". Ta gaidata              " Lafiya".Ta amsa.

        "Reyhana".Mommy ta kira sunanta cikin wata murya lokacinda ta zauna.

         "Na'am". Reyhana ta amsa gwiwarta ba 'kwari.

           "Kinsan ni mahaifiyarki ce kuma bazan yi wani abu dan cutar dake ba koh?" Mommy ta tambayeta.

         Kai kawai Reyhana ta kad'a alamar "eh" ba tare da tace komai ba.

          "A gaskiya ni ban amince da komawarki gidan Ahmad ba,bazan amince ki cigaba da zama a irin wannan rayuwar ba". Mommy ta fad'a.

          Wani irin fad'uwar gaba taji ,a take zuciyarta saurin bugunta ya 'karu.

        "Reyhana a kullum ina fad'a maki ke ba tsarar Ahmad ba ce,ki duba kiga aikin dayake baze iya ri'keku ba kuma yanzu nauyi ya 'karu idan yau Abbanki ya baki kud'i gobe wa ze baki idan matsala ta faru? Wannan abubuwan nake guje maki shiyasa tun farko na'ki amincewa da aurenki dashi,dan haka tun ba'ai nisa ba gara a yanke ala'kar aurenku ,gatanan dama Allah yayi itace rabon auren". Mommy ta fad'a tare da kallon Nasreen.

        Reyhana jinta take kamar wata kurma ,kwalla ta cika taf a idanuwanta a take ma'koshinta ya bushe.

            " Mommy? " Reyhana ta fad'a lokaci guda kuma hawaye ya gangaro a idanuwanta.

          "Reyhana nasan hakan baze zo maki da sau'ki ba amma ki sani dan farincikinki nake komeh da kika gani".

      Bata sake wata maganar ba Abba ya shigo d'akin dan already ya jiyo su da Mommy.

        Mommy tana ganin ya shigo ta tashi ta bar d'akin ,hakan yasa Reyhana ta gano sun sami sa'bani da Abba kuma tasan baze wuce akan maganar aurenta ba.

        " Ta fad'a maki koh?" Abba ya tambaya.

       Kuka Reyhana ta fashe dan bata da wani sauran dauriya a tare da ita.Bece sake cewa  komai ba yabi bayan Mommy.

        Ita kuwa Reyhana gefe guda ta ajje Nasreen ta shiga rera kuka,a lokacin kuma taji wayarta na ringing koda ta duba taga Dear❤

       Seda ta katse ya sake kira tukun ta iya  picking, d'an share hawayen tayi tare da sassaita muryarta tai magana.Duk da haka seda yaji yanayin muryar tata ya tamabayeta.

        "My Amarya meya faru?"

AR²💖

Please share..

Jasko💕

                     🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣5⃣

       "Yaya ba komai ,kawai de kaina ke ciwo". Tayi 'karya.

       " Toh! Allah ya sawwa'ke kin sha paracetamol? " Ya tamabaya.

       "A'a amma zansha". Ta fad'a.

       " Toh ki samu ki sha,ya Nasreen?"

        "Tayi bacci". Ta amsa.

         " Toh ki shafan min kanta".Ahmad ya fad'a.

          "Kema ki samu ki baccin  kan ze dena,nima yanzu zan fita".

            "Ok,toh seka dawo". Ta fad'a.

        Daga haka sukai sallama ta ajje wayar wani sabon hawaye ya sake gangarowa a fuskarta.

       Mommy kuwa kafin Abba ya 'karasa d'akinta ta rufo 'kofarta,tana ji yana kiran sunanta amma tayi burus.

     Ba 'karamin 'baci ransa yayi ba haka ya koma wajen Reyhana ya tarar da ita tana kuka mey cin rai,rarrahinta yayi yana bata ha'kuri.

              ***

     Sageer ya lura da irin change da aka samu kwana biyu a gidan ,Mommy,Abba,Reyhana ba kamar yadda ya saba ganinsu ba ,kawai de be tanbayi Reyhana bane,abinci ma Mommy ta dena ci tare dasu  dinning haka Reyhana ma ko da daddare idan ya dawo d'akinsa yake shigewa dan yason ko meze ce wa Mommy ba sauraransa zatai ba.               Reyhana sun cikake 40 harda kwana biyu akai ,Ahmad har ya soma gajiya dan haka yau yazo gidansu Reyhana.

       Sanda ya shiga ya tarar da Sageer dake parlour nan suka gaisa ya hau sama yake fad'a ma Reyhana.                Jiki a sanyaye ta tashi ko Nasreen bata d'auka ba dan bacci take.

         Reyhana tana taka step dan ta sau'ka bata 'karasa zuwa parlour ba ta hangi Mommy a palourn.

     Ba shiri ta tsaya cak,da alama Mommy bata dad'e da zuwa parlourn ba,lokaci guda bugun zuciyarta ya 'karu.

      "Shikenan Mommy zata fad'a masa komai". Ta fad'a a ranta tana ja da baya,da sauri ta koma d'aki ta fad'a gado ta shiga aikin kuka.

       A parlour kuwa Mommy bayan sun gama gaisawa da Ahmad ta soma gyaran murya.

       " Uh..Ahmad nasan dole wannan maganar da zan fad'a maka zaka ji nauyinta,amma banyi haka dan na ba'kanta muku ba nayi haka ne dan nema muku sau'kin rayuwa".Mommy ta d'iga aya amma bawai ta gama ba.

      Jin irin kalaman Mommy yasa Ahmad ya tsinci kansa a irin wani yanayi na daban.

      "Ri'kon mace ba abune mey sau'ki ba,kuma musamman ga Reyhana da bata saba da rayuwa irin ta gidanka ba,yanzu kuma idan ka duba zaka ga nauyi ya sake 'karuwa fiye da da wanda ba abune mey sau'ki gareka ba,sana'arka ba mey 'karfi bace da zaka iya ri'ke su dan haka ina neman alafarma daka sawwa'ke wa 'yata Reyhana".

       Ahmad maganar Mommy yadda ta doki kunnensa ze iya cewa be ta'ba shiga tashin hankali kamar na ranar ba,dan jiyake kamar mafarki.Reyhana matar tasa?Ummu Nasreen Azizatynsa?Tir'kashi!

      " Mommy dan girman Allah ki taimaka mini ki dena fad'ar wannan maganar ".Ahmad ya fad'a kamar mey shirin yin kuka.

       " Gaskiya ce dole na fad'a Ahmad,kuma babu uwa da zata so 'yarta ta shiga cikin wani yanayin wahala,inde har soyayyar da kake mata ta gaskiya ce toh baza ka bari ta sha wahala a rayuwarta ba".Mommy ta fad'a.

       "Mommy kiyi ha'kuri amma rabuwa de Reyhana ba abu ne mey sau'ki ba". Ya fad'a already 'kwalla ta cika idanuwansa.

       " Ai nasan da hakan shiyasa nace maka alfarma,kuma nima ba abune mey sau'ki ba na bari 'yata ta shiga wahala".Mommy ta fad'a a lokacin ta fara 'kosawa.          "Mommy ki duba ki tausaya wa rayuwata da halin da zamu shiga nida Reyhana na sani itama bazata so hakan ba". Ya fad'a muryarsa na rawa.

       " Ahmad na gama maganar nan bazan chanja ra'ayina ba,kaje ka sake tunani".Mommy ta fad'a tare da barin parlorn.

        Ahmad ai zama yayi dirshan hawaye na ziba a fuskarsa ya rasa inda ze saka kansa.Wayarsa ya lalubo a aljihu yai dialing number ta Reyhana.

       Ya kirata yafi a 'kirga amma bata d'aga ba,koba a fad'a ba yasan tana cikin wani hali yanzune ya gano dalilin dayasa bata maganar komowarsu sede kullum shi yayi mata.

       Mommy kuwa tana hayewa sama d'akinta ta shige ita kanta ta tausaya masu amma ba ta jin zata iya 'kyalesu haka.

      Reyhana kuwa tana ganin wayarsa amma ta kasa picking dan tuni tasan aikin gama ya gama,batasan mey zata ce dashi ba.

       Ya shafe yafi 30min kafin ya fita daga gidansu Reyhana jiyake kamar yaje d'akin da Reyhana take,haka da'kyar ya iya tafiya direct gidan Umma ya wuce.

     Umma ta tsorata ganin yanayinsa ,kuka yasa mata a tsakar parlour kamar d'an yaro ,ta 'kosa taji abinda ya faru ita ta zaci ko wani abunne ya sami Reyhana ko Nasreen.

       "Ahmad kukan ya isa nace, ka fad'a mini mey yake faruwa se kayita kuka". Umma ta fad'a.

      " UMMA Reyhana,bazan iya rabuwa da ita ba".Ya fad'a cikin kuka.

      "Reyhana? Wa yace zaka rabu da ita?" Ta tamabaya a  kid'ime.

        "Mommy ce  Umma ,bazan iya ba Umma dan Allah kije ki bata ha'kuri". Ahmad ya fad'a.

      Umma ita kanta batasan sanda hawaye ya zubo a fuskarta ba,take tausayin d'anta ya 'karu a zuciyarta.

       "Innalillahi wa inna ilaihi raji'u". Abinda ta furta kenan.

      " Ita Mommy da kanta tace ka rabu da 'yarta?" Ta tamabaya.

      "Mommy wai na saki Reyhana taya zan iya rabuwa dasu Umma ?"

     Umma dafe kanta tayi ta rasa mey yake mata dad'i.An d'an tsahon lokaci a haka ,Ahmad ya bar sheshe'kar kukan sede hawaye gashi idanuwansa yayi ja jijiyoyinsa ma sun tashi fuskarsa tayi jazir.

        "Kayi ha'kuri in Allah ya yarda baza ka rabu da ita ba ,addu'a zakai". Umma ta fad'a.

     Duba da lokacin yasa bata tafi gidan ba ,8pm tayi.

           Gidansu Reyhana kuwa shiru kukeji kowa yana d'aki dan koda Abba ya dawo Sageer ya zayyane wa Abba komai dan yana jiyo Mommy da Ahmad.

      Abba ransa a 'bace ya shiga d'akinsa jira yake gobe tayi ya shawo kan matsalar(Hmm😶).

            Reyhana da dare yayi ko bacci ta kasa gashi Nasser tana ta mata kuka koh cikinta yake ciwo ,ita kad'ai take ta lallashinta amma ta'ki shiru hakan yasa itama Reyhana ta taya ta sukaita kuka bame rarrashin kowa.

       Ahmad ko gidansa be koma ba yana parlourn Umma sallah yayi koh abinci ya'ki ci tunanin Reyhana da Nasreen kawai yake.

               *** Washegari da safe Umma tun asubah bata koma ba ,shiko Ahmad dama jiya beyi wani bacci ba sallah yayi yaita adduo',ise around 4:30am bacci yai gaba dashi.

        Tun bayan sallahr Asubah be koma ba dukda kuwa baccine a idanuwansa.

       Umma around 8am ta tafi gidansu Reyhana dan hankalinta ya kasa kwanciya,inno ce tayi mata iso.Nan inno taje ta sanarwa da Mommy ,ba dad'ewa ta sakko 'kasa.

        Sama-sama ta gaisa da Umma dama tasan meke tafe da ita.

         "Mommyn Reyhana meyai zafi haka...". Ko 'kare maganar batayi ba Mommy ta katseta.

        " Duk wani abu da zan fad'a na riga na fad'a wa Ahmad saboda haka banga amfanin dawo da zance baya ba".Cewar Mommy ba ko damuwa a tare da ita.

        "Ehyi nasan da haka amma dan Allah ki tausayawa yaranannan ki bashi dama ,Ahmad rabuwa da Reyhana matsala ne a gunsa abune me wuya". Umma ta fad'a cikeda tausayawa.

      " Itama Reyhana zama dashi abune mey wuya  a gunta damu kanmu baza muso ta shiga 'kuncin rayuwa ba".Mommy ta fad'a.

       "Dan Allah kiyi ha'kuri ki bar maganar nan". Umma ta fad'a.

       Mommy ta 'kosa sosai dan ta fara kad'a 'kafa komai ze iya fitowa daga bakinta.

       " Nifa yanzu takardarta nake jira bana san sake jin komai".Mommy ta fad'a.

        "Baze sake tan ba".Abba ya fad'a.

       Dama ya gano sanda Umma ta shigo gidan a d'akinsa.

       " Kiyi ha'kuri Umman Ahmad inshAllahu ma yau zan maido da ita gidanta da kaina.Abba ya fad'a.

       "Ba inda zata je, ta gama zaman gidan Ahmad". Mommy ta fad'a.

       Umma da take zaune ta mi'ke tsaye taga abun ba na zama bane.

      Itako already Mommy tun sakkowar Abba ta mi'ke tsaye.

        Ikram datake shirin sakkowa ta hangi abinda ke faruwa dan haka ta shiga d'akin Reyhana da sauri ta fad'a mata.

       " Yaya Umman Ahmad tazo ,kinga Abba ma ya fito suna magana Mommy kuma...".Bata 'karasa ba tayi shiru.                Reyhana ko bata fad'a ba ta gano inda ta nufa,da sauri ta tashi zuwa parlour.

       Daga can gefen bene suka tsaya itada Ikram suna kallon ikon Allah.

      "Ni na fad'a a yau seta koma gidanta". Abba ya fad'a cikin d'aga murya.

      " Ba inda zata je".Cewar Mommy.

       "Dan Allah ayi ha'kuri". Umma ta fad'a.

     Da ace tasan hakan abin ze kaya da bata zo ba,dan haka tayi ta basu ha'kuri.Suna kallo ta fita daga gidan,su kuwa basu fasa ba.

      " Ke kike da iko da ita koh ni?"Abba ya fad'a.

      "Bani bace,kayi yanda kake so kaji". Mommy ta fad'a cikin fushi.

       " Kece kuwa ? ".Abba ya tamabaya .

      Yana mamakin yadda ta sauya ,yasanta da zafi amma ba irin haka ba ace yau har a gaban sirika yana fad'a tana fad'a.

       Yana cikin wannan batun Mommy tayi wucewarta ta haye sama yaran suna kallo.Sageer da se lokacin ya fito daga d'akin ,wajen Abba Reyhana ta 'karasa tana basa ha'kuri ,ba abinda yake illa jinjina kai.

       " Mommy ina zaki je?" Suka jiyo muryar Walida da ta biyo bayan Mommy.Wani irin shock gabaki d'ayansu suka ji ganin Mommy tana sakkowa da trolley.

        Ta yafa gyale ga takalmi data saka hannunta key na motarta,hakan ya bayyana tafiya zatai.

        "Mommy?" Reyhana ta furta cikeda mamaki.

        Har gabansa ta 'karaso ba tare da ta kalli yaran ba tace."Sanda kaga bana nan seka tabbata nice,ga yaranka kaine kake da iko dasu".Mommy ta fad'a fuuu ta wuce.

AR²💖

Jasko💕

Pls share.

     

                  🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣6⃣

       Gabaki d'aya yaran da sauri suka 'karasa wajen Mommy da ta kusa kaiwa 'kofar fita.

       "Mommy dan Allah karki tafi ki barmu". Walida ta fad'a tana ta'be baki zatai kuka.

      " Mommy please kar kiyi haka".Reyhana ta fad'a ta ri'ko hannun Mommy.

     Se lokacin ta kalleta ,Sageer ma 'karasowa yayi.

     Mommy dan Allah ".Ya fad'a muryarsa a raunane.

       " Sakeni".Mommy ta fad'a tana mata wani kallo.

       Reyhana a hankali ta sauke hannunta dan tasan duk dalilinta hakan ta fara.

       Suna ji suna kallo ta fita ,Walida take ta buga 'kafa tana ta kuka tana kiran Mommy.

       Abba da tun d'azu be kalli inda take ba duk da kuwa abun ya damesa sosai ,seda yaga ta fita ga Walida tana kuka.Fita yayi ,yaran zasu biyosa yace su tsaya.

      "Maryam". Abba ya kira sunanta.

      Yana 'karasawa inda take ya fisge trolley d'in daga hannunta.

      " Mey kike tunanin yi? Idan kin tafi ina zaki je"?" Ya tamabaya.

    "Gidan kawu na". Ta amsa.

     " Ki shiga ciki nace".Abba ya fad'a yana nuni da 'kofa.

     "Kusha zaman ku kaida yaranka muddin baze saketa ba ni kuma bazan dawo gidannan ba". Ta fad'a.

       " Adalci kenan ,ki raba auren yarannan?"

       Shiru tayi bata ce komai ba tana tsaye ita bata shiga motar ba kuma bata koma ba.

       "Ki duba kiga yarannan,haka zaki tafi ki barsu wani hali zasi shiga? Abba ya fad'a a sanyaye.

      " Nide na fad'a maka muddin na koma toh seya saketa".Mommy ta fad'a.

      "Muje ki shiga ciki". Abba ya fad'a.

      Tana huci tabi bayansa yaran suna kallo ta shigo da sauri suka je wajenta.

     Reyhana kuwa komawa tayi d'aki jiki a sanyaye. A zuciyarta tana tunanin mafita " Yanzu a kaina yau Mommy take 'ko'karin barin gidannan!" Reyhana ta fad'a a zuciyarta hawaye na gangarowa a idanuwanta.

               ***

   Umma tana komawa gida Ahmad ya 'karaso inda take.

      "Umma ta ha'kura Mommyn" .Ya tambaya muryarsa a raunane.

      Kallonsa kawai tayi amma ta kasa cewa komai.

      "Umma ki fad'a min". Ya fad'a.

      " Ahmad sede mu cigaba da addu'a ,Mommyn ta ta'ki amincewa mahaifinta ne de ya goyi bayanta ba". Umma ta fad'a.

     Labarin duk abunda ya faru ta zayyane masa,hannu yasa ya dafe goshi kansa yana sarawa.

     "Ha'kuri zakai Ahmad duk abinda kaga ya faru Allah ne ya tsara". Umma ta fad'a.

      Seda tayi da gaske yaci abinci kad'an koh fita ya 'kiyi,wayarsa ya d'auka bayan yayi sallahr zuhr yayi dialing number na Reyhana.

     Seda ta kusa katsewa tayi picking.

       " Reyhana ".Ya kira sunanta.

      " Uhmm".Ta amsa dan idan tayi 'kwakkwarar magana kuka zatai.

      "Reyhana dan Allah karki rabu dani ,bazan iya zama bake ba ina 'kaunarki Reyhana". Ya fad'a muryarsa na rawa.

      Jin haka yasa ta shiga kukan da take dannewa." Ahmad taya zanso na barka kaima kasan bazan so na rabu da kai ba".Ta fad'a.             "I know Reyhana". Ya fad'a.

       " Yaya ina tsoro".Ta fad'a.

       "Reyhana inshaAllah muna tare". Ya fad'a duk da kuwa zuciyarsa ta karaya.

      Labarin abunda ya faru bayan tafiyar Umma ta basa, hakan ba 'karamin tsorata sa yayi ba.

       " Yaya bazan iya bari Mommy ta bar Abba a dalilina ba".Ta fad'a.

      Kai kawai ya kad'a kamar yana kusa da ita,sun d'au lokaci kafin Ahmad ya sake magana.

       "I love you so much that I can't afford lose you Azizaty".Ya fad'a.

       " Idan na rabu dake ya zami da Nasreen ? Reyhana I can't do this".Ya fad'a zuciyarsa na sake karaya.

        Kud'in wayar ne da suka 'kare yasa basu cigaba da magana ba ,Reyhana wani sabon kukan ta soma yi Allah yasa Nasreen bacci take.

       Kowa rayuwar ta'ki masa dad'i ,dukansu sun shiga damuwa gashi idan yaje gidan baya samun ganinta yanzu Mommy ma wayar ma so take ta hana su kuma.Reyhana jikinta yayi sanyi dan bata jin zata iya bari a dalilinta Mommy tabar gidan dan haka yanzu tana ganin zatace wa Ahmad ya bata takardarta muddin hakan ze dawo da faruncikin Mommy.Dan yanzu Mommy bata wani sakkowa 'kasa idan kuwa Abba yana parlour bata zama.

      Ahmad koya kira Mommy ya sake ro'konta bata picking call d'insa sede yayi ta tura mata text amma kamar bayi yake ba.

        Reyhana tana d'aki tana shirya Nasreen Ahmad ya kira ,wani tausayinsa taji dan yau kusan kwana biyu Mommy ta hanata picking call d'insa.

      "Reyhana". Ya kira sunanta bayan ta d'aga.

     " Yaya".Ta kira sunansa itama.

      "Are you OK?" Ya tambayeta.

      "No am not". Ta amsasa idanuwanta na tsiyayar hawaye.

      " Reyhana ki dena kuka please ".Ya fad'a

       Bata 'kara magana ba sega Mommy ta shigo.Wata uwar harara Mommy ta watsa mata dan haka ta katse wayar.

     Mommy 'karasowa inda wayar take ta d'auka tayi switching off ba tare da tayi magana ba ta fita.

       An d'au kusan month da arba'in ,ba abunda ya chanza Mommy haryanzu tana kan bakarta dan yanzu ta gaji da zama a haka da ake so take Ahmad ya rubutowa Reyhana takardarta.

     Da kanta yau ta d'au 'kafa taje gidansu Ahmad,Umma kad'ai ta samu a gidan.

      Bayan sun gaisa Mommy take fad'a mata abinda ya kawota.

       " Mommyn Reyhana ba wanda yasan gobe gabaki d'ayanmu,shiyasa nake ro'konki da ki sake bashi dama ko ze samu wani aikin".Umma ta fad'a.

      "Umman Ahmad banzo nan ba dan mu sake tattaunawa akan maganarnan ba ,takardarta nazo kar'ba".Mommy ta fad'a.

      Hakan ba 'karamin 'konawa Umma rai yayi ba ,tasan ta d'areta nesa ba kusa ba danma bata haifi Ahmad da wuri ba amma shine take mata irin wannan maganar cikin kakkausan harshe sekace 'yarta ko si'arta.

       " Amma yanzu de ai kinga yaron baya nan koh?" Cewar Umma.

       "Toh ai shiyasa na zo sanar wa da mahaifiyarsa wata'kila koya rubuta". Mommy ta fad'a.

      " Shikenan inde takardarta ce ze kawo mata da kansa".Umma ta fad'a ranta a 'bace.

       Tashi tayi Mommy ta fita disappointed dan taso ace Ahmad yana nan.

     Umma kawai bin bayan ta da kallo tayi ta girgiza kai.

       Ahmad yana wajen aikinsa amma hankalinsa yana gun Reyhana baida tunani sai nata.

       Wajajen 4pm Ahmad ya shigo gidan dan yanzu kusan koyaushe yana gidan kwana ne yake maidashi gidansa.            Umma seda taga ya kammala cin abincin sannan tayi masa maganar zuwan Mommy.

      "Ahmad yaushe zaka bata takardarta?"Umma ta tambaya.

       "Umma ya kike fad'an haka?" Cewar Ahmad.

      "Kai baka gaji da wannan abun ba ,lokaci yayi da zaka ha'kura Ahmad babu yanda zami da 'kaddara". Umma ta fad'a.

      " Umma saki fa ba abune mey sau'ki ba".Ahmad ya fad'a.

      "Ka fiso a cigaba da zuwa ana cimin mutunci ko,har yanzu baka gaji da wula'kanci ba? Kokuwa so kake se an kai maganar kotu?" Cewar Mommy, daga yadda take maganar ya gano tana cikin 'bacin rai.

     "Umma mey tace miki?" Ya tambaya lokaci guda zuciyarta ta fara tafasa dan zaey iya jure komai amma banda wulan'kanta mahaifiyarsa            "Jin mey tace mini ba shine ba kawai kayi ha'kuri ka sawwa'ke mata kowa ya huta". Umma ta fad'a.

    Kai kawai ya kad'a ba tare da yace komai ba ya fita.

     Gidansa ya nufa,d'akinsu ya shiga ya bud'e wardrobe d'in wasu kayan Reyhana da bata tafi dashi ba ya d'auka yana sha'kar 'kamshin turarenta ,take hawaye ya gangaro fuskarsa.Tun farkon had'uwarsu da ita ya tuna da auren su,sanda tana laulayi,da tafiyarta gida.

      " Shine 'karshen zamanta a gidana kenan?"Ya tamabayi kansa.

      Tuna maganar Umma da yayi yasa ya janyo drawer ta gadon ,takarda da biro ya d'akko ,se 'karewa takardar kallo yake a zuciyarsa yana jin nauyin rubuta mata saki.

      Ya shafe kusan 20min kafin ya d'ora biro a kai.

       Ni Ahmad Yusuf, yau laraba ././... Ya rubuta date.Na saki mata ta Reyhana saki d'aya.

       Yana gama rubutawa yai folding d'inta.

        Seda yasha kukansa tukun ya fito daga gidan,be tsaya a ko ina ba se gidansu Reyhana. A 'kofar gida ya tarar da Sageer ,cikin mutuntawa suka gaisa ya mi'ka masa takardar dan bayajin zai iya bata hannu da hannu.

     Yana bashi ya tafi,shikanshi Sageer jiyake kamar yai kuka.Ko ba'a fad'a ba yasan mene,a d'aki ya isketa tana ta lalla'ba Nasreen tayi bacci.

     Ganin Sageer 'ki'kam a tsaye ya kasa magana amma fuskarsa da damuwa.

        "Sageer meya faru?" Ta tambaya.

      Takardar ya mi'ka mata ba tare da yace komai ba ya fita.

    A sanyaye ta bud'e takardar gwiwarta tayi sanyi...

AR²💖

Jasko💕

Pls share.

    

     🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣7⃣

     Safar  da take hannunta ta Nasreen ta saki a 'kasa,kukan ma ta kasa.

     "Ahmad ya sakeni?" Abinda take ta nanatawa kamar zautacciya.

     Kuka mara sauti ta soma,ita kuwa Nasreen se wuri wuri da ido take tana d'aga 'kafafuwa sama.

       Ahmad kuwa daga gidansu Reyhana gidansa ya koma yai zaman dirshan ,hotunan bikinsu ya d'auko yana ta kalla harda murmushin yake.

      Umma tayi tsammanin dawowarsa amma taji shiru,da ta kira wayarsa a kashe taji dan kuwa baya son jin kowa komai kawai yafison ya zauna shi kad'ai.

      Mommy da maghrib bayan tayi sallah ta shiga d'akin Reyhana lokacin tana toilet.Har zata fita ta hangi takardar a kan gado.

    A hankali ta 'karasa ta d'auka,koda ta karanta wani sanyi taji ya ratsa ta a zuciyarta tace"Alhamdulillah,an rabu da 'kaya".

      Hannunta ri'ke da takardar Reyhana ta fito fuskarta ba annuri da ka ganta za kasan tana cikin damuwa.

      Mommy ita kanta rasa abinda zata ce mata tayi dan tasan a wannan lokacin tana tare da 'bacin rai saboda haka Mommy ta ajje takardar ta fice.

         Abba kuwa da ya dawo Mommy ko kunya haka ta shiga d'akinsa ta sanar masa.

      "Toh yanzu hankalinki ya kwanta koh?" Abba ya fad'a           Mommy shiru tayi bata ce komai ba se turo baki datai a zuciyarta kuwa tana mey jin dad'i.

           Ahmad se wajen 10:30am tukun ya koma gidan Umma da hankalinta ya tashi.

          "Kai kuwa ina ka shiga ina kiranka a kashe wayar?" Umma ta tambaya.

          "Naje gida neh". Ya amsa ciki ciki.

          " Du ka tayar min da hankali". Umma ta fad'a.

         "Kiyi ha'kuri". Ahmad ya fad'a.

           " Abinci fa?" Ta tambaya.

           "Na 'koshi ". Ya amsa ya shige d'aki.

        Kai kawai ta girgiza ta koma d'aki.

       Daren ranar daga Reyhana har Ahmad ba wanda ya iya bacci,daga ya fara gyangyad'i seyai mafarkin Reyhana tana kuka a firgice yake tashi.

                   ***

2weeks later

       Mommy itada Anty Asma'u sukaje gidan Ahmad suka sa aka kwaso kayanta ,dama kud'in hayar ya kusan 'karewa dan haka suna kwashe kayansu Ahmad ya dan'kawa mey gida gidansa.Shi kuwa ya komo gidan Umma.

        9:46pm yana rigingine ya 'kurawa ceiling ido yana tuna last maganar da sukai da Reyhana a waya.

  ** Waiwaye**

             " Reyhana am so sorry, I have no choice ".

        " Yaya na fahimta,stop apologizing ".Reyhana ta fad'a.

        "Wannan itace 'kaddararmu". Ahmad ya fad'a.

            Da'kyar ya iya rintse idonsa ba isashshen bacci yake ba yanzu.

            Mommy kuwa abin Reyhana ya fara isarta tun sanda Ahmad ya bata takardar ta ta dena sakin fuska ,fitowa parlour ma wataran se a wuni bata fito ba.

       Tana gyara gado dan shirin kwanciya Mommy ta shiga d'akin.

       Waje ta samu ta zauna,bayan data d'auki Nasreen da har lokacin idonta biyu.

      " Reyhana ".Ta kira sunanta.

      " Uhm".Ta amsa tana cigaba da abinda take.

       "Reyhana saboda nasa Ahmad ya rabu dake shine bakya son yi mini magana?" Cewar Mommy.

      "Mommy ba haka bane".Ta fad'a tabar abinda take.

         " Toh yayane?"Mommy ta tambaya.

        'Karasowa tayi kusa da Mommy ta zauna gefen gado ta zauna opposite da Mommy.

       "Mommy taya za'ai na'ki yi miki magana akan haka". Reyhana ta fad'a.

      "Toh ya akai kin chanja bakya shiga cikin 'kannanki ko abinci ma bakya ci damu kinga dole nayi tunani ko kina gab..". Mommy bata 'karasa ba Reyhana ta katse ta.

       " Mommy kidena fad'in haka,dan Allah kiyi ha'kuri amma banyi hakan dan na 'batamiki ba ,na bari ".Reyhana ta fad'a tare da tasowa ta zauna gefen Mommy tasa hannunta ta ri'ko yatsinta tana murzawa.

       " Kiyi ha'kuri Mommy ".Reyhana ta fad'a hawaye na sakkowa daga idanunta.

      Mommy kafad'arta ta d'ora kan Reyhana tana tapping bayanta" Ya isa kukan".Ta fad'a.

      Kai kawai take kad'awa ba tare da tace komai ba.

       Daga wannan lokacin Reyhana ta cigaba da sakewa dasu,sun dawo kamar da tana sakkowa parlourn suyi kallo duk wata damuwarta ta danne a ranta.

       Ta 'bangaren Ahmad a 'yan kwanakinnan yakan fita majalissa wajen abokansa,ko be fito ba Sadiq abokinsa da kansa yana shigowa ya tayashi hira kuma yana kwantar masa da hankali.

      Yau d'inma ganin be fito ba yasa sadiq ya zo gidan.A d'aki ya tarar dashi ,wayarsa ce a hannunsa amma bawai tapping yake ba kawai wasa da ita yake a hannunsa amma hankalinsa baya gun.

      "Maza! Yane ka zauna a d'aki kai d'aya baka fito ba?" Sadiq ya tambaya.

        A kasalance ya d'ago da kansa ya kalli sadiq.

      "Sadiq". Ya kira sunansa.

        Zama yayi kusa da shi kan katifarsa.

       " Ahmad kai baka gajiya neh? Koyaushe cikin tunani haba mana ya kamata ka dena damun kanka haka".Sadiq ya fad'a.

      "Sadiq baza ka gane bane,bakasan yanda nake ji bane". Ahmad ya fad'a.

       " Ai gashi se rama kake,lafiyarka nake jiye ma se kace ba namiji ba duk wani abu daya sami mutum qaddararsa ce haka ba yadda zami,yin haka ba abinda ze 'karama illa kashe maka zuciya".Sadiq ya fad'a.

      "Toh naji".Cewar Ahmad yana gyara kwanciyarsa.

       " Ni da zaka bi shawara ta ma da ka mance da wannan damuwar".Sadiq ya fad'a.

      "Na mance" Ahmad ya maimaita cikeda rainin hankali.

      "Yes,akwai wani scholarship da naji ana cikewa na cyprus ,abinda yasa banyi ba    saboda waec d'ina banda English ,kai kuwa naga kana da result mey kyau why not kai applying?"

       "Mtchww! Ina cikin wannan yanayin zakai min maganar scholarship". Ahmad ya fad'a.

      " Cigaba ne fa ,wai kai shikenan ka kashe rayuwarka ko meh,rabuwa da Reyhana baya nufin yin destroying life d'inka koh ita ance ma haka zata zauna tayi ta damuwa kamar yadda kake ?" Sadiq ya fad'a cikin fushi.

      "Ni kaga rabu dani". Ya fad'a.

       "Karka saurareni d'in rago kawai ". Sadiq ya fad'a tare da talle masa tafin 'kafarsa ya fita.

      Ahmad ya d'au pillow da niyyar cilla masa yaga ya fice.

          Washegari da safe koda ya gaisheda Umma yaji tayi masa maganar da Sadiq yayi mishi jiya.

          " So zuwa yayi ya fad'a mata".Ahmad ya fad'a a ransa.

       "Umma ki rabu dashi shirmensa ne". Cewar Ahmad.

      " Kaide kake shirme,ca akai ma kowa irinka neh da be iya ri'ke 'kaddara ba".Umma ta fad'a.

      Shiru yayi bece komai ba ,ita kuma ta tafi kitchen had'a karin kumallo.

                   ***

    Ahmad kalaman Umma da Sadiq ne suka fara tasiri a zuciyarsa,dan yana ganin inde ya cigaba da zama haka zuciyarsa ce zata mutu gara ya mi'ke ya zama cikakken namiji.Zuciyarsa ta fad'a.

      Sede fa yana tunanin kuma barin Umma ita d'aya haka bayanan waze dinga kula da ita?

        Haka yayi ta tunaninsa gashi koyaushe cikin addu'a yake Umma ma bata dena ba.Cikin ikon Allah yaji 'kuncin da yake zuciyarsa yana raguwa kuma scholarship d'in ya soma kwanta masa a rai.

      5days later ,da kansa yace wajen Sadiq ya fad'a masa ya amince ,sosai Sadiq yaji dad'i .Ba 'bata lokaci yayi applying cikin ikon Allah yaci jarabawar,sauran month ya rage su tafi.

       A cikin 'yan kud'ad'en aikinsa yayi wa Nasreen siyayyar 'yan kayan pampers da sabulun wanka.Umma da kanta ta kai wa Reyhana ,cikin girmamawa suka gaisa da Umma ranar Mommy ma bata gida.

       Haka rayuwa ta cigaba da kasancewa da dad'i babu ,tafiyar Ahmad ya rage week shida Umma sunje Zaria yayi sallama da wasu 'yan uwan ,wani yayan Umma ya bashi 30k ,shima wasu 'yan kud'ad'en nasa ya had'a dasu kad'an daga ciki yayi wa Umma 'yan siye-siyen kayan abinci.

       Ana saura kwana biyu tafiyarsa ya kira Reyhana suka gaisa yake tambayarta Nasreen, sede beyi mata maganar tafiyarsa ba,da ba zeje gidan ba seda Umma tayi da gaske yaje,Nasreen ta sake wayo kamanninta dashi sun sake bayyana yayi mata pics a sabon wayarsa da ya siya.

    Umma harda kukanta amma bata nuna a gabansa ba ,ranar da ze tafi shi kansa ya kasa cin abinci har airport Umma da Sadiq suka rakasa ✈(Nima nayi 'kwalla😧).

AR²💖             Readers! Ya kuka ga page d'in? 🔥🔥pls comment,vote ,luv u all😘

   Jasko💕

Pls share

       

     

       🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

      *Thank you so much for your warm support Ummeeytr,sisi kema ban manta dake ba ina godiya ,masoyan littafinnan na whatapp godiya mara adadi Allah ya barmu tare 😘 Ameen.*

🅿 1⃣8⃣

         Umma da suka dawo tare da Sadiq jikinta a sanyaye ,tana tunanin yadda ze gudanar da rayuwarsa har tsahon lokacin da ze gama karatunsa,dan d'an nata be ta'ba yin nisa da ita ba kamar wannan karan.

       Around 8pm Umma taji ringing d'in wayarta ,koda ta duba international number ta gani,dama a cikin ranta tayi tunanin Ahmad d'inta neh.

         "Umma". Ya kira sunanta.

         " Ahmad kaine".Umma ta fad'a da saurinta.

         "Eh". Ya amsa.

          " Kun isa lafiya?" Ta tambaya.

          "Lafiya lau Umma". Ya asa.

           "Toh kuna makaranta ne ko kuwa?" Ta tambaya.

           "A'a mun samu Apartment ne tare da  wasu 'yan kano da muka tafi dasu". Ahmad ya fad'a.

          " Toh abinci fah ?" Ta tambayesa.

           "Zanci". Ya amsa.

            " Toh ka samu de kaci karka zauna da yunwa kaji".Cewar Umma cikeda damuwa.

        "Toh inshaAllahu". Ya fad'a.

         " Yawwa ka kula sosai".Ta fad'a.                "InshaAllah". Ya amsa.

     Daga haka sukai sallama,bayan nan ya kira Sadiq ma ya sanar masa ya isa.

        Ahmad ya samu yaci abinci kad'an duk da kuwa yana jin yunwa ,kawai kewa ce da ba'kunta suka sa ya kasa ci dayawa.

       Sauran da suke apartment d'aya dashi suna falo su uku se surutu suke kamar ba wanda yau neh zuwansu na farko ba,Ahmad kuwa rufo 'kofar d'akin da yaye ya kwanta dukda ba shi kad'ai ne a d'akin ba.           Da'kyar ya samu bacci ya kwashe shi dan daya rufe idanuwansa Reyhana yake gani.

Washegari,6:08am ya tashi,hayaniyarsu ce ta tashe shi.               Da sauri ya mi'ke yayo alwala yayi sallah.D'ayan room mate nashi yaga ya baje se narkar bacci yake da alama beyi sallah bama.

      'Karasawa yayi gadon da yake ya tasheshi,daga nan ya komo ya zauna.

       Ba jimawa sauran guda biyun sukai knock a d'akin.

        " Shigo". Ahmad ya fad'a.

         "Assalamu Alaykum". Sukai sallama.

      Ahmad ya amsa musu ,'karasowa sukai  wajensa sukai handshake.

        Nan suka sake introducing kansu.Da Ibrahim da  Idris se room mate na Ahmad, Imran sunansa.

        Kusan shine  sa'an Ahmad sauran kuwa baza sufu 22 zuwa 23 ba.

        Tare dukansu suka fita cin abinci a restaurant bayan sun shirya.

        Shawara sukai a junansu suka siyi kayan abinci ,inyaso sa dinga girkinsu a gida.

        Hrs later Ahmad ya kira Umma suka gaisa ,basiyi wani hira mey tsaho ba credit ya 'kare.

        Shi gashi ba mey hira ba sosai,yana hangosu a falo suna ta hirarsu kowa yana bada labarinsa banda shi da ya ma'kale a d'aki.

                    ***

       Duba da sun fara shiga class Ahmad ya bada attention akan karatunsa,inda yaci sa'a shima Imran yana son karatu,kuma a kwana biyu ya fara sakin jiki dashi sede har yanzu duk cikinsu ba wanda yasan Ahmad ya ta'ba yin aure.Suna waya da Umma amma ba koyaushe ba ,Sadiq ma.

     Tunanin Reyhana da Nasreen kuwa kullum dashi yake kwana yake tashi gashi har yanzu be sake yin waya da ita ba.

                    ***

Nigeria ***

        Umma ganin an d'an kwan biyu bata jin labarin 'yar jikallenta Nasreen dan ba waya take da Reyhana ba haka yasa ta shirya zuwa gidan.

        Lokacin da inno tayi mata iso falo sisters d'in Mommy suna nan sun baje se hira sike irin ta mata sun cika falon da hayani.

     Umma kan kujera ta zauna ,Anty Ummi ce ta lura da shigowarta ta gaisheta.Suma sauran suka gaisa da ita ba nuna alamar sun ganeta,Mommy tare da Anty Asma'u suka sakko daga bene.

       "Kamar babar Ahmad nake gani". Cewar Anty Asma'u 'kasa-'kasa.

       " Ehyi itace".Mommy ta amsa.

       "Toh ita kuma mey tazo yi?"Cewar Anty asma'u.

        "Kema kya fad'a". Mommy ta fad'a.

        Shiru sukayi basu sake magana ba lokacin da suka 'karaso inda Umma take.

        Umma bayan ta gaisa dasu take tambayar su Reyhana.

        "D'azu yara sun fita da ita za'ai mata photo,Reyhana kuma tana bacci". Mommy tai 'karya dan kuwa tana d'aki tare da Reyhana.

        " Ayya!"Umma ta fad'a a ranta bata ji dad'i ba.

         Daga haka shiru ya ziyarci d'akin,su kansu masu hirar shiru sukai suna 'kus-'kus Anty Ummi se alamu take musu da siyi shiru suka 'ki.

      Hakan yasa Umma ta tsargu,tana jiyo wata daga cikinsu tana cewa Anty Ummi "An rabu kuma meye na bibiya".

         Umma in ranta yayi dubu ya 'baci,a ranta tana fad'in "Zuwa ka duba 'yar d'anka ma ya zama laifi".

       Mi'kewa tayi taiwa Mommy sallama ta fita, bata kai bakin gate ba tajiyo kukan Nasreen kasancewar window na d'akin Reyhana a bud'e yake.

         Umma jin kukan Nasreen yasa ta gano 'karya Mommy tayi mata,ba yadda ta iya haka ta fita.

       Se bayan tafiyar Umma Reyhana taji Ikram da Sageer suna maganar,ji tayi dama ta sakko falo lokacin." Sema ta d'auka ko ina sane na'ki fitowa".Ta fad'a a ranta.

                  ***       Umma tana isa gida taga Sadiq a 'kofar gida.

         "Umma unguwa kika jene?" Ya tambayeta.

        "Naje gidansu Reyhana duba Nasreen ne". Ta amsa .

      Daga yadda ya kula da fuskarta ya gano wani abu,seda suka shiga ciki ya sake tambayarta.

        "Ta 'kara wayo koh?"

         "Ai dayake ban samu na ganta ba". Umma ta fad'a tare da shimfid'a tabarmar dake jingine a tsakar falon.

      "Toh ya akai haka?" Cewar Sadiq yana son sake jin 'karin bayani.

      "Cha sukai wai an tafi kaita photo". Umma ta fad'a.

      " Cha sukai? Kuma Umma kin yarda? Toh ina ita Reyhanan?" Sadiq ya tambaya.

        "Nide ban ganta ba tana bacci suka ce".Umma ta fad'a.

       "Rainin hankali". Ya furta.

        Umma kaf ta bashi labarin abinda ya faru ,Sadiq   dama akwai saurin fushi lokaci guda ya hau masife -masife shi har Reyhana d'inma yayi blaming.

        Umma seda tayi ta bashi ha'kuri wai seyaje gidan yayi musu rashin mutunci.

  Cyprus 10:07pm ,Ahmad yana zaune kan kujera yasa litattafi a gaba yana karatu wayarsa tayi ringing.

     Koda ya duba yaga Sadiq,fuskarsa d'auke da murmushi yai picking.

       "Saddiqu". Ahmad ya kira sunansa.

       " Ya ,ya karatu?" Ya tambaya.

      "Alhamdullilah gashi muna tayi". Ahmad ya fad'a.

       " MashaAllah,toh bari na barka".Sadiq ya fad'a.

       "No !wait". Cewar Ahmad.

       " Wani abune?" Sadiq ya tambaya yasan Ahmad idan yana so ya fad'i abu haka yake.

       "Umma tana zuwa ganin Nasreen kuwa?" Ahmad ya tambaya.

       "Danme zata ke zuwa ana wula'kantata". Cewar Sadiq ba tare da yasan ze fad'i hakan ba.

        "Bangane ba Sadiq? Zuwa tayi suka wula'kantata!?" Ahmad ya tambaya ,pen d'in dake hannunsa ma ya ajje.

       Shiru yayi kafin ya fad'a masa duk yadda akai.Bayan sunyi sallama dashi ya ajje wayar gefe yana mey jin zafin abinda sukaiwa Umma.

        Da tunanin abin ya kwana ko karatun ma 'kin cigaba dayi yai ya rife littafin.

           °°3 years later°°               Abubuwa da dama sun sauya ,Reyhana har yanzu bata sake wani auren ba duk wanda yazo yana sonta korarsa take tace ita bata shirya ba,tun Mommy tana magana har ta gaji ,ta koma Masters ma ta'ki aikin ma a nemo mata bazatai ba.Abba kuwa duk abinda tace bataso baya takurata ,Mommy ma sanin dalilinta Reyhana ke zawarci yasa bata takura mata.

       Nasreen ta 'kara girma ,3yrs da 'yan kai kamanninta da Ahmad ba abinda ya sauya sede 'karuwa ma.

       Ikram ce ta fito daga d'akinta taci kwalliya,yanzu ake jin 'yanmatanci tana 21yrs, biki ake a dangin Abba shine zasi dinner.

      D'akin Reyhana ta shiga inda ta tarar da ita ko d'auri batai ba se fama take da Nasreen ita a lalle setayi kwalliya ,kuma kawai salon 'bata fuska ne da kayan kwalliyar kansu.

       "Kai! Yaya ko d'auri baki ba haba dan Allah wannan ai har a gama dinner d'in". Ikram ta fad'a.

       " Inyee irin wannan d'auri haka pls nima d'auran irinsa".Reyhana ta fad'a.

       "Anty nima ki d'aura min". Nasreen ta fad'a cikin muryarta da bata gama fita ba.

        " Kinga fuskarki kuwa!" Cewar Ikram sanda ta kalli Nasreen.

         "Barni da ita nide gama d'aurin". Reyhana ta fad'a tana mi'ka mata d'ankwalin matiriyal  d'in.

       Sky blue ne ,d'inkin ya hau jikinta sosai doguwar gown ce ta shawu,itama Ikram irin kayan ne a jikinta.

       D'auri Ikram ta tsantsarawa Reyhana ga kwalliya data 'kara mata sosai ta fito kamar ba itace mey 3yrs daughter ba.

        Farin gyale d'an siriri ta yafa se purse silver ta zira takalminta me tsini silver.

         " Ummie zan biki". Nasreen ta fad'a tana miko hannunta.

         "Allura akewa yara a wajen,ki zauna da anty Walida". Reyhana ta fad'a tana spraying turare a jikinta.

       Dede lokacin Mommy ta shigo,baki wangalau ta saki ganin irin yafen da Reyhana tayi.

       " Reyhana mayafinne zaki sa'kala haka  a kafad'a?" Mommy ta fad'a.

       "Dinner fa akace". Ta fad'a tana kallon mudubi.

        " Toh ita wannan fa?" Mommy ta tambaya tana kallon Reyhana.

         "Tana tare daku mana Mommy". Cewar Reyhana.

           "Ikram mije,bye baby girl". Cewar Reyhana tare da shafa kumatunta ta d'auka key d'in motarta.

            Ko jira abinda Mommy zata ce basi ba suka fice,take Nasreen ta rusa ihu,Mommy kanta ta dawo tana rarrashinta" Atoh babarki ta ya dake".Mommy ta fad'a.

        Galleliyar farar Accord Abba ya siya mata bata fi shekara d'aya ba.

        Da sauri ta zugesu suka bar gidan gudun kar Abba ya dawo yace dare yayi tunda 9pm ya shige.

         Ba jimawa suka isa wajen bikin, sakin baki sukai dukansu ganin Sageer a wajen shida wata beb suna zaune.

          "Ikram kinga yarannan koh?" Reyhana ta fad'a disbelievingly.

          "Yes,na ganshi". Ikram ta amsa tana kad'a kai still bata d'auke idonta a kansu ba.

        " Ina cayai mana baze samu zuwa ba kansa ciwo yake,amma kin ganshi".Reyhana ta fad'a harda nuni da hannu.

       "Ai bama wannan ba kalli jibgegiyar da yake kulawa wannan ai seta zaune shi". Ikram ta fad'a.

      Dariya suka hau yi ganin de abin bana 'kare bane suka 'karasa ciki ba tare daya kula dasu ba,dan yayi nisa se tsarata yake, ita kuwa madam d'in ta hakince se blushing take.

       Sageer bade 'yan mata ba,number 1 ne wajen kula bebs,ga tsaurin ido as age d'insa 24 da 'yan kai se a gansa da 'yan 25 zuwa 26 ma,duk wannan abin da ake Mommy bata da labari dan ita a ganinta Sageer har yanzu yaro neh.

       Reyhana tunda tayi pic da Bride ta samu seat ta hakimce,Ikii ta bari can itada sauran sa'anninta suna ta shoshalewa.

        Kamar daga sama taji muryar namiji.

        " Assalamu Alaikum".

    Tana d'ago kanta taga Sameer(D'an yayan Mommy).

            "Sarkin naci". Ta fad'a a ranta.

             A ciki -ciki ta amsa sallamar,take ta d'aure fuska.

            " Toh waye ya fad'a masa ina nan?" Ta tambayi kanta,wata zuciyarce tace"Ikram".

       "Munafuka!" Ta furta.

       "Na'am?" Cewar Sameer.

        "No bance komai ba".Ta wayance ,batai tunanin yajita ba.

         " Surprise, right?"Ya tambaya yana d'age gira .

     Hakan yana d'aya daga cikin abinda yasa take jin haushinsa,iyayin tsiya.

        "Surprise d'in mey kuma?" Ta fad'a cikeda 'kosawa.

         "Ehman,I know zaki mamakin ganina anan tunda baki sanar mini ba". Ya fad'a.

          " May i sit?"Ya tambaya.

          "Uhmm". Ta fad'a.

      Ji take kamar ta kurma ihu,hirarsa tamkar kukan sauro haka take ji.

      " Thanks". Ya fad'a.

     Thanks d'in ma cikin wani murya da bata so ya fad'a.

       Dinner d'in ma seda tayi regretting zuwa saboda Sameer,ya cika ta da surutu iya kaci tace "Eh ko a'a.

       10:39pm na bugawa ta kira Ikram suga tafi,kafin su tafi a wajen ma seda ya isheta.

     A hanya tayi ta balbale Ikram da masifa har suka is a gida ,Nasreen tuni tayi bacci da sand'a suka shiga d'akunansu kar Abba ya jiyo su.

       Sameer tun kafin tayi aure yake son Reyhana ,amma fafur ta'ki shi.Bata dad'e da aure ba ya tafi America ,befi shekara  d'aya da dawowa ba yaji labarin mutuwar auren Reyhana shine ya sake komowa har yanzu beyi aure ba ,yana da shekara 32 a yanzu.Ba fari bane chan yana da kyau shima kuma dogo ne,ba 'karamin son Reyhana yake ba gashi duk yadda takai ga shunning d'insa baya ha'kura.

    Cyprus***

         Zaune kan kujera a falo,su Imran sun d'an fita.Ahmad yanzu sun zama 'yan gari sun saba da abubuwa ,Imran dashi sun zama abokai sosai shi kad'ai yasan ya ta'ba yin aure,hakan ma wani lokaci ne daya ga pics na Nasreen a wayarsa kuma yana yawan ji yana maganarta a waya idan sunyi waya da Umma.

        Babu wani chanji sosai gameda shi na shekaru sede fatarsa data 'kara yin haske, ga gashin kansa ma da yanzu ba sosai ya fiya askeshi duka ba ,yananan luf-luf hakan yana daga cikin amsarsa da weather d'in 'kasar tayi.

       Kiran daya shigo wayarsa ne yasa ya ajje cup d'in tea dake hannunsa.

    Number ne daga Nigeria ya gani amma besan mey shiba.

            "Assalamu Alaykum". Ya fad'a bayan yayi picking.

            " Waalaikumussalm". Yaji muryar mace ta amsa.

   AR²💖

         *Toh! Readers guess who?*

   Jasko💕

       *Comment,share and vote, luv u all😘*                       

         

       

      

     

        🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 1⃣9⃣

        "Ya Ahmad ina kwana".Aka fad'a daga d'ayan 'bangaren.

         " Lafiya lau".Ya amsa yana so yayi recognizing muryar me magana.

            "Zainab ce". Ta fad'a.

             " Oh! Zainab, ban d'auki muryar ba ya gida?" Ya tamabaya.

              "Lafiya lau,ya karatu?" Ta tamabaya.

              "Alhamdulillah". Ya amsa.

              " Ina gidan Umma fah".Ta sanar masa.

             "Ok ,kuna hutu ne??" Ya tambaya.

              "Uhh ai mun kammala ma". Ta amsasa.

        " Good,Allah yasa albarka". Ya fad'a.

           "Ameen,ga Umma zakui magana". Ta fad'a.

         " Ok bani ita".

        Umma da take kusa da ita ta mi'ka mata.

        "Ahmad kaji wayata shiru koh?" Cewar Umma bayan ta ma'kala a kunnenta.

        "Eh na kira bana saminki". Ya amsa.

         " Wayar ce ta samu matsala shine nasa Zainab ta kira ka ,tazo nan gida dayake ta samu admission a B.U.K  zata fara zuwa".Umma ta fad'a.

     "Ok,yanzu take fad'a mini sunyi graduation ashe har ta samu admission". Cewar Ahmad.

      " Ehh,na sami mey taya ni zama".Umma ta fad'a.

        "Gaskiya kam,zan kira sadiq seya kai maki gyaran wayar taki".

        Hira kad'an suka ta'ba sannan sukai sallama.

                ***      Ta 'bangaren su Reyhana kuwa Inno ta tafi garinsu anyi rasuwa,yau kowa daya tashi seya nufo dining yaga wayam.

        " Mommy kuwa ta fito?" Reyhana ta tambayi bassam da yake falo shida Walida suna kallo.

       Bassam a shekaru ukunnan ya 'kara girma sosai dan ya kere Reyhana a tsaho yana 18yrs a yanzu,Walida ma ta 'kara tsaho se siranta kamar a 'balla ta😂

       "A'a". Suka amsata.

       " Tohh! 9am fah,kace yau za'a sha yunwa kuwa".Reyhana ta fad'a tare da shiga kitchen d'in.

      Ruwan tea ta d'ora a tea pot ta komo falo tai joining d'insu.

     Ba jimawa Mommy ta sakko."Ina kwana ".Suka gaisheta a tare.

      " Lafiya".Ta amsa had'e da yin hamma.

     "Bade baku d'ora wani abu ba?" Mommy ta tambaya.

      "Ina fa,yanzu kowa yake tashi". Reyhana ta amsa.

      " Aiko yau kowa ya d'and'ana inno kunsan bata nan nima yau hutawa zanyi kwasan yadda kukai".Mommy ta fad'a.

    "Nide na d'ora tea,Ikram da Walida kuyi saura". Reyhana ta fad'a.

      Ikram tana bacci Walida ta taso ta se turo baki take ita batason aiki.

       Sageer yana fitowa daga d'akinsa yaji kiran Reyhana, sasu tayi a gaba har bassam suka shiga kitchen Mommy tai zamanta a falo.

      " Oya jeki d'ebo dankali keda Walida zaku fere"Reyhana ta fad'a.

      Sageer shi dariya ma abin ya bashi saurayi dashi wai za'a had'a da girki.Gefe guda ya tsaya ya nad'e hannunsa  yana kallan ikon Allah ,jira yake yaga shi kuma nashi aikin.

      "Toh su Sageeru se'ai blending pepper da onion". Reyhana ta fad'a tare da dire kayan miyan data d'ebo a bowl.

      Wani dariya ya fashe da ita harda ri'ke ciki." Haba kema da wasa kike ki dubi kamar ni kice nayi wani blending sekace cooku".

     "Kana mamaki koh,karkayi yaro in kasan wata bakasan wata ba".Ta fad'a tare da d'an matsowa kusa dashi ta rad'a masa yadda  su Walida baza suji ba.

       "Koh kayi ko kuma na fad'a wa Abba da Mommy d'ansu ya girma har Beb yana da ita".

         Sageer da sauri ya zaro ido yana mamakin yadda akai ta sani,what if da gaske zata fad'a ? Ya tambayi kansa.

     " Naji".Ya fad'a.

    Murmushin da yake ma ya koma ciki,turn d'in Reyhana ne se murmushin mugunta take.Su Ikram da suke jira suga zeyi ko baze ba take suka hau 'kunshe dariyarsu.

     Bassam kuma aka had'ashi da 'bare spices da za a had'a sauce d'in.

      Kowa aikinsa yayi facing Ikram se masifa take wa Walida wai tana fallatsa mata ruwa idan zata saka dankalin a ruwa.

     Sageer wai dan yayi sauri se wani cakumar attarugu yake yana cire 'ya'yan attarugun da hannu yana cillawa a blender d'in.

     Bassam mey spices har ya gama yana shirin fita ta tsayar dashi."D'an albarka  a soya wa 'yata indomie da 'kwai mana".Ta fad'a tana masa winking eye.

     Buga 'kafa yayi ya dawo se 'kun'kuni yake.

       Sageer bayan ya gama blending har ze fita yaji saman idonsa na 'kai'kayi, yatsansa ya d'ora ya sosa wheui!

    Lokaci guda ya fara dancing a tsakar kitchen d'in, Reyhana da ta d'ora kaskon suya taji 'kara.

     Kallone ya dawo kansa,Mommy da take falo ma seda ta jiyo ta shigo kitchen d'in.

      "Lafiya?" Ta tambaya.           "Mommy idona!" Abinda yake fad'a kenan.

       "Kai mey ta kaika sa yaji a ido sekace yaro". Mommy ta fad'a tana dafa ha'ba.

        " Zoka tara idon a fanfo ka wanke".Reyhana ta fad'a kamar mey shirin yin dariya.

        "A daddafe ya 'karasa sink d'in yaje ya tara fuska ,duk da ya wanke idon be fasa dafe idon ba.

       " Ka tsaya mana a hure ma".Reyhana ta fad'a tana d'age ta dafe kansa sekace 'kan'kanin yaro.

      Ba su Ikram ba har Mommy seda tayi dariya,'kwace kansa yayi ya tsaya yana gogewa da hannun rigarsa.

     Ficewa yayi daga kitchen d'in ya barsu suna dariya."Maganinka kenan".Reyhana ta fad'a.  

     Kafin su gama girkin seda suka 'bata kitchen d'in, se 10:30am suka chi abincin.

     Nasreen da ta dad'e da tashi amma bata fito ba tana toilet ta saki fanfo se wasan ruwa take.

        Seda Reyhana ta koma d'aki ta jiyota,fito da ita tayi ta 'kwa'k'kwad'eta tayi ta kuka seda Abba ya rarrasheta.

       Har Reyhana tayi wanka ta shirya Nasreen bata sake hawowa saman ba,a falo ta iskesu ita da su Mommy.

      "Zo muje nayi miki wanka".Ta mi'ka mata hannu.

      Kafad'a ta ma'kale ita bazata yi ba,Reyhana ta mance ma fushi take.

      " Ki zauna hakan ina ruwa na,ki fara zuwa makaranta kowa ma ya huta".Cewar Reyhana tare da zama daga gefen Walida.

     Ba jimawa wayarta tayi ringing, tana dubawa taga Sameer.

        "Mtchww!". Tayi tsaki ta ajje wayar.

         Mommy data kula da ita tace " 'Kalau?"

       "Sameer ne". Ta amsa.

        "Toh kuma seki 'ki picking? Ni bana son wula'kanci".

         " Mommy damuna zeyi kawai".Reyhana ta fad'a.

      Se a kira na biyu neh tayi picking,bayan sun gaisa take ce mata yana bakin gate.

      "Toh ka shigo mana". Ta fad'a.

        Bata jira amsarsa ba ta katse wayar,wani haushinsa take ji.Yana shigo bayan sun gaisa ta koma d'aki taja hannun Nasreen da se surutu take masa.

               ***    Har Sameer ya tafi bata fito ba tana d'aki.Da yamma Aunty Asma'u tazo gidan Mommy.

        " Ya kuwa wannan mutanen har yanzu shiru?" Anty ta tambaya.

       "Hmm har yanzu, duk tsahon shekarunnan da aka shafe shiru koh waya basu sake yi ba". Mommy ta fad'a.

      " Amma wannan basu da mutunci,ace ko kira suji lafiyar 'yarsu bazasi ba balle akai ga ha'k'ko'kinta kuma,wannan akwai mutanan banza,ita Reyhana idan ta kirashi baya amsawa neh?" Anty Asma'u ta tambaya.

      "Toh wayar ta samu tashiga ma tukun,kuma idan ma an sameshi tace masa meh?" Mommy ta 'kare da tambaya.

     "Tuna masa zatai ba dutse bace 'yarsa ,su wannan da wane idon ma zasi kalli yarinyarnan? 'yarda a yanzu idan ance babanta bata sani ba".

     " Ita ajinta kakanta ne Abbanta ai,barsu su cigaba da yanda suke so lokaci zezo zai nemi 'yarsa aikoh".Cewar Mommy tana jinjina kai.

               ***      2 days later

       Zainab around 9:30pm lokacin tana d'aki Umma ma ta kwanta,wayarta ce a hannunta tana chat a Whatapp.Contact take dubawa idanta ya tsaya kan sunan "Ya Ahmad" kamar yadda tayi saving.

     Tana gwada bud'ewa taganshi online,haka kawai ta tsinci kanta tana son yi masa magana,typing tayi ta tura masa sa'ko kamar haka;

"Assalamu Alaykum,ina yini".

   Seda aka shafe kusan 10min yayi reply dan har ta fita daga profile d'insa.

        Ahmad be kula da message d'in ba da wuri,ganin  "Xynab" kamar yadda yayi saving yayi reply da;                              "Wa'alaikumussalam,lafiya lau".

      " Ya kke? Ya school ?"Ta tura.      

    "Alhamdulillah,ya kuke ?" Shima ya tambaya.

"Lafiya lau".Tayi replying.

" Ina Umma koh tayi bacci?" Ya tambaya.

    "Eh". Ta amsa.

      " Ok". Ya amsa.

Yatsa ta sa a baki tana tunanin mey zata kuma cewa ,kusan 2min basu sake magana ba.

    "Kin fara zuwa school d'in?" Ya tambayeta.         Murmushi ta fara yi ganin ya sake mata magana wanda bata zata ba.              "Se Monday". Ta amsa.

" Ok,wani course?"Ya tambaya.

"Industrial chemistry". Tayi replying.

" Good👍 Allah ya bada sa'a".Yayi sending.

"Ameen, tnx". Tayi replying fuskarta d'auke da murmushi.

  " It's 10pm right? You should have sleep.

"Yaya by 11:00 dae koh". Tayi sending.

" 😱 it's late ,what will you do?"

"Ha! Chatting with you mana". Ta tura.

     " Are you sure? "Yayi sending.

    " Yes mana don't you believe me?"

"I do believe, ok am quitting now".Ya tura.

" Ok,nima yanzu zan kwanta".

"Gudnight ,recite du'a before sleeping".

" Tam night,bye".Ta tura.

Kamar yadda yace tayi addu'a tukun ta kwanta,shima ajje wayar yayi ya dauro alwala ya tada sallah.      

AR²💖

     *Comment,share and vote pls.Luv u all😘*

Jasko💕       🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣0⃣

    Alhamdulillah we reach page 20,happy page twenty🎈🎈   Umeeyr tace "Zainab want to snatch our ya Ahmad " 😂 Juma'at Kareem.

     Reyhana kwance a kan gado ,Nasreen na manne da jikinta ta zagaye hannunta a bayanta da hannin damanta na hagunta kuma tana shafa mata gashin kanta,Nasreen da tayi nisa da bacci hankalinta kwance.

       Babu rana da zata wuce Reyhana batayi tunanin Ahmad ba,idan ta tuna shekarun da aka shafe basu sake had'uwa ba kuma ba waya seta ji haushinsa wani 'bangaren zuciyarta kuwa har yanzu da gurbin sa a ciki."Meyasa ze guji 'yarsa? Mey Nasreen tayi masa a duniyannan daya watsar da ita?" Abinda kullum take tambayar kanta wanda amsar hakan ta gagara.

       Bata yi aune ba taji danshi a fuskarta,hannun ta sa da goge hawayen ,the more tana gogewa the more yana sake fitowa dan haka ta dena mah,gam ta sake ri'ke Nasreen a jikinta tare da d'ora ha'barta lightly a goshinta ,idonta ta rufe gam ba jimawa bacci yai gaba da ita.

                 ***

    Zainab 8am ta tashi dan bata fiya bacci dayawa ba bayan subh,kamar kullum a nitse tayi shara ba tare da Umma ta tashi ba,haka toilet ma ta wanke sannan ta koma d'aki.

       8:20am,wayarta dake jone a charge ta zare.Chat da sukai da Ahmad jiya ta shiga dubawa a hankali step by step tana sake karantawa tana murmushin.

       Data tayi switching on ko zata ganshi online,koda ta duba taga be hau ba tun jiyan.

       Tana jiyo fitowar Umma daga d'aki ta ajje wayar ta fita,cikin rissinawa ta gaisheta.

      "Zainab da sassafennan kika tashi harda shara".Cewar Umma.

      Murmushi kawai tayi ba tare da tace komai ba." To sannunki da 'k'o'kari".Umma ta fad'a.

       Har abincin breakfast tare sukai da ita,ko wanke-wanken ma bata bari Umma tayi ba ,haka Umma tayi ta shima ta albarka halin Zainab yana birgeta.

            ***     Kiran Sameer ne yau ya tashi Reyhana 8:47am taji 'karar wayarta.

      "Hello". Ta fad'a bayan ta d'aga muryarta a cushe.

       " Morning ". Ya fad'a.

       " Morning ". Ta amsa rai a 'bace.

      " Tun d'azu nake jiran 9 yayi sena kira ki amma  I can't even wait,just want to know how you're doing ". Ya fad'a.

      " Am ok". Ta amsa kamar ta sha'ke shi.

     "Nasreen fah is she awake?" Ya tambaya.

      "Ya Allah". Ta furta a ranta dan ta gaji da amsasa ,magana da safe aiki yake mata haka kurum ma balle da Sameer.

       " Bata tashi ba nima bacci nake". Ta fad'a.

      "Oh am sorry na tashe ki,I just can't wait to hear your voice"

        "Uhmm". Ta fad'a.

        " Ok mayi waya anjima,yanzu ki koma bacci kinji bye". Ya fad'a.

         Ko amsasa batai ba tayi hanging taja tsuka.Baccin ma se ha'kura tayi.

      Tun kafin ta 'karasa sakkowa take jin hayaniyar su  Sageer.            "Ku kuma kun cikawa mutane kunne daga tashi". Ta fad'a bayan ta sakko.

         "Hira muke me dad'i". Cewar Ikram.

         " Ni rufen baki". Ta fad'a tare da nufa kitchen.

     Mommy ta tarar tana had'a breakfast, tama kusa gamawa nan ta taya ta suka gama.

   °Cyprus°          Yau Ahmad ba class saboda haka shida Imran suk a fita zagayawa bayan sunyi breakfast.

        Imran ya takura Ahmad seyayi pic,kusan seyace be ta'ba gani ya tsaya yin pic ba a hanya.

        "Kawai d'aya zakai,haba ko Umma ai ka turawa taga d'an handsome d'inta". Imran ya fad'a yana dariya.

       " Malam rabi dani". Ahmad ya fad'a yana cigaba da da tafiya.

        Imran daya tsaya daga can baya ya 'kwala masa kira.Shi ya zaci ko wani abune ,yana juyawa yaga flashing camera.

        "Wow! Kaganka kuwa". Cewar Imran yana 'karasowa inda yake.

         Ahmad a jikin pic d'in ya zira  hannunsa d'aya a aljihu hakan ya bada style sosai gashi fuskarsa da d'an murmushi (If u want to see the pic comment with yesss let me see who fall for Ahmad😂).

      "Let me know idan kana son pic d'in kai magana na turo ma,if not senai posting a insta kaga baza a rasa masu so ba". Ya fad'a.

      Ahmad jin ya ambaci insta yasa ya ciro wayarsa ya mi'ka masa.

           " Ha! Better ". Imran ya fad'a.

           Sun d'an zazzaga gari tukun suka komo gida.

       Su Ibrahim kuwa dama jiran dawowarsu suke coz suke da kitchen😂

         " Alhamdulillah gashi ya dawo".Ibrahim ya fad'a.

       Shi Ahmad ma ya manta shaf inba yanzu da sukai magana ba.

       "Maza yau mey za'a dafa mana neh?" Idris ya tambaya.

        "Se abinda kuka gani". Ya amsa.

         "Nikam yau d'an wake nake son ci". Cewar Ibrahim.

          " Nikuma sakwara".Idris ya fad'a shima.

         "Nikam dambu". Imran ya fad'a.

         " Kun dad'e baku ci ba".Cewar Ahmad ya watsa musu harara.

        Dukansu dariya sukai daman salan sashi magana ne.

         D'aki ya shiga ya rage jacket d'in daya d'ora kan kayanshi sannan ya fito zuwa kitchen.Seda yai kusan 5min yana tunanin abinda ze girka, idea ya d'auke yau da gobe ta'ki wasa sun gaji da abinda suke dafawa.              Fridge ya bud'e yana kalle items d'in ciki,idea neh ya fad'o masa ya d'akko wayarsa yai searching nan ya gano stew na cous cous                "Butter nut squash and White bean"               Daya duba yaga suna da items da ake bu'kata,ba tare da 'bata lokaci ba ya fara had'awa.

         Kitchen yayi kaca-kaca everything scattered Maza! anyi girki😂

       1hr later table is complete lunch is ready,Imran shi ya fara serving su Idris da 'kamshi ya bigi hancinsu suma suka d'ibi nasu.Ahmad kallonsu ya tsaya yi yana jira yaga ya taste d'in abincin nasa ze kaya.

       Imran spoon d'aya yakai baki yana tattaunawa still bece komai ba,alama Ahmad yayi masa da gira "yaya?"

        "That's yummy! bro"Imran ya furta yana sake d'iban wani loman.

        " Kai dama kasan da wannan kake barinmu da jollof?" Cewar Idris.

       "Wannan anyi mugun mutum". Ibrahim ya fad'a bakinsa cike da abincin.

       Bece komai ba se murmushi kawai dayake shima yaja plate ya ziba.

       Bayan sun gama ya koma d'aki,in less than 2min sega kiran Xynab.

          " Assalamu Alaykum".Tayi sallama.

         "Waalaykumussalam". Ya amsa.

         " Ina yini".Ta gaishesa.

          "Lafiya".ya amsa.

           " Ga Umma zaku gaisa".Ta fad'a.                        "Bari na kira". Ya fad'a tare da hanging.

       Baya so yai exhausting credit nata tunda alhamdullillah ana basu allowances.

         Umma ce tayi picking bayan ya sake kira,nan suka gaisa sun jima suna hira da ita kafin daga bisani sukai sallama.

                 ***

 Zainab  tun chat da sukai rannan basu sake yiba har ta fara zuwa school kuma yanzun an gyara wayar Mommy dan haka bata sake kiransa ba,shima test da yake dashi kwana biyu yasa baya hawa chat.

       Kusan about 2weeks kenan ,Zainab an 'kwame gaban mirror ana tsara d'auri farar fusakarta tasha make up as always bata fiya zama ba janbaki ba se kwalli shima bata fashin sawa ko ba fita zatai ba.

       Zainab itama tana da nata irin kyan most her exciting lips O shape matsakaicin tsaho gareta and ba siririya bace a murje take but not fat whoo! (Don't ask me about her hair fah,idan nace muku Fulani ce you know kawai! 😁)

       Ko breakfast bata tsaya tayi bama,12:30 sun fito daga class a cafeteria suka tsaya it a da friend tata koda taci abinci wayarta ta d'auko ta bud'e whatapp luckily taga Ahmad online wani farinciki ne ya ziyarceta.

Xynab: "Hello"

" Hi".Yayi replying bayan  1min.

Xynab:"Ya school?"

Ahmad:"Alhamdulillah".

Xynab:  " Ni baka tambayi nawa school en ba". Ta tura bayan kamar 3min.

Ahmad:"Ohh ya school? ".

Xynab:" Seda na ro'ka

Ahmad:"Sorry". .

Xynab:" Is OK".

Xynab:"Toh kai wani course make studying?"

Ahmad:"Computer science".

Xynab:" Nyc".

Ahmad:"Where are you now?"

Xynab:"School".

Ahmad:" At school and you are chatting? "

Xynab:"Ai bana class".

Ahmad:" where? "

Xynab:"Guess!"

Ahmad:"Hmm masjid"

Xynab:"No"

Ahmad:"Ok,school compound"

Xynab:"Hhh No"

Ahmad:"Then where?"

Xynab:"So you gave up"

Ahmad:"Uhmm"

Xynab:"Cafeteria".

Ahmad:" Acici"

Xynab:"Am not😞"

Ahmad:"Are you really not?"

Xynab:"Yes"

Ahmad:"I take back my word,Ok for you?"

5min silent batai reply ba,kuma bawai ta fita bane tana so taga ze damu.

Ahmad:"Hello are u there?"

Xynab:"Uhmm"

Ahmad:"I said am sorry "

Xynab:"😝"

Ahmad:"Hmm Xynab"

Xynab:"What??"

Ahmad:"Nothing"

Xynab:"Please say it"

Ahmad"U are acting childish 😁"

     Xynab:  "Am not"

Ahmad:"OK let see,how old are you?"

Xynab:"😯"

Ahmad:"Look at you girl,you think I don't know?"

Xynab:"Yes😕"

Ahmad:"Look at you ,I even..."

Xynab:"Yaya what?"

Ahmad:"Forget about it 🙊"

Xynab:"😱"

Ahmad:"Time up,prayer time"

Xynab:"OK"

Ahmad:"Bye"

Xynab:"✋"

Gaahide ya sauka amma ya kasa dena murmushi,Zainab had seda 'kawarta Siyama tayi tapping d'inta ta dawo daga tunanin data tafi wata duniyar.

       She can't stop blushing yau tayi chat da Yaya conversation d'in ya mata dad'i ."Ashe yana magana haka" Ta fad'a a ranta.

                    ***     Reyhana koyaushe Sameer seya kira baya damuwa zata d'aga ko bazata d'aga ba.

      Sageer daba school yanzu take zuwa ba tinda ya gama  Ikram da ya rage mata 1yr kullum fama take da Sageer wajen kaita school ,Reyhana idan 'yan mutuncinta sun tashi wasu lokutan tana kaita.Yau ma ta shirya Sageer take jira jin shiru yasa Reyhana ta tashi taso shi dan idan Ikram da kanta zata rashin mutunci yake mata.

        Koda ta Shiga ta tatar yana bathroom ,har zata fito ta hangi wani rose flower akan mirror, dan san gulma da sauri ta 'karasa wajen ,rose d'in ta d'auka taga  greeting card daya sha ado cover d'in da heart kala-kala a ajje.

       "Lover boy". Ta furta a fili.

     " Yaya!" Ya kira ta da 'karfi tare da 'karasowa ya wafce rose d'in da card.

     "Iyee wata za'a kaiwa wannan Sageer?" Ta tambaya tana murmushi.

   "Babu". Ya amsa yana turasu a drawer.

" Idan baka fad'a min ba a bakin Abba Yaro".

   "Kai dan Allah waike.."

    "Yanzu de fara fita ka kaita school idan ka dawo mayi maganar lover yaro". Reyhana ta katseshi tare da fita tana dariya.

AR²💖

            *Whooo! how is the page?? Tell me what is about to happen BTW the two two😂 A&Z, S&R ❤*

choose whoaa!

*Pls comment,share and vote.*

Jasko💕                    🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣1⃣

     Zainab yanzu har ta saba ma kanta inde batai chatting da Ahmad ba bata jin dad'i,duk ranar friday kuwa seta kirashi sun gaisa.Umma har ta soma gano wani abun gameda Zainab dan ta tana lura da ita bata da zance sena Yaya Ahmad.

      Har pic d'insa ta saka ya turo mata wai duk sunan Umma ce zata gani dukda kuwa ba haka bane.Tun bata gasgata abinda zuciyarta ta fad'a yanzu ta yarda she fall for him.

                *** Reyhana ce tsaye  hannunta ri'ke da yarinya ,a hankali ya 'karasa inda suke a tsayen.Koda ya isa wajensu ya tarar sun juya masa baya.

        "Reyhana". Ya kira sunanta cikin sanyin murya.

         A hankali ta juya fuskarta cikeda hawaye da nuna alamar damuwa.Kallonsa ya mayar kan yarinya ,a hankali ta waigo sede fuskarta ba komai(Hollow)

   A razane Ahmad ya farka,lokaci guda ya had'a zufa .Agogo ya kalla yaga 2:30am ,jikinsa a sanyaye ya shige bayi ya d'auro alwala ya tada sallah.

        Ko bayan ya idda sallar ya kasa komawa bacci,mafarkin da yayi ne yake ta masa yawo a kansa.

      " Koh wani abun ne ya faru?" Ya tambaya a zuciyarsa.

       "I have to call Reyhana  tomorrow morning".

        Wayarsa ya d'akko ya shiga gallery,photo na Nasreen tana baby ya bud'o yana kalla,hannu ya d'ora kan fuskarta yana shafawa a ransa yana ta sa'ke-sa'ke.Wayar na hannunsa bacci ya saceshi ,kan 'kirjinsa ya kifata ya soma bacci.

         Washegari da safe bayan yayi breakfast ya shige d'aki.Wayarsa ya d'auko ,number d'in Reyhana ya sa a wayar dan numbern ta baze goge a memoryn kansa ba.Da 'kyar ya samu yai dialing sede bata fara shiga ba ya katse.

      Kusan seda ya maimaita haka yafi sau hud'u amma sam baida courage yana tunanin ta ina zai soma magana kuma mey ze fad'a mata? Ya fad'a a ransa.

      Haka ya ha'kura da kiran ya ajje wayar gefe yana mey jin haushin kansa, da ace be d'au tsahon wannan lokacin ba da ba abinda ze hana ya kirata.

      Umma ya kira suka gaisa se sadiq shima dan sun kwana biyu basi waya ba.

               *** Reyhana 'kawarta saudat ta haihu yau ake suna last two years tayi aure.

       Nasreen se tsalle take yau za'a unguwa da ita ta ishi kowa da maganar duk wanda ta gani seta fad'a masa Ummienta zata unguwa da ita dan Reyhana bata fiya fita unguwa da ita ba gara ma Mommy.                 3:30pm ta shirya ,itama Nasreen an shiryata tayi kyau sosai kamar a d'auka a gudu.

       Sallama sukai da Mommy suka fita.Ko barin layinsu batai ba mota ta tsaya yin duniya ta'ki tashi.

       Gashi Sageer baya gida balle ta kirashi ya kaita Mommy kuwa ta dena basu motarta.

      Tana cikin tunanin yadda zatai sega motar Sameer ta doso layin.

       "Shikenan kuma anace yazo". Ta fad'a tare da dukan steering motar.

        Aiko yana ganin motarta ya tsaya,yasan ko ya sauke glass d'in motarsa ba sauke nata zatai ba dan haka ya fito.

      Se da taga yazo daf ta zuge glass d'in.

       "Fita zaki ?" Ya tambayeta.

         Kai ta girgiza masa alamar "Eh".

        " Ok,but amma kamar motarki ya samu matsala koh?"

       "Eh amman zan samu napep". Ta fad'a dan karma yai mata tayi.

       " You don't need that,am here Reyhana senai dropping d'inki wajen da zaki". Ya 'kare maganar da murmushi.

       "No Sameer thanks don't worry zan tafi da kaina". Ta fad'a.

       " Reyhana come on ni nace fah'.Ya fad'a.

        "Sameer..."

          " Please".Ya katseta.

           "Ok". Ta furta.

     Dande ba yacca zatai neh kuma batason missing zuwa shiyasa dole ta ha'kura ze kaita.Baba mey gadi tasa ya kira mata mey gyara kafin ta dawo.

       Se janta da hira yake amma bata wani responding sosai " Eh" ko "A'a" shine abinda take amsasa. Ya rasa gane wace irin mace ita,har yanzu bata chanja ba tana nan da halinta ,sekace yau ta fara ganinsa.

    Rabin hirar ma da Nasreen sukai ,yana kaisu tace ya tafi zata kira Sageer yazo d'aukansu.

      ***

  Zainab yauma taci sa'a Ahmad na online, waje na musamman ta samu ta 'kule 'kuryar d'aki an d'auki pillow an d'ora a cinya ta aza hannunta akai se tapping phone take.

        Xynab: "Yaya an bamu wani assignment naso ace kana nan da ka koya min".

    Ahmad:" Hmm".

    Xynab: .Yaya wai me hmm d'innan take nufi da anyi magana sekace hmm".

    Ahmad: "Sarkin tambaya ".

Xynab: " Eyi ina so na sani".

Ahmad: Haka kike a school? "

Xynab:"Yes 😀"

Ahmad: "Ok, kina nufin kice duk wannan samarin class d'in naku haka kike musu koh"

Xynab: "Laa! 😱 Yaya ni bana kula mazan class d'in mu fa ,ni idan bakai bama ba wanda nake kulawa".

Ahmad:"Hmm".

Xynab: "Ka ganka koh😒"

Ahmad:"Stubborn ".

Xynab:" Naji,yaya saura wata nawa ka dawo?"

Ahmad: "Mey kika tanadar mini?"

Xynab: "I just ask".

Ahmad :"not more than 9"

Xynab: "😱har 9"

Ahmad: "Yayi nisa?"

Xynab: "Sosai,kai bama ka damuwa".

Ahmad:Toh ya zanyi inma na damun?"

Xynab:Umma kam tana kewarka"

Ahmad: Umma kad'ai?"

Xynab:"Uhm.."

   Ahmad :Wannan sister tawa batai missing d'ina ba".

A ranta seda taji ba dad'i ,ita bataso yake ce mata sister gara ya kira ta da sunanta.

Xynab: "I do mana🙈"

Ahmad: "Uhm harda rife ido".

Xynab:"...."

Ahmad: "Mey hakan yake nifi?"

Xynab: "😝😝"

Ahmad: "Kin ganki koh,shiyasa nace maki.."

Xynab: "Kace ni yarinyace koh? Yaya university fa nake kuma wanda yake 17yrs shine za'a kirashi yaro ? nide ba yarinya bace😠"

Ahmad :"Hhh just 17 ,sannu aunty Zainab"

Xynab: "😭😬 kuma an dena chat d'in".

  Kusan 5min bata sake typing ba shima haka,ganin da gaske take dan yaga alamar ta sau'ka seya kira.

      " Hello".Ta fad'a ciki-ciki.

      "Ayya sister sorry am just joking". Ya fad'a.

      Boom! Taji zuciyarta tayi alert ,wani tsantsar sonshi ne ya sake shiga zuciyarta,yanayin yadda yai magana ne yayi mata dad'i  dan bata ta'ba ji yayi irinta ba(Ahmad fa ya manta bada Reyhana yake magana ba😂)

        " Na'ki d'in". Zainab ta fad'a cikeda shagwa'ba.

        "Please". Ya fad'a.

         " Toh a koma chat tukun".Cewar Zainab.

         "No,sekin ha'kura.Ya fad'a.

           "Toh idan na ha'kura baza ka sake cemin yarinya ba?"

         "Bazan 'kara ba". Ya amsa.

           "Toh na ha'kura". Ta fad'a.

           " That's my zee". Ya fad'a shi kanshi besan lokacin ba.

      "Wannan wata irin su'butar baki ce ta sameshi?" Ya fad'a  a ransa.

      Zainab ta kasa sake cewa komai dan ruwan kanta ya 'kone what if shima yanda take ji haka yake ji? Kai amma da tafi kowa jin dad'i.Du ita kad'ai take zancenta a zuciyarta.

       "Zainab are you there?" Ya tambaya.

       "Eh". Ta amsa a hankali.

        " Bacci koh?" Ya tambaya.

          "Uhm". Ta amsa duk da ba baccin take ji ba kawai de over happy yasa wayar ma ba zata iya ba a yanzu.

            " Ok,toh kiyi addu'a ki kwanta". Ahmad ya fad'a.

         "Toh ,seda safe". Ta fad'a.            Shima seda safen yace tukun yayi hanging.Da 'kyar ta iya saita kanta ta kwanta wayarta a gefen kanta tayi bacci dan pic nasa da imran yai masa ta 'kura ma ido tayi ta kalla.

      Yana ajje wayar gefe ya lura da Imran da yai tsaya yana wani murmushin na tarfo ka.

        " Mey kake kai kuma bakai bacci ba?" Ahmad ya tambaya yana wayancewa.

          "Mallam ba abinda zaka 'boyen,na jiyo ka". Imran ya fad'a.

          " Kaji mey? "Ahmad ya tambaya yana nuna be san komai ba.

         " Karka rainan hankali ka gane mey nake nifi,kullum ace sister toh yau 'karyarka ta 'kare".

      "Idan ba sister ta bace taya zance maka haka".

      " Ai shiyasa naji kana kwantar da murya ,ashe kaima ka iya, ko dayake dama ance irin ku.. "

    Be 'kare ba Ahmad ya cilla masa pillow a fuska.Dariya yai tayi sannan yace.

      "Gara ka lalla'bani ka bani labari idan ba haka ba na fallasa magana gun wa'ancen kasan su baza su raga ma ba".

        "Allah Imran ba wasa nake ba ni ba wani abu tsakanina da Zainab kawai na d'auketa a matsayin sister ne". Ahmad ya fad'a fuskarsa ba alamar wasa.

       " Hmm ai daga sister d'in ake zarcewa,kuma ni ai hakan ma dad'i yayi mini kaga du sauran damuwarka na past zaka manta dashi".Imran ya fad'a.

       "Na fad'a maka ni aure ma baya gaba na,koda ace na gama karatu ba aure zan bafa". Ahmad ya fad'a.

      " Kasan kaima hakan baze yiwu ba mahaifiyarka bazata bar hakan ba,akan wata bazaka kashe life d'inka ba".

       "Who knows ma koh ita tayi nata auren,saboda haka kawai ka bawa Zainab dama bakasan irin alkairi dake tattare da ita ba kuma koh a yanzu kasan she is a kind person".

        " Imran please let not talk about this now,bacci nake ji".Ahmad ya fad'a.

      "Ok ,amma kayi tunani". Imran ya fad'a tare da nufar nashi gadon.

      Ahmad sam bawai baccin yake ba kawai de ya kwanta ne ,kalaman Imran sun basa tsoro mussaman maganar " Who knows ma ko tayi nata auren".Abinda ya tsaya masa a rai kenan.

       "What if abinda ya fad'a gaske ne,3yrs zeyi wuya ace bata sake aure ba,but Zainab? toh ita Zainab damage tana da feelings a kaina ne? taya zata so ni? taya zan aureta ma yarinya ce fah? No this is not possible". Da wannan tunanin yayi bacci.

AR²💖

*Please vote, comment and share.Love u all😘*

Jasko💕

          🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣2⃣

      Ahmad tun sanda sukai chat da Zainab be sake hawa online ba yau sati d'aya.Yana so yayi avoiding d'inta yana mey tsoron kar maganar Imran ta tabbata,d'azunma yana ganin kiranta amma ya'ki picking.

       Littafinsa ya d'auko ya soma karatu su Imran sun fita shi kad'ai ne a gidan.Kiran Umma ne ya shigo wayarsa,da farko yayi tunanin koh Zainab ce seya share,se a kira na biyu ya duba yaga Umma.            "Umma ina kwana". Ya gaisheta.

        " Lafiya lau,ya karatu?"Umma ta tambaya.

        "Alhamdulillah". Ya amsa.

         " D'azu muka dawo daga asibiti Zainab bata da lafiya". Umma ta fad'a.

         " Toh! Meya sameta?"Ya tambaya.

         "Malaria neh". Ta amsa.

          " Allah ya sawwa'ke".Ya fad'a.

          "Ameen". Ta amsa sannan sukai sallama.

      " Shiyasa ta kirani ashe,Allah sarki".Ya fad'a a ransa.

     Dialing number d'inta yayi amma batai picking ba kusan 3× dole ya ha'kura a ransa ya ayyana ko fushi tayi tunda taga ya amsa kiran Umma.

      Karatunsa ya cigaba dayi se bayan 1hr tukun ya sake kiranta ,se a karo na biyu ta d'aga.

      "Assalamu Alaykum"

       "Waalaikumussalam". Ta amsa a hankali.

        " Zainab ".Ya kira sunanta.

         " Uhm".Ta amsa a ciki.

          "Ya jiki?" Ya tambaya.

           "Naji sau'ki". Ta amsa.

   Sunfi 2min ba wanda ya sake cewa komai.

       " Am sorry d'azu bana kusa da wayar lokacin da kika kira".Ahmad ya daure ya fad'a.

       "Uhm na gane".Ta fad'a.

        " Kinsha magani?" Ya tambaya yana so ya chanja topic.

      "Eh nasha". Ta amsa.

      " Toh ki daure ki dinga cin abinci kinji".

       "Tahm". Ta fad'a.

       Daga haka sukai sallama,ta ajje wayarta befi 1min ba message ya shigo.

    " Get well soon Sis"

     Lokaci guda ta saki murmushi ,har cikin ranta taji dad'i ya damu da ita.

                 ***      Reyhana ce a d'aki ta ciga tayi fam haushin ya isheta saboda Abba yayi mata zancen Sameer.

      Mahaifiyar Sameer da kanta tazo wajen Mommy sukai maganar Reyhana Mommy kuma ta fad'a wa Abba abinda yake faruwa.

     Tana cikin wannan yanayin Walida ta shigo take fad'a mata Sameer yazo.

      "Kije kice ganinan".Reyhana ta fad'a.           Mayafi ta d'auka ta yafa sannan ta fita.

      A falo ta tarar dashi shi kad'ai ko Nasreen bata nan,zama tayi opposite dashi.

       Bayan sun gaisa Sameer ya fara magana"Uh..Reyhana bakya ganin it's the right time?".

      " Right time for what?" Ta tambaya.

        "To give me chance, Reyhana baza kice bakisan abinda ke raina ba   duk iya tsahon shekarunnan ,at first nayi losing and now ga second chance na sake samu i don't want to miss it you know ,I so much care about your life,  everything yours you are always in my mind ,my love for you  will never vanish from my heart you are the only one i ever loved,  you are my first love and no woman can ever take your place in my heart, yet I never find someone like you  ,Reyhana you are different from others, you are unique, if am to stay here for years I can't stop describing how i valued you and the love that I have for you,Reyhana please consider".

       Reyhana sam kalamansa beyi tasiri a zuciyarta ba dan be hanata fad'a masa;" Sameer,a yanzu inaso na koma karatu and i need to wait for Nasreen to start schooling".

       "Kina nufin kice se ta fara makaranta and se kin kammala masters right?"

      "Yes". Ta amsa.

        Jira take taga mey zece ,zuciyarta tana fad'a mata " Shikenan kin kawo 'karshen abin,Sameer baze iya jira har wannan lokacin ba".

       D'an guntun murmushi yayi kafin yace"Reyhana how many times do i have to tell you i am always your supporter I promise to be by your side always and forever, wannan ba wani matsala bace I promise to wait for you no matter how long it wiil take us".

         "Sameer taya zaka jirani har wannan lokacin b..." Bata 'kare ba ya  katseta.

      "I promised Reyhana".

       Shiru tayi bata sake cewa komai ba ,shigowar Nasreen  tasa basu cigaba da magana ba.'Karasowa tayi wajen ummienta tana mata hira,daga baya ta koma gun Sameer.

            °•° >3 years Later <°•°

   " Nasreen!" Reyhana ta kwala mata kira tana daga d'aki.

         Seda ta kwashi minti kusan 5 ta shigo d'akin,tana manne daga jikin 'kofa ta 'ki 'karasowa se zazzare ido take cikeda tsoro.

       "Zonan!" Ta kira ta tsawace.

          "Ummie dan Allah karki dakeni". Ta fad'a cikin rawar murya.

           " Ayyo! Watoh kinsan mey kikai? Zonan nace".Reyhana ta fad'a tana mata nuni da yatsa.

     A hankali ta 'karaso gurin kanta a sunkuye.

      Rigar uniform d'inta ta makaranta ta d'auko ta nuna mata.

       "Waya yanka wannan?" Ta tambayeta.

        Shiru tayi bata amsa ba yanzun ta d'ago kanta.

       "Ba magana nake ba?"

        "Ummie kiyi ha'kuri na dena". Ta fad'a kamar zatai kuka.

        Reyhana da hanzari ta tashi tana shirin fizgota sega Abba ya shigo d'akin.

     Da gudu taje ta ma'kale a jikin Abba.

      " Toh meya faru kuma?" Ya tamabaya yana d'ago kanta.

     "Dukana ummie zatai".Ta amsa.

     " Ya da haka?" Cewar Abba yana kallon Reyhana.          "Abba rigar makarantarta ta yaga saboda karta je gobe".Ta amsa tana nuna masa.

       "Ayi mata afuwa yanzu bazata 'karaba ,uniform d'in ba biyu bane?" Abba ya tambaya.

    Se lokacin ta tuna biyu ne da idonta ya rife,Nasreen jin ance biyu ta tur'bina fuska dan bata son zuwa makaranta.

      "Ungo chocolates d'inki". Abba ya fad'a tare da mi'ka mata nylon dake hannunsa.

     Tsalle ta shiga yi tazo wajen Reyhana tana nuna mata.

     " Toh nagani seki ce kin gode".Ta fad'a.

      "Abba thank you". Ta fad'a.

       " Yawwa 'yar baturiya".Abba ya fad'a.

      Tare suka sauka 'kasa da Abba ta ruga a guje  wajen su Walida tana nuna musu.

         Walida da anzama 'yan mata da ace dane da seta ce ta bata, yanzu kuwa kau da kanta tayi ta cigaba da abinda take.

       A shekaru ukunnan abubuwa da dama sun gudana.Reyhana ta kammala masters d'inta,Nasreen kuwa an sata makaranta 2yrs da suka wuce yanzu tana nursery 2 koyaushe fama ake da ita wajen shiryawa school.

      Sageer tuntuni ya fara aiki a asibiti as medical laboratory technician ya zama busy ba kasafai suke ganinshi a gida ba se dare.

       Ikram ma ta zama cikakkiyar journalist tana zuwa aikinta itama,se Bassam da saura shekara d'aya ya rage ya kammala degree d'insa,Walida wannan shekarar tayi graduating yanzu admission take jira.

       Sameer kuwa ya koma America amma yana zuwa jefi-jefi kuma wani sa'in suna waya da Reyhana.

       Mommy se kallo dan wani lokacin idan ta gansu full house setaga kamar ba ita ta haifesu ba ,kowa ya girma.

                   *** Ahmad°•°

        Shigowarshi gida kenan daga gidansu Sadiq yake bayan ya dawo daga aiki ya biya se yanzu ya shigo gida,6:02pm.

        D'akinsa ya shiga ya watsa ruwa tukun ya fito cikin 'kananan kaya blue jean da ba'kin T-shirt.

    A falo ya iske Umma,cikin girmamawa ya gaisheta.

      "Yaushe ka shigo banjiba?" Ta tambaya.

       "Ba jimawa". Ya amsa.

        " Toh abinci fah".Ta tambaya.

       "A'a na 'koshi". Ya amsa.

        " Nikam gajiya akai da abincin nawa yau kusan kwana uku ba a ci".Umma ta fad'a.

        "No kawai bana jin yunwa neh fa anjima zanci". Ya fad'a da murmushi kad'an a fuskarsa.

     "Toh ai shikenan". Ta fad'a.

       Remote  dake kan center carpet ya d'auka ya chanja channel daga Arewa24 zuwa MBC Action.

         " Aikin kenan ,wannan masu damben koh me za'a kalla anan oho". Umma ta fad'a.

       Ahmad kuwa murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba ya cigaba da kallonsa.

       1 year kenan da fara aikinsa ,mahaifin Zainab shi ya taimaka masa ya samu aiki a NGOs(Non-governmental organizations).

     Komai ya sauya tun sanda ya samu aiki,Ya gyara musu gidansu ya koma kamar sabo ba abinda Umma ta rasa a yanzu inde na bu'katar alatu da sauran wani jin dad'i although rayuwa ba koyaushe ake cikin jin dad'i ba no matter how billionaire you are.

       A yanzu haka yana da farmland na noman shinkafa kuma cikin ikon Allah yana samun profit kuma wannan shawarar Umma ce ta sashi yin noman shinkafar.

      Zainab tana zaria, ta kwashe 2weeks a can amma nan da kwana biyu zata dawo tunda wannan week d'in aka koma school.

      Zainab ba abinda ya chanja a cikin ranta gameda son da take wa Ahmad sede har yanzu bata fito tace tana sonsa ba.

     Tun sanda ya dawo gida Nigeria Umma tayi ta tirsasashi yaje gidansu Reyhana amma kullum seya ce mata ba yanzu ba,daya gaji da tunatar dashi da take seyai 'karya yace yaje,idan ta tambayeshi ya sake zuwa seyace mata "Eh" akan haka ya barta.

     Daga yayi attempting zuwa seya fasa, baida kalaman daze fad'a mata(A tunaninsa) from bad to worse da ana maganar 4yrs yanzu 6yrs be saka 'yarsa a ido ba,shikanshi idan ya tuna yana jin haushin kansa.

                    ***

     Reyhana kuwa a zuciyarta tana 'ko'karin mantawa da Ahmad amma kamannin da Nasreen ta d'auko na Ahmad yasa bazata mance da fuskarsa ba,ita tama fidda ran sake ganinsa a rayuwarta.

      9pm lokacin baccin Nasreen,seda tayi addu'a kamar koyaushe Reyhana tana karanta mata ita kuma tana repeating.

     Seda ta tabbata tayi nisa da bacci tukun ta komo falo,duk yaran gidan suna falon amma banda Sageer.Kusan kwana biyu haka yake seya 'ki fito ba kamar da ba dayake fito a d'an yi hira kafin su kwanta.

     "Walida Sageer be dawo bane?" Reyhana ta tambaya.

    "Ya dawo yana d'aki". Ta amsa.

     " Yaci abinci?" Ta sake tambaya.

     "Beci ba ,Yaya Ikram ma tana masa magana yayi banza da ita ya wuce d'akinta".Cewar Walida murya 'kasa-'kasa.

        Kai kawai ta kad'a ta zauna kan kujera.

       AR²💖

       Comment,vote and share.Luv u all💋

Jasko💕

      

    

            

       

    

             🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣3⃣   

Washegari da safe around 8:15am kowa ya hallara a dining seat d'in Walida ne kad'ai empty se Nasreen da tun d'azu driver ya kaita makaranta.

   

"Walida bata tashi bane?" Abba ya tambaya.

"Ta tashi". Ikram ta amsa.

" Toh mey take baza ta fito ba?" Mommy ta fad'a.

"Ikram kije ki kirata". Cewar Mommy.

" Mommy nafa makara is almost 8:30am".Ikram ta fad'a.

"Bari na kirata". Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa.

Murya taji 'kasa-'kasa lokacin da ta shiga d'akin,blanket taga alaman Walida ta rufe kanta dashi.

" My Prince ka daure kasha magani idan ba haka ba kanka ze cigaba da ciwone kaji".

Baki Reyhana ta saki jin muryar Walida tana waya.'Karasawa gadon tayi ta cukuikui blanket d'in ta yaye ta.

       Cikin razana Walida ta mi'ke zaune ,wayar ma tayi cilli gefe da ita,a zatonta Mommy ce.Ganin Reyhana ce yasa ta d'an ji relief tasan komai zezo da sau'ki             "Iyye abinda kikeyi kenan?" Reyhana ta fad'a.

     Walida a sukwane ta d'auki wayar tayi hanging sannan ta dawo da kallonta wajen Reyhana.

       "Da 'kawata fa nake waya". Walida ta fad'a.

        " Shiyasa naji kina cewa My Prince ko? Ke bazaki nutsu ba koh ? Shikenan zan fad'a wa Abba kinga se ya aurar dake kowa ya huta naga alamar aure kike so".

       "Yaya dan Allah kiyi ha'kuri bazan 'kara ba". Walida ta fad'a.

       "Waye wannan d'in?" Reyhana ta tambaya.

        "Waseem". Ta amsa tana sosa kai.

         " A ina yake?"                    "Uhm..uhh d'an school d'inmu". Ta amsa a kunyace.

          " Class mate d'inki?,'karya yake miki wannan iyayensa ba aure zasi masa yanzu ba har nawa yake,just wannan year d'in fa kukai graduating kuma shine kike kulashi sakarya ,duk sanda na sake gani kina waya dashi sena fad'a wa Abba ya miki auren dole".

       Shiru tayi kanta a sunkuye ta'ki cewa 'kus.

     "Tashi ki wuce ki breakfast". Ta fad'a tare da ficewa.

      Bayanta tabi suka sauka 'kasa lokacin har Ikram ta tafi aiki.Muzurai tayi tayi kar Reyhana ta fad'a wa Mommy.

            ***

     Ahmad yau ko breakfast beyi ba ya fice a motarsa marcedes mey black color, yana hanya sega kiran Zainab.

        " Yaya ina kwana". Ta gaisheshi.

         "Lafiya lau". Ya amsa.

          " Umma tace gobe zaki dawo koh?"

           "Eh".Ta amsa.

            " Ok toh Allah ya kaimu".Ya fad'a ta amsa da Ameen ,daga haka sukai sallama ba tare da sunyi doguwar hira ba.

°°°

   3pm Reyhana da Mommy suna zaune a falo kamar daga sama suka ji an turo 'kofa da 'karfi.

     Sageer suka gani da sauri ya wuce d'akinsa ko ta kansu bebi ba.

      "Mommy wai Sageer lafiyarsa lau kwana biyu?"Cewar Reyhana.

       " Atoh gashinan de kullum cikin 'kunci da fushi".Mommy ta fad'a.

       "Bari naje".Reyhana ta fad'a tare da mi'kewa ta nufi d'akinsa.

         A bud'e ta tarar da 'kofa saboda haka sallama tayi ta shiga.

       A kwance ta iskeci yayi rigingine hannunsa akan goshinsa ya 'kura wa ceiling ido ko takalmin dake 'kafarsa be cire ba.

       " Sageer meyake faruwane wai?"Reyhana ta tambaya.

        Se lokacin ya kula ma tana d'akin.

       "Babu". Ya fad'a ciki-ciki.

        " Amma na ganka haka".

        "Kawai na gaji ne". Ya fad'a.

        " Nifa ba wacce zaka 'boyewa abu bace, meye amfanin 'yan uwa idan bazasu san matsalar ka ba su taimaka maka kayi solving ba?"

      Mi'kewa yayi zaune fuskarsa damuwa 'karara ta banyana.

      "Wannan abun ba abune wanda zaku iya taimaka min ba kuma ina ganin ma na makara". Ya fad'a.

       " Koda addu'a ai mu masu taimaka maka ne,tell me meyake faruwa".Reyhana ta fad'a tare da 'karasowa inda yake.

        Wayarsa kawai ya d'auko ya bud'o wani pic na mace 'yar budurwace kyakkyawa a kai.

      "Fatima". Ya fad'a.

      " Fatima? Itace damuwarka koh?"

      "Ummien Nasreen Allah bazan iya rayuwa ba ita ba,I can't bear to loss her,suna nema su rabani da ita".

       " Suwaye?" Ta tambaya cikin nuna damuwa.

       "Iyayenta ,sune zasu aura mata cousin d'inta".Ya 'kare maganar kamar zeyi kuka.

       Reyhana tausayin 'kanin nata ne ya kamata lokaci guda kuma ta tuno rabuwarsu da Ahmad.

      " Komai zezo da sau'ki Sageer,zan taya ka da addu'a  kaima ka dinga yi".Ta fad'a.

       Kai ya gid'a almar "Toh" tare da fad'in "Amma karki fad'awa Mommy".

      " Don't worry bazata sani ba".

             "Thank you". Ya fad'a.

     Murmushi ta 'kalo tace " Is okay".

             ***

    Ahmad yana komawa gida ya tarar da Imran yazo,Umma tana fita daga falon Imran ya tinti'beshi.

       "Ya ake ciki har yanzu baka Jeba?"

      "Uhm". Ya amsa.

      " Ina baka shawara ka gaggauta zuwa kar kazo kayi da kasani,this is too much 6yrs ba wasa bane Ahmad ya kamata ka gane".

      "Ni kaina nasani Imran tunanin yadda Reyhana zata yarda da abunda zance mata nake"Ahmad ya fad'a.

      " Malam ka cire wannan abun  a ranka,ta yarda karta yarda Nasreen is your daughter ba yadda zasi ,dan haka gara ma ka mi'ke ba wajensu zaka ba 'yarka kaje gani".

      Sosai maganar Imran ta shigeshi,yaji 'karfin gwiwa a yanzu ya shirya zuwa gidansu Reyhana.

          Da daddare Umma take fad'a masa gobe ze d'akko Zainab daga tasha.

      Beso kasancewar hakan ba saboda lissafinsa ze ruguje na zuwa gidansu Reyhana.

°°°       2days later

       Daga aiki koh gida be komo ba Ahmad direct ya wuce gidansu Reyhana around 5pm lokacin.

     Daga can nesa yai parking a zuciyarsa yana sa'ke-sa'ke iri -iri ,ya shafe kusan 30hrs be fito ba se shawarwari yake,gashi bega ko mutum d'aya na gidan ba a waje.

        Ya dafa hannunsa a steering ya maida kallonsa gate d'in gidan ,mota ya gani ta sauke yara guda uku ta juya.

       Biyu daga cikinsu mace da namiji d'ayar kuwa Nasreen ce suna sanye da uniform na Tahfiz.

      Guda biyun gidan dake gefensu Reyhana suka shiga ita kuwa Nasreen bye tayi musu da hannu tsayawa tai gate ta hau kan wani tudu se cisgo flowers da suka shingid'o ta bango take.

     Sam ya kasa bawa kansa amsar abinda zuciyarsa ke tambaya."Is she Nasreen? My daughter ?"

      Baro 'kofar gidan tayi tana nufowa inda motarsa take,daya kalli direction da takeyi ya kula ashe ita mage ta biyo takeson d'auka.

     A sanyaye ya fito daga motar ya bita da kallo magen ta gudan mata ,komowa tayi zata shige inda yake ya tsayar da ita.

       "'Yar yarinya". Ya kira ta.

       Waiwayowa tayi ta kalleshi" Ni gida zan tafi ummiena ta hanani magana da wasu a waje".Ta fad'a.

      "Eh yanzu ai zan tafi,amma ya sunanki?" Ya tambayeta.

      "Nasreen, Aisha Ahmad Yusuf". Ta amsa.

      Amsar data bashi ya isheshi tabbatar da abinda yake tunani.

     Ma'kwat! Ya had'iyi yawun daya tokare a ma'kgoronshi.

       " Kaji kunya 'yarka bata sanka ba".Zuciyarsa ta fad'a.

      Daurewa yayi yace" Ni sunana Uncle".

     "Uncle ? Koya min karatu zaka yi?" Ta tambaya.

     Fuskarsa d'auke da murmushi yace "Eh".

      " A nan?" Ta sake tambaya.

       "A'a ,ya sunan school d'inku?"

       Amsa masa tayi sannan tace"Ummiena zata jamin kunne idan ban koma ba".

      "Eh kije gida yanzu". Ya fad'a.

      Da sauri ta wuce ta shiga gidan yana tsaye har ta shige tukun ya koma mota ya tafi.

      Nasreen kuwa tana shiga gida ta soma bada labari taga wani sunansa Uncle.

      " Ban hanaki yiwa mutanen waje magana ba?" Cewar Reyhana.

     "Shine ya fara yimin magana wai ze koyan karatu".

     " Toh karki sake kinji koh".Reyhana ta fad'a.

      "Toh ummie". Nasreen ta fad'a tana cire hijabi.

     Reyhana tunani ta shigayi wannan waye?

AR²💖

Comment,vote and share.love u all💋

Jasko💕        

                   

                🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣4⃣

      Lokacin da ya dawo gida su Umma na falo yana jiyo su ita da Zainab,d'akinsa ya shiga ya zauna yana ta tunano Nasreen.

      Se yanzu ya sake gane rashin kyautawar da yayi na rashin bata kulawar da ta wajaba a kansa.

  °°° Se wajen maghrib daya fito zeje masjid Zainab ta ganshi.

     "Laa dama ka dawo gida".

      " Eh ai ban jima da dawowar ba". Ya amsa.

      "Masallaci zaka?" Ta tambaya.

      "Uhm". Ya amsa.

      " Toh seka dawo". Ta fad'a.

          Zainab bayan fitarsa ta shiga kitchen had'a abincin dare.

                   ***   Reyhana tana d'aki hankalinta ya d'aga Sameer yazo Nigeria d'azu ya kirata ya fad'a mata.Yanzu bata da 'karyar da zata fad'a masa,bama shi kad'ai ba har Abba.Nasreen tuni tayi bacci ita kad'ai se juyi take ta kasa bacci tunani ya isheta.

       Saudat ce abokiyar shawara yanzu kuma dare yayi sede gobe,abunda ya fad'o mata a rai kenan.Dakyar ta samu ta iya yin bacci.

                     ***       Washegari da safe bayan ya gama shirinsa ya fito falo ,Zainab ya tarar tayi shirin school da alama ma shi take jira.Shi ya mance ma da kaita school se yanzu ya tina.

       "Ina kwana yaya". Ta gaisheshi.

        " Lafiya lau". Ya amsa.

     'Kokari yayi ya kauda idonsa daga kallonta dan kwalliyarta tana masa 'kwarjini,sosai tayi mugun kyau.Doguwar riga blue tasa se rolling datai golden d'in mayafi ta sa'kala jakarta golden fuskarta tasha kwalliya ga maroon lipstick daya haskata.

      "Ka shiryo kenan".Umma ta fad'a sanda ta shigo falon.

        " Eh d'azu na shigo mu gaisa kuma kin koma bacci,ina kwana". Ya gaisheta.

       "Lafiya lau,bazaka karya ba?" Ta tambaya.

        "Eh se anjima". Ya amsa.

         " Toh sekun dawo"Ta fad'a.

          Yana ficewa tabi bayansa,a cikin ranta tana jin dad'i musamman da taga sunyi ango shi yasa blue d'in shadda.

        Cikin 'kan'kanin lokaci ya kaita kafin ta fita daga motar ya 'kara mata kud'in makaranta dukda ana bata daga gidansu.

•••

Yauma daga aiki be koma gida ba seya je school d'insu Nasreen,4pm lokacin yana tsaya a gate d'in yana tunanin yadda ze ganta.

      Da'kyar mey gadi ya barshi ya shiga wani daga cikin malamanne ya kira Nasreen tazo.

      "Kinsan wannan?" Suka tambayeta.

      Seda ta tsaya na d'an lokaci tukun tace "Eh".

      Wata daga cikin malaman tace " Ai gashi ma kamar su d'aya".

     Dama sun fito sallah basu koma ba dan haka ya kamo hannunta suka zauna daga wani bench a compound d'in makarantar.Ita de Nasreen tana jin d'ar-d'ar musamman idan ta tuna abinda Ummienta tace.

        "Nide ummiena ta hanani kula mutanen waje".Ta fad'a.

        " Kinmanta ni Uncle ne? Na kawo maki wannan ".Ya ciro mata Twix guda biyu daga aljihunsa.

        Aiko da sauri ta mi'ka hannu ta kar'be" Amma karka fad'a wa Ummiena kaji".Ta fad'a harda zaro ido.

       "Toh". Ya amsa tare da kad'a kai.

        "Karatu zaka koyamini wai?" Ta tambaya tana 'bare ledar.

        "Eh amma yanzu zaku shiga aji se anjima idan kun tashi ina waje ina jira".

        " Kai zaka kaini gida?"Ta tambaya.

        "A'a".

        " Dan Allah ka kaini gida  ,kullum kullum semun dad'e ake zuwa d'aukan mu".

       "Ai zanyi hira daku kafin a zo d'aukanku".

        Kai ta kad'a tana cigaba da shan chocolate d'inta.Ba jimawa ta koma aji,kamar yadda ya fad'a seda ya jira aka tashesu.

       Tana fitowa ta ganshi a bakin gate da gudu ta 'karasa inda yake taji dad'i ganin ya jira an tashesun kamar yadda ya fad'a mata.

     Kan mota tasa ya d'orata suma sauran yaran ma'kotan nasu haka kafin driver yazo.

    Littafinta ta bud'o se nuna masa H/W d'inta take da C/W,kusan seda suka 'kara 15min driver yazo da sauri yaran suka je,Nasreen ce 'karshe sam drivern be kula bama ya jasu suka tafi ita kuwa se waving bye take wa Ahmad.

       Ya kasa dena murmushi har ya isa gida,ya ji dad'in yadda Nasreen ta sake jiki dashi dama hakan yake so.

       Yana shiga gida be jima ba ya fito waje ,Zainab ya gani tana tahowa se sauri-sauri take daga gefenta kuwa wani saurayine da alama magana yake mata amma ta'ki sauraronsa.

      Har 'kofar gida yana biye da ita ,se a lokacin Zainab ta kula da Ahmad dake tsaye .Shikuwa yiyai kamar be gansu ba dan kauda kansa yayi gefe kamar besan da mutum a gurin ba.

       "Assalamu Alaykum". Yaji anyi masa sallama.

     Se lokacin ya lura Zainab har ta shige gida.

      Hannu ya mi'ka masa suka gaisa,ita kuwa Zainab data shiga gida wuf ta shige d'aki ko Umma bata ji sallamarta ba.

       Tana cikin sa'ke-sa'kenta a d'aki taji shigowar Ahmad, kunya taji ta lullu'beta tana jiyo muryarsa yana magana da Umma gudun karya fad'awa Umma yasa tayi sauri ta fito.

       " Zainab dama kin dawo?"Umma ta tambaya.

       "Eh yanzu ban jima ba ". Ta amsa.

      Tana had'a ido da Ahmad taga yayi mata murmushi ko ba'a fad'a ba tasan ma'anar murmushin,a take ta sauke kanta katsa.

       Umma ce ta koma d'aki tabarsu a tsaye gun,Zainab ma da sauri zata juya ya tsaida ita da fad'in.

     " An bani sa'ko".

      "Yaya sa'ko kuma?" Ta tambaya.

       "Eh ba'konki na waje shi yace na fad'a miki".

        " Mey?" Ta tambaya tana had'e gira.

        "Wai yana sonki". Ya amsa.

         Bata sake cewa komai ba ta koma d'aki ,kafin ya sake wata maganar yaga ta bace masa dan haka ya koma d'akinsa.

     A d'aki tunani ta shiga yi shin wace amsa Ahmad ya bashi? Ko zeji haushi? wata zuciyarce tace mata" Be damu ba".

      Jitai ba dad'i dan batai tsammanin haka ba,a tunaninta ze nuna kishi a fuskarsa sede taga ba hakan ba harda ma yimata murmushi.

  •••

    Koyaushe Ahmad inde ya dawo daga aiki seya biya school d'insu Nasreen, ta saba dashi sosai har home work yake koya mata idan taje gida ta fad'a musu se sike tunanin ko Uncle na school ne.

     Ta 'bangaren Sageer kuwa abu kullum gaba yake ko abinci yanzu be fiya ci ba a d'aki yake zama ya'ki fitowa ga wani mugun rama da yayi Mommy tun abun baya damunta yanzu ya soma ,kuma tambayar duniya baze fad'a mata ba Reyhana ma ta'ki fad'ar abinda ke damunsa.          Reyhana kuwa data yiwa Saudat magana akan Sameer shawara ta bata akan ta cigaba da addu'a.

      Yau wasu 'kannen Umma  banda mahaifiyar Zainab suka zo daga Zaria,sanda suka zo Ahmad baya nan se Zainab yau bata da lectures.

      Tunda take da Ahmad basi ta'ba maganar Reyhana ko Nasreen da ita ba,yau tana jinsu Sister's d'in Umma suna hirar zasi je gidansu Reyhana suga Nasreen.

     Tana daga d'aki amma kunnanta yana kwashewa,ita jitai tsoro ya shigeta kada ace fa Ahmad ya dawo da Reyhana.

       Umma tana kallo suka fita wajen 4pm,hadda yi mata siyayyar kayan biscuit.

     Sanda suka shiga Walida suka tarar a falo, ita taje ta fad'awa Mommy da tana d'akinta Anty Asma'u tazo.

       Da farko Mommy bata gane su ba seda sukai bayani.Anty Asma'u tasa Walida ta kira da tana d'akin Mommy.

                    °°°         Ahmad daga aiki ya wuce wajen Nasreen ,yana zuwa aka tashesu.Kamar koyaushe tana ganinsa ta ruga da gudu ta d'ale shi.

      "Uncle ina chocolate d'ina?"

       "Gata".Ya d'akko a aljihunsa.

        Tana tsalle ta kar'be suma sauran abokan tafiyarta ya basu nasu.

°°°   Reyhana datai waya da driver yake fad'a mata yana kwance baida lafiya dan haka daga gidan Saudat tayi makarantarsu Nasreen.

       Daga gefen gate tai parking ta fito ,'yan tsirarin student dake wajen ta kalla ko zata ga Nasreen.

       Daga can nesa ta hango Nasreen d'are-d'are a kan mota.Mutum taga tsaye a kusada Nasreen amma kuma ya juya baya.

     'Karasawa tayi har inda suke,seda ta 'karasa kusa tukun Nasreen ta ganta.

      " Ummie!!!"Ta kira sunanta da 'karfi.

      Ahmad daya ji ta 'kwala kira ta ambaci Ummie hakan ya tabbatar masa Reyhana ce.Cak ya tsaya ya kasa motsi balle juyowa.

     Da gudu ta 'karaso inda Reyhana take ta rungumeta.

     "Yau da kanki kika zo d'aukanmu?" Ta tambaya.

     "Eh". Reyhana ta amsa.

     " Ummie kinga Uncle".Nasreen ta fad'a tana nuna inda yake.

       Se lokacin Reyhana ta dawo da kallonta kansa.

      "Uncle kaga Ummiena". Nasreen ta fad'a.

      Ya rasa mey zeyi ,wata zuciyar tana cewa kar ya waigo ? "Toh idan ma be waigo ba ya zeyi baida choice dole ta ganshi".Ya fad'a.

     A sanyaye ya juyo idanunsa suka sauka kan Reyhana, wani irin blinking ido tayi tana so ta tantance gaske ko mafarki.

       Suman tsaye tayi ta kasa ko motsi ganin ba mafarki take ba,duk cikinsu kowa ya kasa magana kuma basu dena kallon juna ba...

AR²💖

           Shocked right?? Comment Vote Share   Jasko💕   

          🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣5⃣

   Duk cikinsu kowa ya kasa fad'ar koda 'a' ce ,daga cikin zuciyarsu kuwa tambayoyine iri-iri musamman Reyhana.

     Kamar 'kiftawar ido yaga taja hannun Nasreen sun shige mota,'ki'kam yayi be motsa ko ina ba kamar wani gunki.            Nasreen cikin rashin nuna damuwa tayi ta waving bye ,cikin 'kan'kanin lokaci yaga wayam.Se a lokacin yayi 'kwa'kwarar 'kifta ido.

     "Meyasa ma na barta ta tafi?" Ya fad'a  a ransa.

      "Am stupid!" Ya daki saman motar.

       Gwiwa  ba 'kwari ya shige mota sannan ya bar gurin

       Reyhana da ikon Allah ta iya tu'kin motar dan hankalinta baya wajen,Nasreen da take mata hira ko sauraronta bayi take ba.Suna shiga gida taga Anty Asma'u da Mommy se maganganu suke suna kumfar baki.            "Banda rainin hankali kai tsaye su sunzo ganin 'yarsu  bako tunani". Cewar Anty Asma'u.

         "Nasreen jeki d'aki gani ina zuwa". Reyhana ta fad'a da'kyar dan bakinta yayi nauyi.

      Ba musu ta wuce sama,su Mommy kuma lokacin sun bar hayaniyar da suke." Mommy meya faru?" Reyhana ta tambaya.

     "Yanzunnan 'yan uwan Ahmad suka fita ,saboda tsabar rashin kunya irin tasu wai gurin Nasreen suka zo harda wani tarkacen ledarsu sunan sunyo mata abin arzi'ki ca akai musu bata ci kowa irinsu neh mitsiyaci!"

    "Kuyi shekara shida baku waiwayi yarinya ba shine seyau ku kwaso tarikican 'kafarku kuce kunzo ganin yarinya". Anty Asma'u ta fad'a.

      Reyhana ta kasa cewa komai illa zame jiki datai ta haye sama dan kanta yana shirin bugawa ta rasa da wanne zata ji,ganin Ahmad koh zuwan wa'acen?

       Da'kyar 'kafafuwanta suka kaita zuwa d'akinta,a sanyaye ta zauna kan gadon Nasreen da har ta 'kwa'be uniform d'inta ,'karasowa tayi inda Reyhana take.

    " Ummie ki d'akko min kayan da zan saka".

     Sam hankalinta bayan gurun ta tafi nisan tunanin seda taji tana jijjiga mata kafad'a ta dawo hankalinta.

      "Ina zuwa ".Ta fad'a tare da mi'kewa ta bud'e wardrobe ta ciro mata.Nasreen tana gama sa kayan ta fita.

     "Shine Uncle da take magana? Meyasa se yanzu? may be aure yayi ya haifi wasu 'ya'yan shine ya tuna da Nasreen koh matarsa tasa yazo wajen 'yarsa ? Naughty brain nashi be fad'a masa abinda ya kamata ba seda.. No it can't be..what if yayi auren ai it's possible but...Ohh " Abinda yake ta mata yawa a 'kwakwalwarta kenan ,se yanzu kuma abunda su Mommy suka fad'a mata ya dawo mata.

°°°

Ahmad yana zuwa gida ya shige d'akinsa ya rufo 'kofa ,se yanzu yake daya sani.Tunani ya shiga yi koh ya kira ta a waya wata zuciyar tace"Kana gani koh magana bata had'aku ba a fili ma kenan balle waya".

     "Reyhana am sorry!" Ya fad'a a fili cikeda nadama kamar tana kusa dashi.

      Yana wannan tunane-tunanen har maghrib tayi be samu zuwa masjid bama se a gida yayi sallahr,se bayan ya idar da sallah tukun ya fita zuwa parlor.

         Umma tana zaune kujera fuskarta ba walwala shi be kawo komai a ransa bama,opposite da kujerarta ya zauna.

       Tunda ta amsa sallamarsa bata sake magana ba se yanzu.

       "Ahmad meyasa kayi min 'karya?" Ta tambaya.

       A razane ya d'ago da kai ya kalli Umma se lokacin ya kula da yanayinta.

     "Abinda kayi ka kyauta kenan? Ashe duk zaman da akai iya tsahon lokacinnan kusan shekara biyu kenan ni gani ka maida ni bansan mey nake ba koh? Ka janyo wa iyayenka wula'kanci da cin mutunci yanzu wa gari ya waya?" Se lokacin ta tsaya da magana.

      Yanzunne ya gane mey ya faru,Aunty's nashi sunje gidansu ,finally Mommy ta fad'a musu 6yrs rabonsa daya taka 'kafa gidansu Reyhana.

       "Ya Allah ka taimakeni". Ya fad'a a zuciyarsa.

    Ya bud'e baki zeyi magana Umma ta katseshi.

      "Ina tunaninka da iliminka ? Ha'k'kin 'yarka dayake a kanka duk ka mance ba ruwanka haka kake kuma jin dad'in bacci ni gani ka d'auke ni shashasha ashe kallon wawiya wacce batasan abinda take ba kake min ban isa na fad'a maka abinda zakai ba kai, gaka ka girma ka zama banban mutum koh? mahaifiyarka za kaiwa 'karya".

       Umma a rayuwarta ba abinda ta tsana kamar ai mata 'karya,gata da mita kuma idan tayi fushi se ansha wuya ake shawo kanta.

     Duk wannan fad'an da tai masa Zainab tana daga d',aki tana jiyowa ,ji take kamar ita akai wa fad'an sosai tausayin Ahmad ya kamata.

      Yana so ya bata ha'kuri amma ga mamakinsa se gani yayi ta tashi ta bar masa parlorn.

     Jiyai duniyar tayi masa zafi ya rasa inda zesa kansa, tashi yayi ya fita daga d'akin yana jiyo sanda ta banko 'kofar d'akinta,d'akinsa ya koma ya rasa mafita yunwar dayake jima ya dena ,wayarsa ya d'auka ya kira Imran ya fad'a masa duk yanda ake ciki ,nan yake fad'a masa gobe zezo suyi magana.

                ***

     Mommy tana ganin Abba ya dawo ta fad'a masa abinda ya faru ,a gaban idonta seya nuna mata bega laifinsu ba amma a ransa ba haka bane.

     Yau dinner d'in boring dan daga Reyhana har  Sageer ba wanda ya hallara ba, Mommy ma haka d'aki ta shige.           12:44am sam ta kasa bacci ga wani zafi da idanuwanta keyi ,tunanin  d'azu ta shiga yi fuskar Ahmad ta fara yimata yawo a kai.Canji kad'an taga yayi mata ,saje dayake kwance a fuskarsa se d'an murjewa daya 'karayi ga haske daya 'karu a  fatarshi.

      Bata ankara ba taji danshi a fuskarta ,ita kanta batasan dalilin kukan ba ,da tayi tunanin zata iya mance da rayuwar da sukai da Ahmad amma a yanzun taga ba haka bane komai ya dawo sabo.

      Ganin kukan baze mata magani ba ta tashi ta d'auro alwala ta tada sallah.

•••

  Washegari Saturday Nasreen ba school da wuri ta farka ta hana Reyhana komawa bacci gashi idanuwanta sunyi mata nauyi.

      "Ummie mije kitchen muyi indomie tare". Nasreen ta fad'a.

         " Nasreen please mana ga Aunty Walida ". Cewar Reyhana a kasalance.

          " Ai ita duka na zata yi idan na taso ta". Ta fad'a.

      Haka dole ta ha 'kura da baccin suka shiga kitchen.Labarin Uncle ta fara bata,chocolates dayake suyo mata.

      "Nasreen tun yaushe yake zuwa makarantar ku?"

      "Kullum kullum ya dad'e ,ya d'orani a lilo ya siyamin chocolate". Nasreen ta fad'a tana nishad'i abinta.

      Reyhana tunani ta tsindima ta mance da frying pan da ta d'ora a cooker gas ,seda taji 'kauri ta tuna da sauri ta dan'ki handle d'in hannunta ya goje ta 'kona d'anyatsa.

      " Arghh!" Ta saki 'kara.

     Takaici biyu ya isheta batasan sanda ta tsuguna ta soma kuka ba.

  °°°

    Zainab tun da ta tashi ta kasa fitowa,daga Umma har Ahmad tsoron had'uwa dasu take, tana tsoro kar ya huce a kanta,Umma kuma batasan ko har yanzu bata dena fishi ba akan abinda akai wa 'kannenta ba.

       Tana wannan batun ne sega Umma ta shigo d'akinta.

AR²💖

         1137+ words ,too short i know,please manage am not feeling well . 😤😷

Pls don't forget to vote.

Jasko💕

     

      🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣6⃣

  Tana ganin shigowar Umma tayi sauri ta mi'ke daga kwance,cikin rissinawa ta gaisheta.

     Umma fuskarta a sake ta amsa tare da fad'in."Yau ba makaranta kenan".

      "Eh".Ta amsa.

       " Dama naji ki shiru nace bari na duba ki".Umma ta fad'a.

       "Uhm yanzu dama nake son fitowa".Zainab ta fad'a fad'a tana sosa kai.

        Umma bata dad'e da fita daga d'akin ba Zainab ta fita itama,kamar koyaushe ta shiga kitchen taya ta had'a breakfast sede ta raba hankalinta biyu tana tunanin fitowar Ahmad.

•••

Mommy a tsugune ta tarar da Reyhana a kitchen d'in se sharar hawaye take,Nasreen tana daga gefe tana kallon Ummienta na kuka fuskarta itama kamar mey shirin yin kukan.

      " Reyhana meye haka? Menene?"Mommy ta tambaya.

      Shiru tayi bata ce komai ba sede yanzun tayi dena kuka,tashi tayi tsaye a daddafe tana share hawayen .

      "Kukan na meye? Mutum da giramansa yasa kuka ga yarinya babarta na kuka kince itama tayi kenan". Mommy ta fad'a.

     Kai kawai ta girgiza ba tare da tace komai ba taja hannun Nasreen ta fita zuwa d'aki.Tana zuwa ta tarar da missed call d'in Sameer bata jin zata iya calling back dan a yanzu bata son magana da kowa.

     Nasreen d'in ma kayan wasanta ta d'akko mata ta bata,ita kuwa kwantawa tayi kawai tana 'ko'karin mancewa da damuwar dake ranta.

                   ***      Umma suna zaune a parlor Ahmad ya shigo,rissinawa yayi ya gaisheda ita ba tare da yana tsammanin amsarta ba.

    " Lafiya lau". Ta amsa ba tare da tana kallonsa ba.

     Zainab ma 'karfin hali tayi ta gaisheshi,yana amsata ya koma d'aki koh takan abinci be biba.

       Wajajen 11:15am sega Imran yazo,yana gaisawa da Umma ya komo wajen Ahmad.

       "Ya ake ciki neh yanzu?" Imaran ya tamabaya.

       "Ya kwa ake ciki ganinan na rasa abinda zanyi". Ahmad ya fad'a.

       " Yanzu ka samu ka kira su Aunty's nakan ba basu ha'kuri atleast za'a samu relief and maganar 'boye-'boyennan bashi bane ka rife ido kawai kaje gidansu ayi magana frankly kuskure ne an riga da anyi ba abinda ze chanja, hakane?"

        Kai Ahmad ya gid'a alamar "Eh".

        " Yaushe toh zakan?" Ya tambaya.

       "Today". Ahmad ya amsa.

         " Good".

    Ahmad bayan tafiyar Imaran ya kira Aunties nashi d'aya bayan d'aya ya basu ha'kuri.

     Da kansa ya shiga kitchen ya zuba abinci yaci ya komo d'aki.

    °°° Se 11:16am Reyhana ta farka daga baccin dan bata san lokacin data soma ba.Yanzu taji d'an ded ba kamar d'azu ba ,seda tayi wanka ta shirya tukun ta sakko 'kasa.Ba kowa a parlor, kitchen ta shiga ta zuba abinci tukun ta dawo parlor ta zauna.

      Mommy da ta sakko ta ganta seda ta sake tambayarta dalilin kukanta amma ta'ki fad'a dan haka ta rabu da ita.

      Yau Nasreen dama ta samu se wasanninta take dukda bame taya ta kowa yana harkarsa.Walida tana d'akinta Ikram kuwa ta fita Bassam ma yana d'aki,Sageer da yanzu yama dena fitowa parlor balle cin abinci a table.

      Se bayan ta koma d'aki ta duba wayarta taga message na Sameer,numbernsa tayi dialing ba jimawa yai picking.

        "Assalamu Alaykum". Yayi sallama.

          " Waalaikumussalam".Ta amsa murya a sha'ke.

      "Are you ok?" Ya tambaya.

      "Yes". Ta amsa a ta'kaice.

      " D'azu na kira koh kina bacci ne?"

       "Eh". Ta amsa.

       " Ok".Ya fad'a.

       "Reyhana". Ya kira sunanta.

     Daga yadda ya kira sunanta ta san maganar da zeyi.

      "Reyhana mun gama karatun ,ga school 'yarmu ta soma zuwa, what are we waiting for?"Ya tambaya cikin sassanyar murya.

    Shiru tayi bata ce komai ba har kusan 2min.

     " Uhm? say something ".Cewar Sameer.

      " Reyhana this is the right time,shekaru suna ja fa ko so kike na tsofe?"Ya 'kare maganar da dariya kad'an.

      "Kowa fa ke yake jira,family sun 'kagu suga in-law d'insu kullum se sin tambayake koh bakyason barin gida neh? don't worry Nasreen na tare dake and you know am always by your side".

      " Sameer please ina so a yanzun ka bani dama nayi shawara".Reyhana ta fad'a.

      "Karki damu inde shawara ce ni zanfi kowa jin dad'in hakan ,na baki dama kiyi shawara Reyhana duk abinda kike so shi nake so". Sameer ya fad'a ba tare da alamar ya damu ba.

      " Nagode".Ta fad'a.

       "Is OK"

       Hira kad'an suka ta'ba sannan sukai sallama, wayar ta dire gefe tana tunanin abin yi.

    •••

Ahmad seda ya bari yayi sallar Asr tukun yayi shirin zuwa gidan su Reyhana, ba tare da ya sanar da Umma ba ya fita dan yasan ba sauraransa zata yi ba.

     Yana hanya a zuciyarsa addu'a yake tayi Allah yasa komai yazo masa da sau'ki ,gashi yanzun baida buri irin Reyhana tayi masa magana ko yaji sa'ida.

     Bayan yayi parking seda yayi kusan 5min tukun ya fito daga motar,a sanyaye ya 'karasa gate d'in,yana shirin tura 'kofar gate d'in sega motar Abba nan ta kunno kai.

      Abba da farko be gane Ahmad ba seda ya fito daga motar ya kula.Cikin rissinawa kansa a sunkuye ya tsuguna ya gaida Abba.

      "Ahmad ne a gidannan" Cewar Abba bayan ya amsa.

      Shiru yayi Ahmad bece komai ba yana jiran Abba ya sake wani maganar."Mu shiga daga ciki koh".Abba ya fad'a.

      Cikin gidan suka 'karasa Ahmad yana biye a bayan Abba.Bassam ya kira ya shigo masa da motar.Parlorn ba'kinsa Abba ya wuce da Ahmad.

      Bassam bayan ya koma ciki yaje ya tsaiguntawa Mommy,tana daga kwance amma seda ta mi'ke zaune tana mamaki.

       "Yanzun yana ina?" Ta tambaya.

       "Abba ya shigar dashi parlonsa". Ya amsa.

       " Jeka kira min yayarku". Ta fad'a.

       A d'an 'kan'kanin lokaci sega Reyhana ta shigo d'akin Mommyn.

      "Reyhana kinji wani abun mamaki?" Cewar Mommy             "Mey?" Ta tambaya.

        "Yanzunnan Bassam yake fad'a mini Ahmad wai yazo ,yanzu haka yana parlorn Abbanku".

      Reyhana bata wani yi mamaki sosai ba dan tasan za'ai haka.

       " Toh wajen Abban yazo ai"Ta fad'a.

        "Ehyyi yasan ba saurararshi zan ba". Mommy ta fad'a.

        " Ina Nasreen?"Reyhana ta tambaya.

        "Au kai masa ita zaki?"Cewar  Mommy.

         " A'a ya za'ai na kaita gurinsa ,ban ganta bane a d'akin". Reyhana ta fad'a.

       °°° "Ahmad ya akai haka shekaru 6 baka waiwayi  yarinyarnan  ba?" Abba ya tambaya.

      Labari Ahmad ya shiga bashi duk yadda akai,daga 'karshe ya bashi ha'kuri.

     Abba ba d'an zafi bane dama saboda haka ya ha'kura da laifin da yayi na 'kin zuwa sanda ya kamata.

     Abba da kansa ya kira Mommy da Reyhana ya fad'a masu komai a gaban Ahmad, itan ma ha'kuri ya bata sosai dukda yasan hakan baze sa ta dena jin haushinsa ba amma shi a yanzu ba wannan ce damuwarsa ba ,bashi da abinda ya wuce Reyhana ta kula shi.

     Tun sanda ta shigo naki ta'ki bari su had'a ido dashi tana jin idanunsa a kanta.

   Abba da aka kirashi a waya ya tashi ya bar parlorn Mommy ma tashi tayi ta fice ta bar Reyhana.

      "Reyhana". Ya kira sunanta a sanyaye.

      Banza tayi dashi batace komai ba.

     " Please talk to me,baki yarda da abinda Abba ya fad'a bane ? nasan ban kyauta ba shiyasa nake so na baki ha'kuri please ki saurareni".

       "Toh waya ce ba ha'kuri kazo bayarwa ba ? Ai nasani you don't have to tell me again,anji ka bada ha'kuri shikenan komai ya wuce then se kowa ya shiga harkarsa koh akwai wani abu daya rage baka fad'a ba a labarin naka?"

     Duk wannan maganar da take masa tana daga zaune.

     "We are not done mana atleast idan baza mi wani maganar ba ai semi ta Nasreen". Ahmad ya fad'a.

      " Really?"Ta fad'a cikeda rainin wayo.

      "Reyhana please". Ya fad'a.

       "Meyasa baza ka cigaba da plan naka ba na wasan 'buya scretely kake ganinta kamar yadda ka saba yi ,I think haka zefi maka at the end kuma sega sace ta". Reyhana tana gama fad'ar haka ta tashi da sauri ta fice.         Baki wangalau ya bita da kallo " A yaushe yace ze sace ta? Yaushe Reyhana ta zama haka? " Abinda zuciyarsa ke tambaya kenan.

      Abba daya dawo d'akin ya tarar da Ahmad shi kad'ai,Ahmad ba tare da ya nuna damuwarsa ba yayi sallama da Abba ya fito.

     A harabar gidan ya tarar da Nasreen ta fito,tana ganinsa ta ruga a guje ta rungumeshi.

     "Yeyy! Uncle yazo gidan mu".

      " Uncle yaushe kazo?" Ta tambaya bayan ta d'ago kanta.

      "D'azu ban ganki bane". Ya fad'a.

      " Zaka zauna miyi wasa?" Ta tambaya.

    D'an murmushi Ahmad yayi kafin ya sunkuyo kad'an yace"Wani lokacin se miyi wasa ,fad'amin mey kike so na kawo miki ?"

     "Kayan wasa da chocolate se 'yatstsana irin na MBC 3". Ta fad'a.

      " Ok don't worry zan saya maki".

      Tsalle ta shigayi tana murna,bye bye tayi mishi tukun ta koma ciki shima ya tafi.Reyhana tana hangosu ta window tun d'azu har ya fita tukun ta dawo ta zauna.

         Waya ta d'auka ta kira Saudat ta fad'a mata abinda ke faruwa.

     "Toh ya zakiyi idan baki ha'kura ba?" Saudat ta tambaya.

      "Hanashi zuwa inda take zanyi ,yana sonta ya tafi ya barta". Cewar Reyhana.

     " Bakida gaskiya anan,kede taki dashi ku tsaya anan amma banda Nasreen babu yadda zaki 'yarsa ce yau ya nemi ya kar'beta ba yadda zaki". Saudat ta fad'a.

     "Cabb! Ya isa ya d'auken ita? Ya kaita ina d'in?" Ta tambaya.

    "Wajen matarsa". Ta amsa ta.

    " Ya dad'e beyi haka ba". Reyhana ta fad'a.

     "Kishi koh,kema kiyi naki auren ga Sameer bawan Allah har ya gaji da jira". Saudat ta fad'a.

     " Toh ke wayace maki ma yayi aure?"

      "Kefa kikace kina tunanin hakan". Saudat ta amsata.            " Oho de". Reyhana ta fad'a.

      "Ke wai ya Sameer d'in har yanzu bani ce masa komai ba?"

       "Eh". Ta amssa.

       " Reyhana baki san alkairin dake tare dashi ba nide ina ganin kawai ki ha'kura ki aureshi mutmunninan yana sonki dayawa fah".

     "Naji ni karki isheni kuma am hanging". Reyhana ta fad'a.

     " Toh kide yi tunani ta Sameer ta Ah.." Bata bari ta 'kare ba ta katse wayar.

AR²💖

    Pls comment,vote and share.Luv u all💋

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣7⃣

  Abba zaunar da Mommy yayi a d'aki yana tuna mata abubuwan da tayi wa Ahmad a baya.         "Kinga de yadda ikon Allah yake koh?"Cewar Abba.

         Mommy shiru tayi bata ce komai ba tasan dama se ya dawo mata da zancen.

       "Shiyasa koyaushe nake fad'a maki ba wanda yasan gobe,yarannan ba irin abinda baki a kansa ba kika d'ora masa karan tsana ke seya saki 'yarki kuma bayan kindena ganin shi a gidanki nan ma ba'a tsira ba toh gashi ya dawo wajen 'yarsa".

     " Kai kuma dawo da zance baya duk abinda ya riga ya faru ai ya faru kuma meye amfanin tada zancen,maganar ya dawo ni be shafeni ba".Mommy ta fad'a cikeda borin kunya.

    "Tunatar dake nayi". Abba ya fad'a.

      "Wannan yaran fah baka ta'ba magana a kan halin dayake ciki ba". Mommy ta fad'a tana son chanja topic d'in.

    " Wa fah?" Abba ya tambaya yana neman 'karin bayani.

    "Sageer mana".Ta amsa.

     " Shi d'in kuma mey yake damunsa?"

      "Gashinan baya shiga cikin mutane abinci ma baka ganinsa ya ci aikin ma ni bansani ba koh baya zuwa".

     "Amma de ai shi ba yaro bane da za'a dinga jawo shi ana tambayarsa meke damunsa". Abba ya fad'a.

     " Toh zira masa ido zamu zauna miyi kenan koh me ze faru ya faru kenan". Cewar Mommy.

     "Ni kin ta'ba fad'a min idan ba yanzu ba?"

     "Toh yanzu ai na fad'a maka".

      " Toh Allah ya sawwa'ke".Ya fad'a.

      "Ameen". Ta amsa                   ***   Ahmad daya koma gida zuciyarsa fyas ,Umma da Reyhana ne damuwarsa yanzu.

     8:13pm bayan ya dawo daga masjid ya d'auki wayarsa yai dialing numbern Reyhana.

•••

   Tana parlor a zaune ita da su Ikram da Mommy sega kira ya shigo wayarta.Sam bata kawo Ahmad bane dan ba layin data sanshi dashi bane.

     " Assalamu Alaykum".Tayi sallama bayan tayi picking.

     Seda yayi gyaran murya tukun ya amsa. "Waalaikumussalam".

      Da tana jingine da jikin sofa amma jin muryar yasa ta gyara zama." Kamar Ahmad ". Ta fad'a a zuciyarta.

   " Reyhana ".Ya kira sunanta.

     Tashi tayi tsam daga parlorn ta haye sama, su Ikram idansu 'kir akan ta bama su kad'ai ba hatta Mommy seda tabi bayan ta da kallo.

     " Waye?" Ta tambaya duk da kuwa ta gane mey magana.

     "Yanzu kin manta da muryar tawa ma?"

      "Da zaka fad'a min da wanda nake magana da yafi dan ina da abun yi". Ta fad'a.

     " Toh ranki ya dad'e ,Ahmad ne". Ya amsa.

      "Wane Ahmad d'in?" Ta tambaya.

      Dariya tambayarta ta bashi dan yanzun ya gano tasan mey magana sarai.

    "Reyhana please mana nasan kin gane mey magana,ina so miyi magana". Ya fad'a.

     " And nace a'a".Ta fad'a.

     "Please ,am very sorry". Ya fad'a.

     "Mey kayi min da zaka bani ha'kuri ?"

     "Laifi mana ,lokacin da ya kamata ace nazo ban..." Be 'karasa magana ba ta katse wayar

       "Reyhana". Ya kira amma shiru yake ji

     Koda ya sake kira bata d'aga ba,daga baya ma kashe wayar tayi ta barta a d'aki ta dawo parlor tana so tayi pretending komai is normal.

     Haka dolensa ya ha'kura ya ajje wayar gefe ,tunane-tunane ya shiga yi ta yadda ze sake 'bullowa ta saurare shi.

    Washegari da safe yana tashi yaje ya gaisheda Umma itama kamar koyaushe ba fuska balle ya zauna yayi mata wani surutai ,Zainab tana d'akinta bata fito ba.

      Wajen 'karfe uku ya fita yayi wa Nasreen siya-siyen kayayyakin data lissafo,suma su Umma yayi musu wasu 'yan siyayyar.

      Zainab ce ta 'kar'bi kayan daya siyo ta kaiwa Umma,ba tare da ta duba ba tace takai store ta ajje.

     Seda yamma tayi tukun ya tafi gidansu Reyhana,lokacin da ya isa 'kofar gidan ya kira Reyhana a waya amma ta'ki picking dan haka yayi mata text ya fad'a mata yana  waje.

      Reyhana bayan ta karanta text d'in ta ta'be baki." Toh ina ruwana"Ta fad'a a fili.

      Yana waje shiru-shiru beji reply ba ,ya jingina da mota yana tunanin wani way d'in ya hangi Nasreen tana fitowa daga ma'kotansu.

      Dad'i yaji sosai ganinta ,tana ganinsa ta 'karaso da gudu ta ma'kaleshi."Uncle yanzu kazo baka ganni ba koh?"

    "Ehyyi". Ya amsa.

     " Ummiena bata san na fita ba ,tana d'aki na gudo waje".Ta fad'a tana dariya.

    "Laa kina so Ummienki ta damu sosai?"

     "A'a". Ta fad'a tana girgiza kai.

      " Toh ki dena fitowa bata sani ba kinji".

      "Toh". Ta amsa.

      " Uncle ka kawo mini kayan wasan?" Ta tambaya.

      "Ehyi na kawo miki suna mota". Ya amsa yana murmushi.

      " Yeyy! "Tasa tsalle tana le'ka motar.

      'Karasowa yayi ya bud'e mata ya d'akko ya mi'ka mata" Yeyy! Uncle thank you".Ta fad'a tana bud'e jakar ledar.

      "Uncle ka taho mije na nunawa Ummiena".

       " Zan dawo yanzu zanje unguwa".Ya fad'a.

       Ma'kale kafad'a tayi tana buga 'kasa."Kace idan kazo zamiyi wasa".

     "Eh mana ba'kyaso naje unguwa na sake siyo miki chocolate?"

      "Ina so". Ta amsa da sauri".

      " Yawwa good girl,toh maza jeki gida".Ya fad'a.

      "Bye bye". Ta fad'a tare da shigewa gida.

       Shima bye d'in yayi mata waving tukun ya shige motarsa ya bar layin.

       Tana shiga parlor ta shiga nuna musu.

       " Ummie kinga 'yatstsanata.

      Reyhana ko ba'a fad'a ba ta san Ahmad ne ya siyo.

      "Toh wanne za'a bamu acikin chocolate d'in?" Walida ta tsokane ta.

     "A'a bazan baku ba".Ta fad'a tana ma'kale kafad'a.

      " Kinga nima bake ba game a waya ta". Walida ta fad'a.

      "A'a".

      Seda ta game kalle chocolates d'in sannan da'kyar ta za'kulo 'kwaya hud'u ta ajje mata.

      " Sauran nawa neh ni kad'ai".Ta fad'a.

       Mommy da lokacin ta fita daga kitchen ta ta'be baki ta haye sama.

      Reyhana ko zama batai ba sanda ta shiga d'akinta sega wani kiran na Ahmad yanzu harta gane numbern ma duk da batai saving ba.Bata dad'e da katsewa ba sega kiran Sameer ya shigo seda ya kusa tsinkewa tayi picking.

     Ahmad daya sake kira yaji  tana waya ,katsewa yayi ya ajje wayar a gefe amma sam hankalinsa ya kasa kwanciya.

     Bayan kamar 10 min ya sake kira, ga mamakinsa seya ji har lokacin waya take,ganin ya isheta tayi rejecting kiran nashi.

     Nan fa ya sake Shiga damuwa a zuciyarsa yana fad'in."Wannan wane irin waya take har ta kaita more than 10 min?"

     Tunani ya shiga yi iri- iri wayarma wulli yai da ita gefe ya kasa samun sukuni.

       Ita kuwa tana gama wayar ta kashe wayar gaba d'aya.

               °°°

Washegari da safe tana bud'e wayarta da text d'in Ahmad ta fara cin karo.

      I am sorry for all i have done,i know i have hurt you badly. I don't know what got over me to behave that bad.Please i am sorry forgive me.

Tana gama karancewa tayi deleting ta ajje wayar gefe.

      Tuna yau Monday yasa ta tashi Nasreen da wuri tayi mata wanka ta shiryata ,sanda suka sakko 'kasa kowa ya hallara a dinning table.

      Yau da kanta ta kaita school driver har yanzu ba lafiya.Nasreen ta cika aljihun jaka da chocolates badan Reyhana ta duba ba da dasu zata shiga class.'kwaya biyu ta rage mata ta kwashe sauran  ta ajje a mota. "Sekace hauka chocolate abinci ne". Reyhana ta fad'a.

     Nasreen kuwa kuka tasa da'kyar ta fita ta shiga makarantar.

°°°

Ahmad da wuri ya fita ,Zainab bata da lecture da wuri shiyasa basi tafi tare ba.

      Yau daga wajen aiki be dawo gida ba ya wuce school d'in Nasreen,lokacin sun fito sallar zuhr.A cikin mota suka ci abincin daya tsaya ya siya a restaurant.

      Ko takan abincin school bata biba ,tana gama ci ta d'akko ragowar chocolate d'in ta ta 'bare.

     " Uncle kaga yau Ummie ta 'kwace min chocolates d'ina ,guda biyu kawai ta bani nayi kuka amma bata bani ba". Nasreen ta fad'a.

     "Toh kiyi ha'kuri Ummie bata so kiyi ciwon ha'kori". Ahmad ya fad'a.

      " Ha'kori na zeyi ciwo ina sha dayawa?"

      "Eh". Ya amsa.

       Seda aka koma class tukun ta koma ciki Ahmad ya tafi, a hanya ya kira Reyhana a waya duk da kuwa yasan baza ta d'aga ba,kusan sau uku ya kira bata d'aga ba ya ha'kura.             Wajajen 7:30pm bayan ya koma gida ya iske Umma a parlor, tafiya da zeyi gobe zuwa Lagos ya sanar mata.

    "Allah ya kaimu" Ta fad'a.  

     "Ameen". Ya amsa .

     Ya zaci zata tambayi kwana nawa zeyi amma yaji ba haka ba,a sanyaye ya mi'ke ze fita ta kirashi.

     " Ahmad ".

   Da sauri ya waiwayi " Na'am".Ya amsa.

     "Kwana nawa zakai a can?" Ta tambaya.

      "Kwana biyu". Ya amsa.

      "Toh bayan ka dawo zami wata magana da kai". Ta fad'a.

     " Toh Umma".Ya fad'a.

     Se bayan ya koma d'aki tukun ya shiga tunanin maganar da zatai masa."Ko mey zata ce? Ko akan Reyhana ne?" Ya tambaya a ransa.

     Da daddare ya had'a kayansa a suit case ,wayarsa ya d'auka ya kira Reyhana, kamar yadda yayi tsammani batai picking ba.

        Pick my call please, i want to talk to my daughter.

Text d'in dariya ma ita ya bata."Watoh gadara ma zeyi,lalle wuyansa ya isa yanka let see".Ta fad'a.

     Sake kiranta yayi karo na biyu,bakinta fal da magana ta shirya rashin mutunci ,ba jimawa tayi picking.

AR²💖

     Next page there is gonna be a special thing👄👄

    Pls comment,vote and share.luv u all💋

Jasko💕

   🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣8⃣

Ahmad yana sane ya fad'i haka dama so yake ta kulashi.

Shiru tayi lokacin da tayi picking ,yana jira yaji tayi magana amma shiru dan haka shi ya fara.

"Bata wayar koh". Ya fad'a.

" Seriously? master right?" Ta fad'a.

"Reyhana waya zaki bata yarinya tana son jin muryar babanta"

"Force me,gara ma kadena wannan mafarkin dan bata san da kaiba kadena wani shishshige mata atoh dan kwanannan seka dena ganinta".

" Ko kuma ke ki dena ganinta ba". Ahmad ya fad'a.

"Au haka ma zaka ce? Yaushe kasanta ma gabad'aya ? Sanda take bu'katarka ina kake?"

"Reyhana kidena fad'in haka ,yaushe zaki yarda dani ne? Believe me ba'a son rai na na d'au tsahon wannan lokutan banzo gareta ba,please i am sorry forgive me".

" You better stop apologizing".Ta fad'a cikin jin haushi.

"Ok then wazan tambaya Nasreen?"

"Don't ever try it,tana yarinyarta bazaka jagula mata lissafi ba"

"Ok toh naji,yanzu tana ina?" Ya tambaya.

"Mey zakai mata?"

"Gaisawa mana". Ya amsa.

" Tayi bacci ".Tayi 'karya.

"'Karya".Ya fad'a.

" Ni nake maka 'karya?"

"Au sorry".Ahmad ya fad'a kamar mey shirin yin dariya.

" Don't sorry me ".Ta fad'a.

Kafin ya sake wata maganar har ta katse wayar.Conversation d'in da sukai ba 'karamin dad'i yayi masa ba ,text ya tura mata kamar haka.

Am sorry Ummien Nasreen,goodnight 😘😘 to my Angel.I mean Nasreen

Check your whatapp pls..

Tana gama karancewa tayi tsaki abin nasa ya soma isarta dan taga alamar ya 'karo wula'kanci.

Da ta ajje wayar se kuma ta d'akko ta kunna data ta hau whatapp.Number d'inshi taga ya turo message tana bud'ewa taga image na teddy bear pink an rubuta

"for someone special❤

Reyhana:"Mey zanyi dashi?"

Ahmad: "Waya ce naki neh? na Baby na neh".

Reyhana: Toh meye na turo mini se ka bari idan ka had'u da ,'yar taka ka nuna mata"

Ahmad:"Bafa baby Nasreen ba,ki gane mana".

Reyhana:" Wai kai 'kalau kake? Wace babyn taka tukunna ma"

Ahmad:"Bafa ke nace ba,ina nufin...."

Reyhana:"Kai ya rage ma".

Daga haka ta sauka ta ajje wayar gefe ,shima ganin bata kai ya ajje wayar.

*** Tunda ya tafi Lagos be samu sunyi waya da ita ba sede yana turo mata apology text,kwanansa biyu ya dawo kano se bayan maghrib ya diro kano a ranar be samu yaje gidansu Reyhana ba.

Umma ta sakko yanzu ta dena fishin da koda ya tafi tana kiransa taji lafiyarsa.

Yau wajajen 10:30am ya biya makarantarsu Nasreen be jima ba ya komo gida ,daya gwada kiran Reyhana yaji switchoff.

Yana zaune Umma ta shigo d'akin,dama yana jira yaji tayi masa maganar da tace zasi bayan ya dawo kuma yaga bata yi ba.

Gefe guda ta samu ta zauna kan wani wani kujera.Gyaran murya tayi kafin ta soma magana.

"Kaga yanzu de baka da wata matsala da take a gabanka da zaka ce ta hanaka yin aure,da farko nayi tsammani na fara jin maganar daga gareka amma shiru shiyasa da kaina zan tambayeka akwai wacce kake da burin aura koh babu a yanzu?"

Tambayar Umma ba 'karamin razana shi tayi ba ,ba dan komai ba se dan baida amsar da zai bata.

"Baka ce komai ba". Cewar Umma.

" Uh..babu".Ya amsa yana sosa 'keya.

"Babu". Ta mamimaita a fili.

Dama haka take son ji dan ta dad'e da 'kudura wani abun daban ,da ace zece da akwai wata bata da hujja amma yanzu tunda babu komai zezo yadda take so.

" Toh mu muna da ta gida". Ta fad'a.

A rikice yace "Uhm?" Yana so ya tantace ko kunnensa neh beji dede ba.

"Nace akwai a gida,abune ya riga daya faru tun farko kuma dama Allah yayi da rabon 'ya shiyasa ba yadda za'ayi amma dama shiyasa so dayawa iyaye da kakanni suka fi gane auren gida gudun irin faruwar hakan ,d'an uwanka yafi sanin darajar ka da mutuncin ka ba kamar bare ba,kuma nasan wannan yarinyar bazata ta'ba wula'kanta ka ba yarinyace me hankali ".

Duk wannan maganganun da take shi ba sune damuwarsa ba kawai soyake yaji ta fad'i yarinya da take nufi.

" Kai kanka kasan halin yarinyarnan Zainab a zamaninnan masu hali irin nata tsirari ne".

"Zainab? Ni nace mata ina son Zainab?

"Toh dole seka ce?" Wata zuciyar ta fad'a masa.

"Amma Umma.." Be 'karasa ba ta katse shi.

"Wani uzurin zaka zake bayarwa? Zan baka gurguwar shawara ne kake tunani ? Kai shikenan kafi so ka cigaba da zama haka ,ka gama karatun,ka samu aiki mey kyau kuma mey kake bu'kata?" Ko wata 'karyar zaka sake yi min?" Ta 'kare fuskarta tana nuna alamar fushi.

Tuna yadda Umma bata iya fushi ba kuma baya so ya sake 'bata mata rai laifi goma da ashirin shiyasa yai shiru yana tunanin amsar da zata fito daga bakinsa.

"Umma duk yadda kika ce ,hakan ba damuwa bane Umma kuma nasan baza ki za'bamin wacce ba ta gari ba".

Umma taji dad'in amsarsa sosai ,tasan yin hakan ba 'karamin farantawa iyayen Zainab ze ba ,kuma zasu ga sun saka musu da tallafawa Ahmad samun aiki da mahaifinta yayi.

"Barka haka nake son ji ,zan kira kawunka miyi magana dashi anjima".

" Umma amma ita ai bata gama makaranta ba".Ahmad ya fad'a du dan ya samo mafita.

"Makaranta ai ba matsala bace abinda ta kusa gamawa ma ,koh Lagos d'in za'a tafi da 'Yar tawa ban sani ba". Cewar Umma cikeda zolayi.

Murmushin ya'ke kawai yayi dan hankalinsa ya d'aga.

Yana ji tana masa maganar ya soma gina wani plot dayake dashi kawai uhm yake amsata tunaninsa sam baya gun har ta fita.

Ya rasa wanne daga cikin abokanansa ze kira yaji sa'ida ,yasan sadiq dariya ma zeyi masa gwara Imran.

Koda ya kira imran ba wani support hakan ba'karamin sake bashi haushi yayi ba,yau yaga abu da girmansa za'ai masa auren dole sekace a 'kauye .Abinda yayi tunani a zuciyarsa kenan.

Ko abincin rana kasa ci yayi be fito daga d'aki ba se lokacin da taji Umma ta kirashi yaje ya d'akko Zainab daga makaranta.

A hankali yake tu'kin har ya isa makarantar ,yana parking ya kirata ya fad'a mata yana jiranta.

Ba'a wuce 5min ba ya hangota tana tahowa.Kallanta yayi tayi tana tahowa shi tunda yake be ta'ba kawota a ransa a matsayin matar da ze aura ba.

Yana wannan tunanin ta 'karaso har motar.Ita kallonta da yake yasa ta sunkuiyar dakai a tunaninta ko du cikin love ne.Se da ta bud'e 'kofar motar tukun ya dawo daga tunanin dayake.

"Yaya barka da rana". Ta fad'a sanda ta shigo.

" Yawwa ya school d'in?"Ya tambaya.

"Alhamdulillah". Ta amsa.

Daga haka be sake cewa komai ba har suka isa gida.

Yana shiga d'akinsa ya sake kiran Reyhana yayi sa'a akai picking.

" Hello".Yaji an fad'a cikin 'yar 'karamar murya.

"Nasreen?" Ya tambaya dan yaji kamar ita.

"Na'am". Ta amsa.

" Uncle neh".Ya fad'a.

"Laa! Uncle ,d'azu Auntynmu ta kawo ni gida kaina yana tayi mini ciwo nayi kuka". Nasreen ta fad'a.

" Ciwon kai kuma,ayya! Sorry kinji ,kinsha magani?" Ya tambaya.

"Eh Ummiena ta bani". Ta fad'a.

" Yanzu ya dena?" Ya tambaya.

"Eh".Ta amsa.

" Ina Ummienki?"Ya tambaya.

"Tana kitchen na kai mata?"

"A'a anjima". Ya fad'a dan yasan kashewa ma zatai.

Labarin school tayi ta bashi kafin daga bisani sukai sallama.

Nasreen da kanta taje har kitchen ta fad'a ma Reyhana tayi waya da Uncle

" Ban hanaki d'aga min kira ba?"

"Ummie Uncle ne fa". Ta fad'a.

" Karki sake kinji koh".Tayi warning d'inta danma tayi ciwon kai da se taja mata kunne.

°°°

Umma ba 'bata lokaci ta kira kawun Ahmad tayi masa bayanin komai bayan ta gama ta kira wata sister tata itama ta sanar mata da abinda ake ciki.

*** Ko sati d'aya ba'ai ba aka je neman auren Zainab,dududu wata uku aka sa Ahmad gani yake kamar mafarki kawai kallon su yake suna abinsu,Zainab murna a gurinta ba'a misaltawa.

Reyhana yau da kanta ta kai Nasreen makaranta ,daga nan zata biya school fees na Nasreen seji tayi an fad'a mata Ahmad ya biya.

"Watoh ta nan kuma yanzu ze 'bullo". Reyhana ta fad'a.

Tana wannan batun sega kiran Ikram,tana d'agawa taji suna asibiti Sageer ba lafiya,da sauri-sauri ta shiga. mota se asibiti.

Mommy, Abba se Ikram sinyi cirko-cirko a bakin 'kofar d'akin da aka shigar dashi.

" Mommy meya sameshi?" Ta tambaya.

"Bassam ne ya shiga d'akinsa ze Kira shi ya tarar dashi a sume".Cewar Mommy.

" Subhanallahi".Reyhana ta furta.

Bata sake wata maganar ba sega doctor ya fito daga d'akin.

Da Abba da Mommy ya kira ya zaunar dasu yake tambayarsu tsahon lokacin da Sageer shafe baida lafiya

.Nan Mommy ta zayyane masa irin halin da suka tsince shi.

"Hajiya wannan yaron depression yana nema ya kamashi,ga dukkan alamu damuwa ta mishi yawa".

" Subhanallahi".Suka furta a tare kowannensu fuskarsa da damuwa.

"Amma yanzu ya samu sa'uki InshaAllahu zamu cigaba da bashi kulawa kafin a sallame ku". Doc ya fad'a.

" Toh muna godiya likita".Cewar Abba kafin daga bisani suka fita.

AR²💖

Pls comment,vote and share.Love u all❤

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 2⃣9⃣

  Sageer bayan kamar 30min ya farka,lokacinda suka shiga be bari ya had'a ido dasu ba ya kawar da kansa.

         Dukkansu suna tunanin wannan wata damuwa ce ke damun Sageer data saka shi ya shiga cikin wannan halin banda Reyhana da ita tasan komai.

                    ***       Around 3pm bayan ya dawo gida ya tarar da Sadiq,yana parlor suna hira da Umma.Ahmad suna gaisawa ya koma d'akinsa seda ya watsa ruwa tukun ya fito zuwa parlor lokacin Umma bata ciki.

     "Abokina yane?" Cewar Sadiq.

     Daga yadda yayi magana ya gano d'aya daga cikin rashin mutunci ne irin na Sadiq yasan Umma ta zayyane masa komai.

       Banza yayi masa bece komai ba sema wayarsa daya d'akko yana tapping.

      "Yanzu sede naji magana a wajen Umma instead ka same ni ka fad'a mini da kanka?" Sadiq ya fad'a.

       "Ni nasan ma mey kake nufi". Ahmad ya fad'a yana cigaba da danna wayarsa.

      " Zaka gane neh  na Zainab ".Sadiq ya fad'a yana 'kare maganar da dariya.

       " Kai! zan zageka".Cewar Ahmad wannan karan ba waya  yake kalla ba.           "Seda kar a kuma, bani labari mana mey kake shirya mana neh?"

       "Bansani ba".Ahmad ya fad'a.

       " Munafiki kana so kana kaiwa kasuwa ,kayi ka gama".Sadiq ya fad'a.

       "Base ka ganni ba zakai". Ahmad ya fad'a yana mi'kewa yabar d'akin.

       " Ina kuma zaka ,koh ka manta zaka d'akko Zainab".Ya jiyo Umma ta fad'a.

        "Nima ze ragen hanya" Sadiq ya fad'a yana daga parlor.

       "Toh kaji". Umma ta fad'a.

      Ahmad a cukule ya fita banda Sadiq daya biyo shi yana sake 'kular dashi.Dama ba wani rage hanya dan har school dashi aka je d'akko Zainab se bayan suna hanyar dawowa ya sauka.

        Ko shiga gida Ahmad beyi ba ya tafi makarantar su Nasreen ,seda ya tsaya yayi mata siya-siye.

       •••

    Sageer kwanansu biyu a asibiti aka sallamesu har yanzu be fad'a musu abinda ke damunsa ba.Se bayan sun dawo gida Mommy ta titsiye Reyhana dan taga alamar akwai abinda take 'boyewa.

        "Mommy wata yarinya fa yake so shine iyayenta suka 'ki ,su cousin d'inta suke son su bata". Reyhana ta fad'a.

       " Yanzu dama akan haka ya shiga wannan halin !?"Cewar Mommy.

       "Tun yaushe akai hakan baku fad'a ba?" Ta tambaya.

        "An d'an dad'e". Ta amsa.

        " Yayi kyau da 'boye-'boye ga result nan ai kungani ze kashe kansa akan wata yarinya ".

        Mommy d'akin Abba taje ta zayyane masa komai, shi fad'a yayi tayi." Akan wata soyayya yana nema ya samu shiga cikin wani yanayi sakarai kawai".

       Har d'akinsa Abba yaje, Mommy tana tsayar dashi amma ko sauraronta beyi ba.

        "Kai yanzu dama wannan abun ne yake damunka kabi ka wahalar da mutane!?"

        Sageer daya sunkuyar dakai ko 'kala ya'ki fad'a yana jin Abba yana fad'a.

       "Karka fasa damuwar tunda a kanka aka fara soyayya baban soyayya kaji".Abba ya fad'a tare da ficewa.

        Gidan tsit kowa ya shige d'akinsa Mommy an barta da tunani,a zuciyarta tana fad'in." Kamar d'anta za'a guje shi,meya rasa yaranta ba talaka ba da iliminsa kuma shi ba muni ba kuma baya shaye-shaye ko wani abu makamancin haka wane dalilin ne zesa a 'kishi ?" Abinda yake ta mata yawo aka.

                °°°         8:34pm Ahmad bayan ya dawo daga masjid yai dialing numbern Reyhana kusan sau uku ya kira amma batai picking ba.Da farko ajje wayar yayi amma wata zuciyarta sake zigashi ,haka ya sake kiranta still batai picking ba be gaji ba ya cigaba da kira ,yafi sau 15 .

     Reyhana jin ya takura mata banda silent da tasa ba dama tayi anfani da wayar ko yaya ta soma tapping seta ga kiransa.

       "Lafiya?" Cewar Reyhana bayan ta d'aga wayar.

       "Ina fa lafiya". Ahmad ya fad'a.

       " Toh se aka yi yaya?" Ta tambaya.

       "Ina Nasreen?" Ya tambaya.

        "Tayi bacci". Ta amsa.

         " Toh ki shafa min kanta".

         "Bata bu'katar hakan tunda kullum babarta tana mata addu'a".

          " Toh mungode da hakan".Ya fad'a.

      Shiru ba wanda ya sake cewa komai kuma ba wanda ya katse.

      "Reyhana". Ya kira sunanta cikin sanyayyar murya.

      "Meye yanzu kuma?" Ta tambaya.

       "Just want to say sorry". Ya fad'a.

       " For what?" Ta tambaya kamar bata gane inda ya dosa ba.             "For everything".Ya amsa.

         " Is that all?"Ta tambaya .

          "No". Ya fad'a.

           "Meya rage?"

           "Goodnight". Ya fad'a.

         Hanging tayi ba tare da ta sake magana ba kuma bata jira shima ya sake yi ba.

         Wayar kawai yabi da kallo yana murmushi sannan ya ajje ta a gefe.

         Reyhana bayan data katse wayar bata ajje ba seda ta 'karewa numbern kallo tukun ta maido da kallonta kan Nasreen da take ta bacci.

                  ***       Mommy da ta kwana da damuwar d'anta a rai da safe bata iya ha'kuri ba dan haka taje tana ro'kon Abba daya yi wani abun akai.

       " Ni kike so na kwashi 'kafa kenan naje nace a bawa d'ana yarinyar!?"

        "Ba haka nake nufi ba amma de idan aka tura manya ai zasu ga da gaske ake koh" Mommy ta fad'a.

       "Ke baki ji bayanin bane since cousin d'inta zasu bata ,toh kuma se 'ka'ka zaki iya hanasu ne?"

       "Ya kake magana haka  kasani ko su chanja ra'ayinsu".

        " Saboda d'anki shine autan maza koh?"Cewar Abba.

       "Dan Allah na ro'ke ka ,ka taimaka kayiwa 'yan uwanka magana".

       " Naji shikenan amma inde basu amince ba bazan sake sa 'yan uwana a wannan mganar ba".

        "Na yarda".Mommy ta fad'a da sauri.

          Aiko hakan akai ,Sageer ya basu address d'in gidansu yarinyar suka je sukai magana da mahaifin yarinyar.

       Mommy tun basu dawo ba ta sakko 'kasa tana jiran su dawo taji ya aka kaya.Shima Sageer yana d'aki duk abinda ake hankalinsa nakai amma ya kasa fitowa dan kunya.

      Seda aka shafe kusan 30 min sega su sun dawo Mommy ziba ido tayi tana jira taga sun zauna taji bayani.

  °°°

Ahmad daga aiki ya biya d'akko Zainab daga makaranta,a da yana so idan ya maida ita gida yaje makarantar su Nasreen amma kuma lokaci baze bari ba dan lokacin tashin su ya kusa,hakan nan ya tafi da Zainab makarantarsu Nasreen.

     Ita de taga an baud'e hanya amma bata tambaya ba,shima kuma beyi bayani ba har suka isa school d'in.

     Lokacin har an tashe su sun fara fitowa,chan sega Nasreen ta fito.Yana ganin fitowarta ya fita shima.

      Da gudu ta 'karaso inda yake tana tsalle." Uncle !"

     Zainab da take daga mota tana hangensu ,tana ganin Nasreen ta kawo ita ce 'yar tashi a ranta.

      "Uncle dawa yau kazo?" Ta tambaya tana hangen Zainab dake mota.

       Waigowa yayi ya kalli Zainab tukun ya juyo da kallonsa kan Nasreen.

       "Anty ce". Ya amsa.

       " Anty sunanta?" Ta tambaya.

        "Eh". Ya amsa.

     Da sauri ta 'karaso motar harda 'ko'karin bud'ewa,Zainab ganin haka yasa itama ta bud'e mata 'kofar.

      " Ina kwana".Ta gaisheta.

      Zainab tana murmushi ta amsa "Lafiya lau har yanzu safiya ce kenan" Ta fad'a tana murmushi.

       "Sunanki Anty koh?" Nasreen ta fad'a.

        "Eh sunana Anty Zainab". Ta fad'a.

       " Anty Zainab".Nasreen ta  maimaita.

        "Eh,an tashi daga makaranta koh".

        " Eh yanzu driver zezo ya d'auke mu".Ta fad'a.

         Hira sosai tayi tayi da Zainab kamar dama ta santa,seda driver yazo tukun ta tafi suma suka komo gida a hanya Zainab take maganar Nasreen,kad'an-kad'an yana amsata.

   °°°

     Abba ne ya soma tambayarsu ya ta kaya,mommy tayi 'kuri tana ji.

     "Ba yadda bami da mahaifinta amma ya'ki, mahaifinta ya riga ya tsaida magana yace mu baku ha'kuri da shima yaron". Wani daga cikin 'kanin Abba ya fad'a.

      Wani takaici ne ya ziyarci Mommy tana mamakin irin wannan mutanen daga baya ma tashi tayi daga parlon ba tare da ta gama sauraran su ba dan ba wata kalma da zata sa taji sanyi.

       Nasreen kuwa tana dawowa gida koh uniform bata cire ba ta soma bawa Reyhana labarin Uncle da Anty Zainab.

       " Nasreen kika ce Anty Zainab tare suka zo?" Ta tambaya.

        "Eh da uncle suka zo ,na nuna mata classwork d'in da Anty ta bamu a aji". Ta fad'a.

     Reyhana ko 'karanshe labarin ma bata ji ba tuni ta tafi tunani.Tunanin last ganinta da Zainab d'in ma ta Shiva lokacin da suka je Zaria suka taho da ita ta zauna gidan Umma.

     " Dududu bata fi 13yrs ba lokacin ".Ta fad'a a zuciyarta.

     " Toh haka kuma zatai ta zama after all shekaru shida da suka wuce!?" Wani 'bangeren taji zuciyarta ta fad'a.

      "Atleast fa tayi 19 koh 20 yanzu,toh koh...anya..kai no..ko ya aureta ma? "

       Lokaci guda taji kanta ya fara d'aukan zafi,haushin sa ne ya sake kamata ma watoh ya raina mata hankali shine harda matar daya aura Zeke zuwa wajen 'yarta.

       Tana wannan batun sega kiran Ahmad, a 'kule ta d'auki wayar tare da switching off."Zaka ga wacce zata d'aga ,watoh ga sakarya".Ta fad'a a fili.

AR²💖               *Pls comment vote and share.💋Next page there is gonna be a pic of...guess!*

Jasko💕

     

     

                     

    

      

                            ? *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣0⃣

Ahmad beyi mamakin 'kin picking call d'insa da Reyhana ta'ki yi ba kusan daman an saba shiyasa be kawo komai a ransa ba.

Ita kuwa Reyhana ta kasa samin sukuni se tunane-tunane takeyi ,ranar batai cikakken bacci ba.

***

An d'auki kwana biyu Reyhana bata picking call d'insa text kuwa baya gajiya haka zeta tura mata tana ignoring.

Yau da safe tana shirya Nasreen se ro'konta take barta taje gidansu Anty Zainab.

"Ko zaki d'ige bazaki ba gara ma kidena tunanin zuwa". Reyhana ta fad'a.

Chono baki tayi tana buntsire-bintsire baki." Tashi mije kiyi breakfast ki tafi makaranta".Reyhana ta fad'a

"Toh". Ta amsa.

Reyhana ce ta fara fita a tunaninta ko Nasreen tana biye da ita.Ganin Ummienta tayi gaba tayi sauri ta bud'e wardrobe ta ciro kayanta kala d'aya ta cusa a cikin jakarta ta fito se muzurai take.

Mommy kafin ta 'karaso dinning d'in ta nufi d'akin Sageer.

" Yau ma bazaka aikin ba?"Ta tambaya.

"Zanje se anjima". Ya amsa.

" Toh ka fito kayi breakfast mana kai shikenan kuma se kaita 'buya a d'aki".

Da 'kyar ya taso,sake cin magani yayi dan ya lura da su Ikram kallon munafinci sike masa,daga ya had'a ido da Abba seya kauda kai.

"Nasreen ya naga jakarnan ta 'kara wani tudu mey kika sa aciki?" Walida ta tambaya.

Reyhana se lokacin ta lura da tudun jakar,hannu tasa tana shafawa ko zataji wani abun da sauri Nasreen taja baya.

"Ba komai fa". Ta fad'a kamar mey shirin yin kuka.

" Toh kiyi sauri ki gama ci kafin driver yazo".Reyhana ta fad'a.

Mommy da hankalinta baya gunsu ko tanka musu ma batai ba.

°°°

Mommy bayan ta komo d'aki ta kira Anty Asma'u ta sanar mata halin da ake ciki daga baya Anty Asma'u tace zata zo Sageer d'in ya kaita gidan itama ta gwada tata sa'ar.

Ahmad se bayan ya dawo gida ya tafi school d'in su Nasreen, lokacin daya je ba'a tashe su ba seda ya jira.

Tana ganinsu ta kyalla da gudu hadda tuntu'be.

"Uncle !" Ta kira sunansa.

"Uncle ita Anty Zainab bata zo ba yau?" Ta tambaya.

"Ehyyi". Ya amsa.

" Uncle ka kaini wajenta". Ta fad'a.

"Driver zezo ya d'auke ki ,ki bari se kin fad'awa Ummienki".

" Ai na fad'a mata ,kaga ta bani wasu kayan ma". Ta fad'a tana zuge zip d'in jakar.

Shide yasan Reyhana baza ta bari ya kaita gida ba.

"Ummienki bata san kin d'akko ba koh?". Ahmad ya fad'a.

" Toh dan Allah ka kaini ai bazan dad'e ba seka fad'a mata".

"Ince mata mey?"

"Kace mata ka kaini wajen Anty Zainab".

" Yanzu yamma tayi ki bari se gobe kinga ba school ma".Ya fad'a.

"Uncle dan Allah ka kaini". Ta fad'a tana bubbuga kafa kamar zatai kuka.

Seda ya d'an nisa tukun yace " Toh zan kaiki".

Tsalle ta shiga yi tana murna ,da sauri ta shige motar.Ahmad seda driver yazo d'aukansu ya fad'a masa Nasreen baza ta biyo su ba.

Ya kira Reyhana a waya dan ya fad'a mata amma ta'ki d'aga wa ,daga baya kawai ya tura mata text  sannan suka tafi.

     Sanda suka isa gidan Nasreen ta 'ki sakewa.

    "Taho ki gaishe da Umma". Ahmad ya fad'a tare da kamo hannunta.

       A hankali ta 'karasa wajen Umma kanta a sunkuye ta gaisheta.

      " An dawo daga makaranta koh?" Umma ta fad'a.

      "Eh". Ta amsa tare da gid'a kai.

      Ganin Zainab ta shigo yasa ta yin murmushi tare da 'karasawa inda take.         "'Yan mata yau kece a gidan?"           Nan ma kai ta gid'a bata ce komai ba.

     "A cire jakar koh?"Zainab ta fad'a.

      " Eh,kayana ma suna cikin jaka".Ta fad'a.

       "Iyee kwana nawa za'ai mana?" Umma ta tambaya.

        "Zaki kwana?" Zainab ta tambaya.

     Kai ta gid'a tana murmushi ,Zainab ce ta jata d'akinta ta sauya mata kayanta, cikin 'kan'kanin lokaci ta fara sakin jiki tana ta labarin school.

     Reyhana yanzu ne ta lura da text d'in daya tura mata a take ta kira Ahmad.Yana parlor kiranta ya shigo dan haka ya d'an fita tukun yayi picking.

     "Ina ka kaimin yarinya?" Ta tambaya bayan ya d'aga.

     "Kinsan de bazan sace taba koh" Ahmad ya fad'a cikin sanyin murya.

     "Taya zan shede ka nasan mey ka zama". Cewar Reyhana.

      " Don't worry ba dad'ewa zatai ba".Ya fad'a.

       "Yanzu nake so ta dawo ni bana son gantali".Ta fad'a.

        " Ita fa tace a kaita wajen Zainab ".Ya fad'a.             " Ni be shafen ba a dawo min da yarinya yamma tayi".Ta fad'a.

       "Toh an gama". Ya fad'a kamar mey shirin yin dariya.

      Bata jira ya sake wata maganar ba ta katse.

        Jealous?  Ya tambayi kansa.

      Yana komawa yace Nasreen ta taso ya maida ita ta'ki ita se anjima,Umma ma hakan tace haka ya 'kyaleta.

     Ba zato ba tsammani hadari ya murtike garin kafin ace mey ruwa ya sauka.Reyhana ta gama 'kulewa takaici ya isheta ita a tunaninta ma yana sane ya'ki dawo da ita.

     Ahmad kuwa ba haka bane a gunsa ya 'kagu ruwan ya tsagaita ya kaita amma shiru 'karfin ruwan ma 'karuwa yake.Nasreen kuwa ko a jikinta se game take a wayar Zainab a haka lokaci yai ta ja, gashi idan ya kira Reyhana baya samunta saboda 'karancin network.

       Har bayan maghrib ana ruwa,Ahmad du yabi ya damu dan yasan Reyhana tana nan ta cika tayi fam.

       Zainab wayar ta amsa daga hannun Nasreen tace zatai mata photo, ba musu ta bata.Tsayawa tayi ta nutsu ta bada attention tana jira a  'kyasta mata.

    Ana d'auka  ta kar'ba taje ta nuna wa Ahmad.

Nasreen

   " Iyye! Toh jeki nuna wa Umma". Ahmad ya fad'a.

      Da sauri taje ta nuna mata itama ,bayan nan Umma ta zuba mata abinci taci ,ba jimawa tayi bacci.

        "Bakai waya da mamanta ba ka fad'a mata?" Umma ta tambaya.

        "Na kira ban sameta ba ba network me kyau". Ya fad'a.

        " Toh ga wayar Zainab ka kira koh zaka semeta kaga shirin ba dad'i".Cewar Umma.

      Wayar Zainab yayi amfani da ita ya kira Reyhana kiran farko ta d'aga.

      "Assalamu Alaykum". Tayi sallama.

      " Waalaikumussalam".Ya amsa.

       "Reyhana it's me". Ya fad'a.

       "Mey zaka fad'a mini kuma?" Ta tambaya cikeda takaici.

       "Na dad'e ina kiranki bana saminki ,kinga yanayin garin baze yiwu mu fito ba". Ahmad ya fad'a.

      " Kana sane kayi hakan ,daga nan ta ri'keta karta baro ta ta dawo". Ta fad'a daga nan tayi hanging.

       Daman yasan za'ai haka bata tsaya ma ta saurare shi ba balle yayi mata maganar tayi Nasreen tayi bacci.

       Reyhana tunda take bata ta'ba kaiwa irin wannan lokacin bata tare da Nasreen ba dan ba inda take iya zuwa ta kwana.

     Su kansu 'yan gidan kowa kewarta yake,tunda Reyhana taga 9pm yayi ta fidda ran dawowarta yau.

      Kowa ya shige d'akinsa itama haka ,ta 'kurawa side da Nasreen take yin bacci se tunanota take,bata jin zata iya yarda Ahmad ya raba ta da Nasreen.

        Wata zuciyarce tace mata ta kira shi,dan haka ta d'auki waya ta kira.Tana tsammanin taji muryar Ahmad amma seta ji muryar mace.

       "Assalamu Alaykum". Aka fad'a.

       Da'kyar ta iya cewa "waalaikumussalm".

      " Uh..ya mance wayar ne a gida".Taji an fad'a.

        Bata ce komai ba ta katse wayar, a zuciyarta tana sa'ke-sa'ke.

         "Zainab?" Ta tambayi kanta.

         Tashi tayi daga zaunen tana ta tunani iri-iri  da ta kalli window ta hangi kamar hasken mota daga gate.'Karasawa wajen tagar tayi ta le'ka ,gani tayi da gaske mota ce ta tsaya lokaci guda zuciyarta ta fad'a mata Ahmad ne.

      Mayafinta tai sauri ta yafa ta fita a sand'a dan garin yayi tsit ga sanyi -sanyi daya ke busawa.

°•°       Ahmad yana gani ruwan ya tsaya around 9:09pm ya d'auka key ,Nasreen da tayi nisa da bacci haka ya d'auketa ya fita.Zainab se bayan ya fita ta lura da phone d'insa daya manta,bayan mintina da fitarsa taji ringing d'in wayar da batai niyyar d'agawa ba seda Umma tace ta d'aga tukun.

        "Azizaty❤" sunan da tagani a screen d'in,dan haka a sanyaye ta d'aga ,da'kyar ta iya tayi bayanin baya nan  and lastly abinda tayi noticing shine an katse wayar.

          Koda ta komo d'aki ba abinda yake mata yawo aka kamar sunan da taga ni a jiki.

       "Har yanzu yana yin waya da ita kenan? hakan yana nufin ze dawo da ita?"

        "Toh ko wata budurwar tashi ce ?" Abinda tayi ta tambaya kenan wanda bata da amsarsu.

      Ahmad koda ya isa gidansu Reyhana wayarsa ya shiga laluba dan ya kira ta amma yaga babu.

         Yana shawarar fitowa daga motar sega Reyhana ta bud'e'kofar gate d'in.  

      AR²💖

     Pls comment,vote and share💋

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣1⃣

Tana daga bakin 'kofar ta'ki 'karasowa gashi fitilar motar ta hasketa.

Fitowa yayi daga motar ya 'karasa har inda take a ransa yana tunanin mey ze fara ce mata.

"Reyhana am sorry ban kawo ta da wuri ba". Ya fad'a .

" Yanzun tana ina?" Ta tambaya.

"Tana cikin mota ,tayi bacci ne".Ya amsa.

Takawa tayi ta 'karasa inda motar take, ta bud'e 'kofar zata d'akko ta ya maida 'kofar ya rufe.

" Ka d'auke hannunka a 'kofar nan".Ta fad'a.

"We need to talk". Ya fad'a.

" Bani da wannan lokacin".Cewar Reyhana tare da watsa masa harara.

"Se yaushe ? Gobe? jibi? Yaushene zaki yarda dani ? Reyhana how many times do I have to tell you,kema kinsan ina nan bazan ta'ba d'aukan wannan tsahon lokacin ban zo ba ,ko bayan da na dawo kece kika hana ni zuwa you know why?" Cikin d'aga murya yake wannan maganar.

"Saboda na rasa abinda zance maki ki yarda dani a wannan lokacin,Umma tayi iya 'ko'karinta tazo amma mey ya faru ? Can you explain that?"

Reyhana shiru tayi ta kasa sake cewa komai ta kau da kanta gefe.

"Why are you punishing me like that ? am begging you please forgive me ,am very sorry!"

Bata ce masa komai ba , kasancewar ya d'auke hannunsa daga 'kofar motar hakan ya bata dama ta bud'e ,Nasreen dake kwance ta kinkimeta ta d'ora a kafad'a.

Bece mata komai ba ya bud'e 'kofar gidan gaba ya ciro jakar Nasreen ya mi'ka mata.

Hannu tasa ta kar'ba ta wuce,seda yaga shigewarta gida ya komo mota ya tafi.

Tana shiga gida ta kwantar da ita ,se lokacin taji sa'ida ba 'karamin dad'i taji ba daya dawo mata da ita.Se lokacin ta samu itama ta kwanta amma kuma se tuna muryar Zainab da taji d'azu take a wayar Ahmad,da wannan tunanin tayi bacci.

*** Washegari da safe bayan Nasreen ta tashi ta soma bawa Reyhana labari.

"Anty Zainab ce ta chanja min kayana". Nasreen ta fad'a.

" Jiya dama kaya ne a jakar ki koh ,shine kika hana a gani".

"Kuma ta d'aukeni a wayar ta". Nasreen ta fad'a.

"Kinci abinci jiyan?" Reyhana ta tambaya.

"Eh Umma ce ta bani ma". Ta amsa.

" Umma?".Reyhana ta tambaya.

"Eh Umman su Uncle ce ".

" Gidan Umma suka je kenan? Toh ko beyi aure ba daman?" Ta fad'a a zuciyarta.

Daga baya Nasreen ta shiga yin wasanta ta bar Reyhana da tunani.

°°°

Su Anty Asma'u yau Sageer ya kaisu gidansu Fatiman sa ,Mommy tana gida tana jiran su dawo taji bayani Abba sam besan da wannan batu ba.

Suna dawowa Mommy ta shiga tambayarsu ya aka 'karke.

"Matsalar daga kece Maryam". Anty Asma'u ta fad'a.

" Kamar ya ?" Ta tambaya tana neman 'karin bayani.

"Mahaifiyar yarinya tayi mana bayanin komai,tace dalilin daya sa suka guji Sageer shine sun samu labari ke bakya yarda 'ya'yanki si auri talakawa ,shiyasa suka ji tsoron abinda ze biyo baya kada daga baya azo ana da an sani".

Shiru Mommy tayi ta kasa cewa komai." Zancen duniya baya 'buya ,shedar da aka yi mata kenan ashe tin sanda tasa Ahmad ya saki Reyhana ". Ta fad'a a zuciyarta.

" Dama wannan dalilin ne yasa suka guji Sageer?"

"Ehyyi haka ta fad'a mana mahaifiyar yarinyar ,kinga kece sila ashe". Wata daga cikin yayyin Mommy ta fad'a.

Mommy kai ta dafe ta kasa cewa komai, tana mey jin haushin kanta ,gashinan halinta yasa d'anta ya shiga cikin wannan halin".

Har sisters d'inta suka tafi ta kasa sakewa,d'aki ta shiga ta zauna tana tuna irin takurawa Ahmad datai a baya ,ta d'ora masa karan tsana har seda tasa ya saki Reyhana,shi Sageer da bema yi auren ba amma ga irin halin da ya shiga shikam Ahmad harda 'ya a gaskiya bata kyauta ba ,batai musu adalci ba.

"Ashe irin halin da mahaifiyarsa ta shiga kenan sanda ya rabu da matarsa ,ya Allah na tuba Allah ka yafemin".

Mommy nadamar abinda tayi ta shiga yi tana dana sani.

Da kanta taje gidansu yarinyar ta fahimtar da ita ,ta fad'a musu bazata 'ki d'iyarsu ba.Se bayan Abba ya dawo da daddare take fad'a masa ,dama shi baida buri kamar Mommy ta gyara halinta kuma yanzu yaji dad'i tunda ta gane kuskurenta na abinda tayi a baya ,dan haka yace mata taje gidansu Ahmad ta bawa Umma ha'kuri.

•••

Kwana biyu Reyhana bata ganin kiran Ahmad haka text d'insa daya saba turo mata shima shiru.Tunani ta fara yi ko lafiya ,wata zuciyar kuma tace koh fushi yake?

" Toh ni nayi masa laifi neh da zeyi fishi ,oho masa".Ta fad'a.

Tashi tayi ta sauka 'kasa ,Walida ce kad'ai a parlorn.

"Walida ina Mommy?" Ta tambaya.

"D'azu ta fita tace bazata dad'e ba". Ta amsa.

" Ina taje?"Ta sake tambaya.

"Nima ban saniba". Ta amsa.

Kai kawai ta gid'a sannan ta shiga kitchen.

°°°

Umma tana parlor taji sallamar Mommy, abinda bata ta'ba tsammani ba kenan.

Iso tayi mata ta shigo parlor Mommy a sanyaye tana mey jin kunyar abubuwan da tayi a baya.

"Ina wuni". Mommy ta gaisheta.

" Lafiya lau ,ya yara?" Umma ta tambaya.

"Yara lafiya lau". Ta amsa.

Shiru ne ya ziyarci parlorn kafin daga bisani Mommy ta fara magana.

" Umman Ahmad, abubuwa da dama sun faru a baya wanda kowa beji dad'insu ba ,ni na zamo silar komai dan Allah ina neman yafiyar ku kiyi ha'kuri da abinda nayi miki inshaAllahu hakan baze sake faruwa ba nasan nayi kuskure ,kiyi ha'kuri".Mommy ta fad'a cikeda nadama.

"Mommyn Reyhana Allah ma ana masa laifi ya yafe ,kuma mu d'an Adam neh muna kuskure fatan mu dama idan minyi laifi mu gano kuskuren mu kuma tunda Allah yasa aka gano hakan an gode Allah ,komai ya wuce dama rayuwa ta gaji haka Allah ya yafe mana baki d'aya".Umma ta fad'a.

" Ameen ,nagode sosai".Ta fad'a.

Zainab da lokacin ta dawo daga school ta shigo parlorn.

"Ina wuni".Ta gaida Mommy cikin rissinawa.

" lafiya lau".Mommy ta amsa.

"Kun dawo kenan". Umma ta fad'a.

" Eh".Ta amsa.

Daga haka ta fita daga parlorn, Umma kuwa bata 'boyewa Mommy ba ta fad'a mata Zainab itace wacce Ahmad ze aura.

Mommy fatan alkairi tayi taja bakinta tayi shiru,seda Ahmad ya shigo shima suka gaisa cikin mitintawa,shima seda ta bashi ha'kuri yace mata ba komai shi dama be ri'ke ta ba.

A yanzu ne Mommy taji sakat da ta nemi yafiyarsu,ranta fyas ta koma gida ta tarar da yaran duka sun dawo kowa yana gida ,hatta Sageer shima yau yana parlor damuwa ta tafi komai ya dedeta.

Sannu da zuwa sukai mata duka yaran bayan ta amsa ta wuce d'aki.Bayan maghrib ta kira Reyhana ta fad'a mata taje gidansu Ahmad.

"Reyhana kema nasan kina..." Bata 'kare ba ta katseta.

"Mommy komai ya wuce dama Allah ya riga daya tsara ba yadda zami ,ki dena tunanin wani abu".Reyhana ta fad'a.

" Toh Nasreen fa zaki fad'a mata yanzu? "Mommy ta tambaya.

" Mommy ni ina ganin a bari nan gaba da kanta zata fahimci hakan".

"Idan yayi aure kina ganin baze kar'bi 'yarshi ba?"

"Mommy ya za'ai ya d'auke ta ,ni bazan yarda ba gaskiya".

" Toh ya zakiyi za'a cigaba da zama a haka ne?,kema wataran ai auren zaki ko wane namiji ne ze ri'ke 'yar da ba ta shi ba?"

Shiru tayi batace komai ba ta tur'bune fuska dan bata so taji ana maganar rabata da Nasreen d'inta.

"Baki ce komai ba?" Mommy ta fad'a.

"Toh Mommy ai bece ze kar'beta ba".

" Lokaci na zuwa,Ummansa ta nuna min wacce ze aura". Mommy ta fad'a.

Wani iri taji jin abinda Mommy ta fad'a, abu de yana shirin tabbata, gaske ne abinda take tsammani Ahmad Zainab ze aura?"

"Kema ya kamata ki kira Umman tashi ki bata ha'kuri ". Mommy ta fad'a.

Se lokacin ta bar tunanin da take ta amsa da " Toh".

Har bayan ta koma d'akinta bata dena tunanin abinda Mommy ta fad'a mata ba.

°°°

Bayan fitar Mommy daga gidan Umma take tambaya Ahmad shirye-shiryen biki ,shi sam baya so take tuna masa.

Duk abinda ta tambayeshi "uhm" kawai yake ce mata, ganin Mommy yasa ya sake karkata wajen Reyhana yana ganin yanzu baida wata matsala gameda dawo da Reyhana tunda Mommy ta ha'kura.

8pm yana d'aki lokacin, number Reyhana yayi dialing ba kamar koyaushe ba yau a kiran farko tayi picking.

"Assalamu Alaykum". Tayi sallama.

" Waalaikumussalam". Ya amsa.

"Nasreen d'in tana kusa?" Ya tambaya.

"A'a". Ta amsa.

" Ok toh shikenan". Ya amsa sannan ya kashe.

Wayar tabi da kallo ta rasa ma mey zata yi,ba abind a ya bata haushi kamar yadda ya kashe maimakon ita ta zama ita ce ta katse.

Washegari kamar yadda Mommy ta fad'a haka tayi, ta kira Umma ta bata ha'kuri.

Tana ajje wayar sega Walida ta shigo d'akin.

"Yaya ga ya Sameer yazo shida sisters d'inshi".

" Yanzun?" Ta tambaya.

"Ehyi suna parlor". Ta amsa.

"Toh kice musu ganinan".Ta amsa.

•••

Yau Ahmad da kanshi ya d'akko Nasreen ze kawo ta gida ,tun daga nesa Nasreen ta hangi motar Sameer.

" Kalli motar Uncle Sameer yazo gidanmu".Ta fad'a tana nuna motar.

"Uncle Sameer?" Ya tambaya.

"Eh Uncle Sameer". Ta fad'a.

Seda suka 'karasa ya lura da Reyhana da take tsaye a 'kofar gidan gefe kuwa Sameer ne suna magana amma besan mey suke cewa ba.

Ita kuwa Reyhana rakiya ta fito koda sisters d'in nashi suka shiga mota Sameer ya tsayar da ita suna magana sega Ahmad.

Yana parking Nasreen tayi sauri ta fito " Ummie yau Uncle ne ya kawo ni!" Ta fad'a tana 'karasawa inda sike.

Sameer se lokacin ya dubi motar ya hangi Ahmad sannan ya dawo da kallonsa kan Reyhana.

"Ahmad, shine mahaifin Nasreen". Reyhana ta fad'a.

Kai ya d'an gid'a sannan ya mayar da kallonsa kan Ahmad.Da Ahmad beyi niyyar fitowa ba amma ganin Sameer yasa ya fito ,a hankali ya tako har inda sike.

AR²💖

Don't forget to tap on the star below, comment and share.Love you all.Tell me if you are ready to see the pic of those three ,four right? Including zee😂

Jasko💕 🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣2⃣

  Yana 'karasawa wajensu ya mi'ka wa Sameer hannu su gaisa,beyi musu ba ya mi'ka masa shima.

       Sede kowa a zuciyarsa da abinda yake tunani.Ita de Reyhana ido ne nata.

         "Sannu koh". Ahmad ya fad'a yana kallon Reyhana                " Yawwa".Ta fad'a ciki-ciki.

       Daga haka ya wuce ya shiga gidan,yana gaisawa da Mommy ya fito dede lokacin Reyhana tana shigowa.

       Kallo d'aya tayi masa ta d'auke idonta ta wuce ta barshi a tsaye ta shige,shima ba tare da yayi magana ba ya fita ,har ya koma gida be dena tunanin Sameer daya gani ba.

        Lokacin daya shiga parlor Umma bata nan se Zainab.

      "Sannu da dawowa ya Ahmad". Ta fad'a.

        " Yawwa".Ya amsa.

         Shiru ne ya ziyarci parlorn kafin daga bisani Zainab ta sake wata maganar.

        "Yaya naga sa'ko na gode". Ta fad'a.

       " Uhm?" Ya tamabaya cikeda neman 'karin bayani.

       "Na agogo da ka bada a bani". Ta fad'a.

        "Uh..ok". Cewar Ahmad yana tunane-tunane.

       " Sadiq?" Ya fad'a a ransa.

       "So ,shine ya bata agogo yace ni na bashi ya bata.." Ya fad'a a ransa.

       "Ka dawo kenan" Umma ta fad'a sanda ta shigo.

        "Eh na dawo". Ya amsa.

         Tashi yayi ya fita ya koma d'akinsa ya d'auki way a ya dannawa Sadiq kira.

       " Na zee".Sadiq ya fad'a yana dariya.

        "Sadiq zan maka wula'kanci". Ahmad ya fad'a.

        " Daga nayi maka abin arzi'ki,dan'kon soyayya na 'kara maku fah".

        "Bana son irin wannan ". Cewar Ahmad kamar yana ganinsa.

        " Kode kishi kake? Gaya mini in baka so nake mata magana sena dena".

        "Ni na saka ka saya mata agogo har kace nina ce ka bata?"

        "Beyi kyau bane agogon?" Sadiq ya tambaya cikeda rainin hankali.

     Ahmad dan tsabar takaici kashe kiran yayi ,ya ajje wayar gefe.Tunani Sameer da Reyhana ne ya sake dawo masa a take ya d'auki wayarsa ya kira ta.

     Seda ya kira sau uku tukun tayi picking.

    "Assalamu Alaykum". Tayi sallama.

     " Waalaikumussalam,nayi sa'a an d'aga min  kira". Ya fad'a bayan ya amsa.

      "Eh ai saboda ban gane number d'in ba shiyasa banyi picking da wuri ba". Ta fad'a.

     " Au dama har yanzu number ta bata chanchanta ayi saving ba?"

       "Eh". Ta amsa a ta'kaice.

         " Toh yanzu ina fatan kingane mey magana?" Ahmad ya tambaya.

           "Ina fatan bazaka sake yimin irin wannan tambayar ba?"

       "Ni na isa". Ahmad ya fad'a.

        "Reyhana wannan dana ganku tare waye?" Ahmad ya tambaya dan sam hankalinsa ya kasa kwanciya.

     "Ina ruwanka dashi?". Reyhana ta fad'a.

      " Kawai inaso na sani neh". Ya fad'a.

      "Toh ,shine wanda zan aura". Ta fad'a cikin rashin nuna damuwa.

       Shiru yayi na d'an lokaci kafin yace." Toh Allah ya tabbatar da alkairi".

      Ita kuwa ta amsa da "Ameen".

     " Nasreen fa?" Ya tambaya.

      "Tana wasa". Ta amsa.

     " Ok,kinji Mommy tace za'a kawo ta wajen Umma tayi kwana biyu koh?"

      "Uhm". Ta amsa duk da kuwa bata san anyi hakan ba.

     " Kinga daganan semi ri'keta kawai idan tanaso". Ahmad ya fad'a.

     "Da fitowa kai fili ka fad'a kana yin aure zaka kar'beta daya fi  kwane-kwanen da kake".Ita kanta batasan zata fad'i haka ba,se da ta fad'a taji haushin kanta kar yace koh kishi take.

       " Ni nace maki zan kar'beta? A ina kika ji ma zanyi aure".Ya tambaya dan besan ta sani ba.

       "Base ka 'boyen ba naji ,wannan be shafen ba kawai de inaso ka sani tunanin ka kar'bi Nasreen ma ka dena dan bazan ta'ba yarda wata tayi mini ri'kon 'yata ba I can do it my self". Ta fad'a.

      "Karki damu tare zakui". Ya fad'a.

       " Mean?"

        "Ga Ummienta ga Auntynta se wadda ta za'ba ai ana tare".

     Yanzun ta gano inda ya nufa aiko da saurinta tace" Allah ya kiyaye".

      "Zamu zama happy family  fa".

       " Bade dani ba chan ka samo wata,ka dena wannan tunanin".

      "For Nasreen". Ahmad ya fad'a.

       " Na fad'a maka ina tare da ita,abinda kake fad'a ma is not possible ".

        " Reyhana kina so kice kin mance da rayuwar mu ta da,bakyaso mu komo...."Be 'kare maganar ba ta katse shi.

      "Maganar baya ta wuce, am hanging". Ta fad'a.

      " Reyhana.. ". Ta katse wayar.

       Wani saban tashin hankali ne ya tunkareta,batajin zata iya zama da kishiya haka bazata yarda a d'auke mata Nasreen d'inta ba koda wuni d'aya ne ,imagine ta shiga yi wai gata ga Zainab a matsayin kishiyarta Ahmad mijinsu.

     " This is not going to happen ". Ta fad'a tare da dafe kai.

       Ko fita parlor ta kasa yi tunani ya addabe ta ji take kamar ta tsala ihu.

°°°      Ita kuwa Zainab koda ta koma d'akinta agogon ta d'akko se kalleshi take tana jin dad'i a ranta." Watoh nauyi yake ji shine ya kasa bani da kansa, my Ahmad kwai miskilanci". Ta fad'a a ranta.                   Ciro shi tayi daga box d'inshi ta saka a hannunta se kalla take tana yaba kyan agogon.

              

                      ***    Kullum abu gaba yake ranakun aure suna matsowa , wata weekend da akai Mommy tasa Sageer ya kai Nasreen gidan Umma tayi kwana biyu lokacin ma Ahmad yayi tafiya.Reyhana a kwana biyunnan kamar tayi musu ihu dan koyaushe tazo kwanciya Nasreen d'inta seta fad'o mata a rai.

      Ahmad kam ta 'bangarensa abu sake 'karfafa yake dan a rana idan beyi mata text sau biyar ba toh yayi sau uku shi da gaske yake so yake ta komo,bama ya tuna cewa ga abinda ke gabatowa.

         Yau wani weekend d'in ya sake zagayowa ,a cikin yaran Anty Ummi ake bikin d'aya daga ciki su Ikram se shirye-shirye sike banda Reyhana da tana zaune koh kayan fita bikin bata sa ba.

       Mommy kuwa tin safe tana gidan uwar biki ,su se yanzu 4pm sike nasu shirin ,Nasreen ma anyi mata kwalliyarta dan yau da ita za'a coz ba dinner bane.

        "Ummie ki shirya dan Allah mu tafi". Nasreen ta fad'a.

        " Ke ki rabi dani ".Reyhana ta fad'a.

         Tana nu'ku-nu'kunta da ta saba a haka ta gama shirin wajen 5pm lokacin, kowa ya gama shiryawa.

        Wannan karan da Walida da Ikram ne sukai anko ,ita Reyhana nata tasa daban.Maroon lace tasa wanda ya amsheta sosai tasa golden gyale.

      Tana shirin fita daga d'akin ta jiyo muryar Sameer a parlor yazo.Shi besan ma da fita bikin ba seda Nasreen take fad'a masa.

      Sam bata so zuwansa ba haka ta sauka suka gaisa.

     " Dukanku zaku fita?" Ya tambayeta.

       "Eh"Ta amsa.

        " Ok idan ba damuwa ai sena kaiku".Ya fad'a.

        "Da ka bari ma". Ta fad'a.

         " Yaya Bassam seya kaimu kawai a motarki ku kuma..."Bata bari Ikram ta 'kare  maganar ba ta galla mata harara.

       "Yes shikenan ma haka za'ai". Sameer ya fad'a.

       Zata sake magana sega kiran Ahmad yana shigowa a,da farko 'kin d'agwa tayi se'a na biyu.

        " Assalamu Alaykum".Tayi sallama          "Waalaikumussalam". Ya amsa.

       " Gani a waje".Ya fad'a.

        "Toh se akai yaya?" Ta tambaya a hankali yadda bazasi jiyo ba dan ta d'an matsa nesa dasu.

      "Nifa ba gunki nazo ba Mommy nazo gaisarwa". Ya fad'a wanda a ransa ba haka bane kuwa itan de ta kawo shi.

       " Mommy kuwa bata nan ba".Ta fad'a.

       "Nasreen fa?" Ya tambaya.

        "Fita zami muma ka bari gobe".Ta fad'a.

         " Aiko shigowa zanyi idan bazaki bari tazo ba".Ya fad'a.

          "A'a gatanan zata zo". Tayi saurin fad'a dan bata so su had'u da Sameer.

        " Am waiting ".Ya fad'a yana dariya dan yadda tayi saurin maganar yasa shi yin dariya.

       " Nasreen".Ta kira ta.

       "Jeki ga Uncle chan yazo kiyi sauri ki dawo". Ta fad'a.

        Da sauri kuwa ta fita tana zumud'i." Uncle kaga nayi kwalliya".Ta fad'a sanda ta 'karasa.

    "Inye! Kinyi kyau sosai ina za'a ?" Ya tambaya.

      "Biki zamu Uncle Sameer yace ze kaimu da Ummiena". Ta fad'a.

        Wani irin haushin Sameer ne ya kamashi " Shine ma ze kaita watoh ,shiyasa bata so ya shiga gidan yanzu Sameer ya fishi a gunta?" Ya tambaya a zuciyarsa.

       "Uncle Ummiena tace nayi sauri na koma ". Nasreen ta fad'a.

      D'an murmushi yayi mata ya gid'a kansa ,da sauri ta koma tana bye-bye ta shige gida.

     Ahmad tunani ya shiga yi ta yadda ze 'bullo da al'amarin,baya jin ze iya jurar ganin Reyhana da wani a mota d'aya ma da sunan za'a kaita biki " Nasan tayi kwalliya ma ,oh shikenan yaga kwalliyanta".Wata zuciyar tasa ta fad'a.

    Tunani yayi ko ya tafi kawai ya huta ganin takaici,a sanyaye har ya bud'e 'kofar motarsa ze tafi wani idea ya zo masa.A take ya saki wani makirin murmushi  da ban ta'ba ganin yayi ba.

      Kalle -kalle ya shiga yi a wajen kamar mey neman wani abu ,can daga  gefe ya gano wata 'kusa doguwa me tsini,da sauuri ya dur'kusa ya d'auka be tsaya a ko ina ba se jikin motar Sameer.Tayar baya ya zage ya chaka mata 'kusar har seda ta sace haka d'ayar ma yabi ya sace na gaba kawai ya bari.Allah yaso ba mutane a layin, ba wanda ya ganshi(😂😂 believe me da'kyar na iya typing d'innan saboda dariya ,bansan Ahmad da irin wannan muguntar ba😂😂😂).

   Komawa yayi jikin motarsa ya jingina harda crossing arms ya basar.

AR²💖

       Don't forget to vote, comment and share pls.

Jasko💕

           

        

            🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣3⃣

    Su Bassam ne suka fara fitowa Ahmad yana tsaye suka wuce a mota,su kuma su Reyhana lokacin suke fitowa da Sameer,Nasreen tana tsakiyarsu.

     Wani irin takaici yaji a ransa ji yake kamar ya sha'ke Sameer.Haka ya daure har suka 'karaso jikin motar Sameer.

      "Shikuma mey yake be tafi ba?" Reyhana ta tambaya a zuciyarta sanda ta lura da Ahmad.

     Kau da kanta tayi tana tsaye jikin motar.Sameer ya sakankance ze bud'e gidan gaba yaga d'anyan aiki.

     Taya tayi da'bas kamar ta shekara da sacewa,se yanzu daya waiwayo ya lura da Ahmad da idonsa akan wayarsa yana tapping kamar besan suna wajen ba.

      Dubawa yayi bayan mortar ya d'auki spare taya ,nan ya sake ganin tayar d'ayan side d'in a sace gashi spare d'in d'aya ne koya sauya ma seya gyara d'ayan.

      Indan Reyhana take ya 'karaso yake fad'a mata abinda ya faru.

     "Toh bari ma sami ko Napep ne". Reyhana ta fad'a.

      " Ummie mun fasa zuwa unguwar?"Nasreen ta tambaya.

        "A'a zamu..." Bata 'karasa ba sega Ahmad tsaye ya 'karaso wajen.

         "Da matsala ne?" Ya tambaya yana kallon Sameer.

      Shiru yayi masa be amsa shi ba se Reyhana ce tace "A'a".

     " Uncle ka kaimu kaga wai motar Uncle ta lalace".Nasreen ta fad'a.

      "Ayya! Do you need help?" Cewar Ahmad yana wa Sameer wani kallon tara saura.

       "No need". Sameer ya fad'a.

         " Ummie mu tafi".Nasreen ta fad'a cikeda 'kosawa.

        Sameer ganin yanda Nasreen ta 'kagu a tafi yasa ya shawarce ta Ahmad ya kaisu dan yasan gyarannan bana yanzu bane.

     "I think it will be better Ahmad ya kaiku kinga lokaci yana 'kurewa and kinga Nasreen ma ta damu". Sameer ya fad'a.

      " Don't worry zami iya jira ma". Reyhana ta fad'a dan ta tura wa Ahmad.

       "Don't mind ,it's ok like that kuje kawai". Sameer ya fad'a.

       " Ummie mije". Nasreen ta fad'a tana jan hannunta.

       "Mije koh". Cewar Ahmad fuskarsa d'auke da murmushi mey nuna fassarori.

      Rolling eyes tayi badan tanaso ba ta tafi zuwa motar shi.Ahmad harda bud'e mata gidan gaba aiko ta'ki shiga ta shige baya,Nasreen kuma ta shiga gaban.

       Ahmad basarwa kawai yayi ya zagaya ya shiga mota,harda wani gyara morror na ciki yana kallo Reyhana da ta kau da kai tana kallon waje.

     Sameer yana tsaye suka bar layin haushi ya isheshi ya daki tayar motar da 'kafa gumm! Ya bige 'kafa." Ahhg!" yai  'yar 'kara.

    Tunda ta fad'i sunan gun da zasu bata sake magana ba, tafiya ake shiru bame cewa komai sai Nasreen jefi-jefi tana wa Ahmad hira.

      Radio yayi turning on channel d'in da sike saurara akai playing wa'kar india "Zaalima"

Jo tere khatir tadpe pehli se hi,kya usse tadpana🎶

O Zaalima o zaalima🎶

(The one who is already longing for you, Why torment him even more? he one who is already misled for you, Why mislead him even more)?

Jo tere ishq mein behka pehle se hi,kya usse behkana🎶

O Zaalima o zaalima🎶

(The one who is already longing for you, Why torment him even more? he one who is already misled for you, Why mislead him even more?)

Ankhein marhaba 🎶

Baatein marhaba🎶

Main sa martaba 🎶

Deewana hua

(Your eyes are great,

Your talks are great I am crazy for you a hundred times over)

Mera na raha🎶

Jabse dil mera🎶

Tere hudn ka🎶

Nishana hua🎶

(My heart ceased to be mine, Since it became a target of your beauty)

Jisku har dhadkan tu ho aise🎶

Dil ko kya dhadkana🎶

O Zaalima o zaalima🎶

(The one whose every heartbeat are you, Why quicken his heartbeat? O cruel one!)

Saasson mein🎶

Teri naz deekiyon ka🎶

Ittar tu ghol de-ghol de🎶

(Mix the perfume of your closeness In my breath)

Main hi kyun 🎶

Ishq Zaahir Karin 🎶

Tu bhi kabhi bol de..bol de🎶

(Why I alone should express my love, You too express your

Le ke jaan hi🎶

Jayega meri🎶

qaatil har tera🎶

Bahana hua🎶

(Your every excuse is a killer, It will definitely kill me)

Tujhse hi shuru🎶

Tujhpe hi khatam🎶

Mere pyar ka🎶

Fasan hua🎶

(The story of my love Commenced and culminated at you)

Tu shamma hai to yaad rakhna🎶

Main bhi hoon parwana 🎶

O Zaalima o zaalima🎶

(If you are a candle, remember that I am a moth (Moth is attracted to the flame) O cruel one!)

Deedar tera milne me baadhi🎶

Chhote meri angdaayi🎶

Tu hi bata de kyun Zaalima🎶

Main kehlaayi🎶

(I pandiculate only after I see you Now you tell me, why I am called cruel?)

          Wa'kar har ya gama playing Reyhana bata kalle shi ba ,ta sani yana sane ya 'karo volume d'in.

      Zaalima (lol)

       Yana parking Nasreen ta fara fita se itama Reyhana tayi saurin yun'kurin bud'e 'kofar Ahmad yai saurin kullewa.

        "Ka bud'e min na fita".Ta fad'a ba tare da ta kalleshi ba.

        " Why are you punishing me like this Reyhana?"Cewar Ahmad bayan ya waigo.

       "Kaide kake punishing kanka".Ta fad'a.

       " How?"Ya tambaya.

        "Please ka bud'en na fice". Ta fad'a.

        " Naji zan bud'e miki amma sekin amsan tambayar da zanyi miki".

       Banza tayi dashi bata ce komai ba ta kauda kai.

      "Do you really love him?" Ya tambayeta.

       D'an murmushi tayi ta kallo shi"Yes i do meyasa zaka damu kanka?"

     "Saboda nasan 'karya ne, ba kya sonshi I can see it in your eyes"

     "Really?"

     "Yes,Reyhana ki dena pretending nasan you still love me ,don't worry bazaki zauna da kishiya ba". Ahmad ya fad'a.

  " Tunda na amsa maka ai yanzu seka bud'e min koh".Ta fad'a.

     "Fine ". Ya fad'a sannan ya bud'e 'kofar ta fita,ko waiwayowa batai ba ta shiga wajen taron.

         Se bayan ta shige tukun ya tafi.

                    ***

   2days later°•°

         Nasreen a kwana biyunnan tana fama da rashin lafiya ,an kaita asibiti amma zazza'bi ya dawo.

      " Reyhana ki kira Ahmad ki fad'a masa yarinyar nan bata da lafiya". Mommy ta fad'a.

      "Mommy ki bari kawai zan maida ita da kaina base an fad'a masa ba".

      " Koh kin kaita da kanki ai ya kamata de ki fad'a masa koh". Cewar Mommy.

      "Toh". Reyhana ta fad'a.

      Tare da Walida suka tafi asibitin Nasreen se kuka take tana shagwa'ba,doctor na duba ta aka ce se an mata 'Karin ruwa zama ya kamasu.

      Hakannan bayan an d'aura mata drip ta kira Ahmad ta fad'a masa.Aikoba jimawa yazo wajen 12pm lokacin.

       " Uncle". Nasreen ta kira sunanshi murya a sanyaye.

      "Sorry kinji  zaki sami sau'ki". Ya fad'a yana dafa goshinta da zazza'bin ya soma sauka.

       "Meyasa baki fad'a mini da wuri ba?" Ya tambaya yana kallon Reyhana.

       Shiru tayi bata amsa shi ba sema phone d'inta data d'auko a jaka ta fara tapping.

         Ahmad ganin tayi masa banza bata yi masa magana ba ya tura mata da text.

    Ana yi miki magana kin'ki amsawa why?

Se lokacin ta d'ago ta kalleshi sannan ta kauda kanta.

         Gefe ya samu ya zauna ya kira Umma yake fad'a mata.Tashi yayi ya fita bata san ina zaije ba shima be fad'a mata ba.

      Fruit ya siya masu da gasashshen chicken se takeaway da juice ya dawo ,fuskar daya gani a room d'in yasa ya had'e rai lokaci guda.

         "" Wannan banzan meya ke yi anan?"Ahmad ya fad'a a zuciyarsa.

        'Karasowa yayi ciki ya samu waje ya ajje ledar kayan sanna yaja gefe ya tsaya,kallon -kallon suka shiga yi da Sameer da take opposite dashi ,Reyhana kuma ta zaune gefen Nasreen da ta ri'ke mata hannu karta barta .

      Ahmad wata uwar harara ya watsa masa  shima Sameer ya mayar masa,yau ko gaisawar basi ba.

     Takawa Ahmad ya yi har kusa da Nasreen ya shafa mata kai yana mata sannu,ta gefen ido kuwa yana kallon Sameer yana so ya nuna  shine fa mey 'ya.Itama Reyhana ta gano haka amma setai kamar bata gansu ba.

         Bayan kamar 20min sega su Mommy da Abba kusan dukansu banda Sageer da Ikram.Suma shagwa'bar tayi ta musu tana nuna musu hannunta da aka saka mata carnular.

       Sameer ne ya fara tafiya kafin Ahmad dan se wajen 3pm hakan ma bawai ya tafi duka bane su Umma ya tafi d'aukowa.Mommy ce ta bud'e ledar taga siyayyar daya yo musu ta bawa Nasreen,Reyhana kuwa 'kinci tayi ,abincin da su mommy suka kawo shi ta ci.

         Reyhana da batai tsammanin ganin Zainab a asibitin ba tasha mamaki ganin su tare da Umma ,a zuciyarta tana fad'in."Haka ta girma yarinyarnan?"

      Kamar bazata amsa gaisuwa ba Reyhana tace "Lafiya".Bayan Zainab ta gaisheta.

         Ahmad yana kallonta ya gano sauyin fuskarta suna had'a ido ta watsa  masa harara ,shi dariya ma ta bashi kai de basarwa yayi.

      " Anty Zainab anan zaki sauna?" Nasreen ta tambaya.

       Murmushi tayi mata ba tare da ta amsa ba.

     "Ai ba kwana zami anan ba anjima zamu tafi".Reyhanana ta fad'a tana kallon Zainab.

       " Kijimin mata kallonnan na miye kuma?"Zainab ta fad'a a ranta.

       Da Umma suka tashi zasi tafi Nasreen tace ita  a lalle se Zainab ta zauna,haushi du ya ishi Reyhana .Mommy tace toh su sesi ragewa Umma hanya anjima Zainab sesu tafi da Ahmad.

      Haka kuwa aka yi Umma tabi su Mommy ,aka bari daga Zainab ,Reyhana se Ahmad.Shuru ne ya ziyarci d'akin bame magana itama Nasreen d'in ta gaji.

     Zainab a gefenta na dama Reyhana a hagu Ahmad yana daga gefe.

        Lokacin maghrib ya yi Ahmad ya fita  sallah ,bashi ya dawo ba se bayan isha'i.Yana shigowa yaga doctor yazo ,lokacin za'a sallamesu.Duk wani charges Ahmad ne ya biya ,sannan suka fito tafiya.

      Ya d'auki Nasreen da ta langa'be a kafad'a."Ni ba a gaba zan zauna ba ,a baya nakeson kwantawa ".Nasreen ta fad'a lokacin da suka 'karaso jikin motar.

        Bayan ya bud'e ya kwantar da ita tukun ya bud'e nashi gidan gaban.A tsaye ya gansu kowacce bata Shiga ba  ,suna daga bayan,kowacce a ranta tana tunanin mey shiga gidan gaba.

     " Ko a zuwanma a gidan gaba ta zauna ?da alama yanzun ma so take ta zauna ,Chab! aiko sede ta zauna a baya".Cewar Zainab.

     "Rawar jiki kike ki Shiga gaba? aiko sorrynki gaba nake dake yarinya duk da ba son shiga nake ba yau sena zauna let me see tsakanin nida ke waya fi damuwa da ita ,naga duk wannan kurarin da ake a iya ina ya tsaya son". Reyhana ta fad'a tana matsawa gaba.

      " What is she trying to do ? Matar nan itace mey 'kin shiga gaba amma yanzu ,she is looking for trouble ,wait itama Zainab shigar take so tayi?"Ya tambayi kansa lokacin da yaga itama Zainab tana matsowa.

AR²💖               1807+ words I try koh? ,dan dan Zee &Rey WWE RAW🔥 😹         Don't forget to tap on that Star below,comment and share pls.love u all💋

Jasko 💕      

   

                       🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

🅿 3⃣4⃣

    Ahmad ya kasa cewa komai yana kallonsu,Reyhana wani kallon tara saura tayi mata tun daga sama har 'kasa sannan ta 'karasa bakin 'kofar ta bud'e ta shige cikeda ta'kama.

     Zainab baki ta saki taga 'karfa-'karfa,chak ta tsaya batada alamar shiga motar.

     Ahmad ne yai mata alama ta shiga baya lokacin da suka had'a ido ,seda taci 1min tukun ta shiga baya ta ra'be gefe haushi ya isheta.

    Shiru kowa yayi a ransu kowa da sa'ke-sa'ken da yake. A haka har aka 'karasa gidansu Reyhana ,yana parking ta fito daga motar ko takan Nasreen bata bi ba tasan dole ze d'akkota kuma da biyu tayi hakan dan ta sake ba'kanta wa Zainab.

       Bayan ya fito ya bud'e gidan baya ya d'akko ta ,tayi nisa ma da bacci.

      Zainab lokacin da taga yana fitowa daga gidan ta kauda kanta ta sake had'e rai,tunda ya shigo motar ya fiskanci hakan.

      "Ki dawo nan gaba". Ya fad'a.

       Yitai kamar bata ji ba seda ya sake maimaitawa tace.

        " A'a nan ma yayi".Ta fad'a muryarta ciki-ciki.

        "Zainab ki dawo nace".Ya fad'a wannan karan ya waiwayo.

        Bata sake cewa komai ba ta fita ta koma gaba tare da rufo 'kofar da 'karfi.

       " Fishi kike da Antyn taki?" Ahmad ya fad'a bayan ta shigo.

       "Anty ta". Ta maimaita tare da ta'be baki.

       "Ehmana ko kin mata ita Antynki ce?"

        Shiru tayi bata sake wata maganar ba tana kallon waje har suka  isa gida.

     Tunda suka shiga gida ta shige d'akinta takaici ya isheta.

                  ***

      Reyhana bayan tafiyarsa ta kai Nasreen d'aki ta kwantar da ita,tunani ta shiga yi na abinda ya faru,murmushi ta tsinci kanta tana yi ."Ko zata koma gaban oho mata".Ta fad'a a zuciyarta.

       Tana wannan batun sega kiran Ahmad ya shigo wayarta,yau a karan farko tayi picking.

      "Assalamu Alaykum". Tayi sallama.

       " Waalaikumussalam"Ya fad'a.

        "Ya jikin nata?" Ya tambaya.

         "Da sau'ki har yanzu bacci take". Ta fad'a.

          "Ok,toh idan ta tashi karki manta ki bata magani".Ya fad'a.

          " You don't have to mention dan bazan manta ba".Reyhana ta fad'a cikin sanyin murya.

      "Kina so kice kin fini damuwa da ita kenan" Ahmad ya fad'a.

       "Toh wa zai had'a ma". Cewar Reyhana.

        " Haka de kika ce ,itama ai ta sani".Ya fad'a.

        "Cabb! Waya fad'a ma nide kullum kodayaushe muna tare ko bacci baya raba mu".

      "Kwana nawa ne zan d'auke ta". Ahmad ya fad'a.

      " Ba inda zata".Reyhana ta fad'a.

       "In kina so ki zauna tare da ita seki biyo ta". Ya fad'a.

       "Hmm".

       " Hmm meh?"Ya tambaya.

        "Babu ,am hanging now". Ta fad'a.

       "So kike ki wayance de ,shikenan toh goodnight". Ya fad'a.

        " Ok ,ka gaida Umma". Ta fad'a.

         "Kinyi mantuwa". Ya fad'a.

          " Name fa?" Ta tambaya tana neman bayani.

          "Baki ce kina gaida Zainab ba". Ya fad'a.

           " Goodnight ". Ta fad'a tare da katse wayar.

      Hakan yasa shin yin dariya ,text ya tura mata tukun ya ajje wayar gefe.

       Ta ajje wayarta taji sa'kon text tana dubawa taga Ahmad ne ya turo.

        

"Your eyes are great, your talks are great I am crazy for you hundred times over I love you very much,goodnight Azizaty❤"

      A take ta soma blushing ta kasa dena maimaita karanta text d'in,har ta kwanta text d'in yana mata yawa a kai.

   °°°

    Washegari Nasreen ta samu 'kwarin jiki  sosai ,bayan tasha magani ta takura Reyhana ta kira mata Uncle dan ya kira da safe lokacin tana bacci.

     Numbern sa tayi dialing shiru har ta katse beyi picking ba,na biyu ma haka be d'aga ba.

     Ahmad kuwa lokacin suna hanya ze kai Zainab makaranta sannan ya wuce aiki ,ya tsaya a gidan mai be jima da fita daga motar ba sega kiran Reyhana.

     Zainab tana le'kawa ganin "Azizaty❤" ta share kiran koda Ahmad ya dawo bata fad'a masa an kira ba shi kuma be samu ya duba wayar ba suka tafi.

       Reyhana jitai ba dad'i ganin lokaci ya sake ja be ko kira ba,tayi tsammanin kiransa amma taji shiru dan haka itama bata sake kira ba.

      Se wajen 12pm ya lura da missed call d'in,ba 'bata lokaci yayi calling back,se a karo na biyu tayi picking.

       "Assalamu Alaykum".

        " Waalaikumussalam"Ya amsa.

         "Sorry kin kira bana kusa seyanzu naga kiran" Ya fad'a.

        "Tun fa d'azu kusan 3hr baka gani ba?"

         "I am sorry Ummien Nasreen kinji ai min afuwa". Ya fad'a.

        " Ga Nasreen zaku gaisa". Ta fad'a.

        "Toh ai baki ce kin ha'kura ba".

        "Naji toh shikenan". Ta fad'a.

        " Thank you".

        Nasreen tasa wa wayar a kunne"Ga Uncle ". Reyhana ta fad'a.

         " Uncle". Ta kira sunanshi.

           "Nasreen ya jikinki ?" Ya tambaya.

            "Da sau'ki Uncle yaushe zaka zo?" Ta tambaya.

          "Anjima zanzo ,kinsha magani?"

          "Eh". Ta amsa.

            " Yawwa toh mey kike so na kawo maki?"

        "Chocolate". Ta fad'a.

         " Good girl,zan kawo miki kinji ,ina Ummie?"

        "Gata nan". Ta fad'a.

        " Yawwa toh bata wayar".

       Mi'ka mata wayar tayi ,Reyhana ta amsa.Ahmad ya cigaba da janta da surutu.

     •••

   Waya se abinda ya 'karu dan yanzu Reyhana bata 'kin d'aga wayarsa gashi ta dena jin haushin 'kwata-'kwata hira suke yi sosai,da kanta ma kira take ta bawa Nasreen su gaisa bayan nan kuma sesu 'bige da waya.

                   ***   3 weeks later biki yana ta matsowa a yanzun Ahmad ya damu sosai dan ko zama be fiya yi a parlour ba balle Umma tayi masa zancen bikin a yanzu ana maganar lefe ,tun jiya Umma take masa maganar amma ya'ki tsayawa ma suyi maganar.

        Yau da ta gaji ta tare shi har d'aki ta soma yi masa maganar.

        "Kai shikenan kuma dan ance yarinyarnan 'yar uwakka ce kuma seka ke haka? Cha a kai ma auren bazawara ne?"

       "Umma zan fa bada ni kud'i kawai zan bada ba ruwana da wani lefe".Ahmad ya fad'a.

      " Toh har sai yaushe? Kud'in base a bayar da wuri ba".Umma ta fad'a.

      "Kaga yarinyarnan taje gida mey kake so tace da iyayenta? Ko kuwa so kake a d'aga bikin?"

      "Dama ai yakamata a d'aga". Ahmad ya fad'a.

      " Aiko baza'a d'aga ba ,mey make jira ? Gida ne ka gama kuma mey ya rage bazan zama mey baki biyu ba".

     "Amma Umm.." Be 'kare maganar ba ta katse shi.

      "Idan ma abinda kake tunanin gaske neh toh kama dena tuananin haka". Umma ta fad'a.

      " Mey fa?" Ya tambaya.

       "Reyhana, idan tunani kake ka dawo da ita ni bazan hana ka ba amma ba a wannan lokacin ba kaima kasani da farko kenan kuma abu na biyu shine inde Zainab bata son zama gida d'aya da ita ba bazaka had'asu ba".

       Shiru Ahmad yayi yana jin abinda Umma take fad'a shi sam ba haka yake so ba ,baida wacce tafi Reyhana a gunsa ita da Nasreen kawai yake burin yaga sun komo gareshi.

         "Kaji de mey nace maka". Umma ta fad'a.

         Daga haka ta tashi ta barshi yana ta tunane-tunane.

                          ***

  Reyhana a yanzu tana son komawa gidan Ahmad d'inta ,abu biyu ke bata tsoro shine aurensa da Zainab ga Sameer batasan ya zatai dashi ba.

      Yanzun ma tana d'aki tana tsammanin kiransa taji ya Umma zata d'auki abun dan cayai mata ze fad'a wa Umma amma ya kasa.

      A sanyaye ya d'auka waya ya kirata.

      " Assalamu Alaykum".Ta fad'a bayan ta d'aga.

       "Waalaikumussalam". Ya amsa.

       " Kayi magana da Umma".Ta tambaya.

     Shiru yayi bece komai ba tana tunanin ta ze soma bayani.

        "Reyhana..". Be 'karasa ba yayi shiru.

         " Ahmad i understand everything, na fad'a maka wannan ba abune mey sau'ki ba dole nasan Umma bazata ji dad'in haka ba kuma bazan so mu 'bata mata rai ba ,ina ganin kawai mu ha'kura".Ta fad'a.

       "No kidena fad'ar haka ". Cewar Ahmad.

       "Haka ne mana ,idan nayi haka banyi wa Zainab adalci ba d.."

      "Stop talking like this na fad'a maki,baza a kai wannan tsahon lokacin ba tare da kun kasance dani ba".

      " Mey kike tunanin yi?" Ta tambaya.

       "Kafin.."

       "Kafin ka auri Zainab na komo gidanka ? No bazan iya yin haka ba mey kake so Umma ta d'aukeni ? "

        Shiru yayi bece komai ba a zuciyarsa yana ta sa'ke-sa'ke,kowa da abinda yake tunani.Har suka 'kare wayar ba wani solution.

        Tunani ta shiga yi ko kawai ta ha'kura ta auri Sameer a huta.

AR²💖

       Don't forget to comment and vote.love you all💋

Pls share.

Jasko💕

         

  

        

       

         🎍 *ARZI'KI RABO*🎍

*WRITTEN BY DIJENSY*

*WATTPAD @dijensy*

*Last page*

🅿 3⃣5⃣

    *Not edited*

Bayan kwana biyu Zainab ta dawo,jikinta a yanzu ya fara sanyi da auren wannan karan ko fad'a masu batai ba zata dawo kawai ganinta Umma tayi.

Shi Ahmad yana aiki daga nan d'in ma seya biya gidansu Reyhana tukun ze komo gida.Tunda tayi tafiya Zaria befi sau uku sukai waya ba satinta d'aya a can.

°°° Reyhana tana jin sanda ya shigo parlour amma bata sauka 'kasa ba se Nasreen ce taje.Koda ya kirata 'kin picking tayi har ya tafi bata sakko ba.

Tana zaune Nasreen ta shigo tana murna hannunta ri'ke da leda "Uncle ya bani". Ta fad'a tana nuna mata.

" Toh naji ". Reyhana ta fad'a.

Kayan ciye-ciye ne kala-kala ya siyo mata.

•••

Koda ya koma gida d'akinsa ya shige besan ma Zainab ta dawo ba.

Yana zaune sega kiran Imran." Aboki yane?" Cewar Imran.

"Ya kua". Ahmad ya fad'a.

" Da matsala ne?" Ya tambaya.

"Kaima ka sani ai"Ahmad ya fad'a.

" Reyhanan de?"

"Ehyi ita".Ya amsa.

" Kaima ka bari se bayan wannan auren tukun ".

" For how long?"

"Duk yanda ya kai mana, kai da ka ha'kura da Zainab d'inka ma". Imran ya fad'a.

" Kai baza ka gane ba,tunda mike dake na ta'ba ce maka ina son Zainab? Imran nifa bana son yarinyarnan kawai de saboda Umma shiyasa zan ha'kura". Ahmad ya fad'a.

Zainab duk wannan zancen dayake yi a kunnenta ,tana tsaye jikin 'kofar d'akin sa.Umma ce ta sata kira mata shi ,zuwan da tayi ta riskeshi yana waya kunnenta ya jiyo mata wannan maganar.

Gwiwoyinta sinyi mata li'kis da 'kyar ta iya komawa d'akinta.Kuka mara sauti ta zauna ta shiga yi ba 'ka'k'kautawa.

"For all this long dama Ahmad be ta'ba sonta ba ,so Umma ce tasa ze aureta ashe ? Shiyasa baya nuna damuwa dani ". Abinda take fad'a a ranta kenan.

Umma jin shiru yasa ta biyo sawu ,Zainab na hango tahowar Umma tayi saurin goge hawayen ta.

" Zainab, naji shiru koh baya nan?" Ta tambaya.

"Yana.. yana zuwa". Ta fad'a.

Gid'a kai tayi tukun Umma ta fita ta koma d'akinta. Zainab sake goge fuskarta tayi sannan ta fita taje ta kira shi ,sam bata nuna alamar wani abu ba kuma shima be gano hakan ba.

D'akinta ta koma ta shiga wani sabon kukan ,tana son Ahmad sosai ba 'karamin ciwo abin yai mata ba duk wannan abun da take ashe shirmenta take,bata ga amfanin auren wanda bata so ba.Ta fad'a a ranta.

*** Sameer yau da yamma yazo gidansu Reyhana, da kanta ta kira shi tace tana so siyi magana a ranta ta gama yanke shawarar fad'a masa zata aureshi.

Bayan yazo sun gaisa da Mommy ta tashi ta bar musu parlourn Nasreen dama bata dawo daga school ba.

Bayan sun gaisa Reyhana tayi gyaran murya kafin ta soma magana.

"Ahma..uh..Sameer". Ta kira sunansa shaf ta mance ta kira shi da Ahmad.

" Dama ina so na fad'a maka shawarar da na yanke,uhn..Sameer na..."Be bari ta 'karasa ba ya katse ta.

"Reyhana base kinyi bayani ba na gano abinda kike so kice,na dad'e da fahimtar hakan ni kaina tun sanda naga Ahmad.."

"Sameer ba haka nake nufi ba n.."

"Karki damu kanki ,kada ki manta na fad'a miki duk abinda kike so shi nake so ,Ahmad shi yafi kowa dacewa dake ,ya kamata ku kasance tare".

Shiru tayi ta zama speechless dan bata zaci haka ba daga wajen sa.

"Amma Sameer.."

"Is ok don't worry,Ahmad is the best husband for you I know you still love each other ,you have second chance to be together Reyhana,don't worry about me am really happy for you".

Tausayinsa ne ya kamata sosai Sameer is a very kind person duk wani abu da zatai baya ganin laifinta kuma tasan yana sonta sosai and duk wani abunda take so shi yake so.

" I am so sorry Sameer ". Ta fad'a.

" Don't worry".Ya fad'a.

"Thank you".

" Don't mention". Ya fad'a fuskarsa d'auke da murmushi.

Itama murmushin ta mayar masa tana jin tausayinsa.

***

•°• 4 month later•°•

Reyhana ce zaune a parlour tana ri'ke da wayarta tana chatting da Ikram.

Reyhana: "Ke wannan status d'in fa ? 'boye fuskar mijin naki kike kar wasu siyi miki snatching"

Ikram: " Hhh ,shima haka yake min bara kiga"

Reyhana: "Iyye ,Amaryar Sameer.

Ikram: "Kinji yaya ,kema Amaryar Ahmad"

Reyhana: "Au ramawa zaki"

Ikram:"Toh ku ina naku pic d'in,a turon na gani".

Reyhana: " Kizo har gida tukun"

Ikram: "Nafi kowa son hakan"

Reyhana: "Sorrynki yarinya se nan da 3yrs😝"

Ikram:"Chabb! Nan da wani watan zan duro 9ja"

Reyhana:"Kiyu biyayya se a kawo ki"

Ikram: "Ha ,ina Nasreen 'yan mata?"

Reyhana: "Tana school"

Ikram: "Se ke kad'ai,gaskia ya kamata ayi mata 'kani da wuri"

Reyhana: "Kede mike jira yarinya 😝 da twins zaki duro 9ja"

Ikram:"Hhhh lokacin kinada 4 koh😋"

Reyhana: "Kin manta 7😎"

Ikram: "Lol"

Ikram: "Am waiting"

Reyhana: "What?"

Ikram:"Naku pic d'in"

Reyhana: "Ok"

Ikram: "😱 kinganki kuwa"

Reyhana: "Mey?"

Ikram: "Kinyi kumatu anya😂😝"

Reyhana:"Zan bige ki"

Ikram:"Ummien boy zan ke kiranki yanzu"

Reyhana"Ke kuma Maman girl"

Ikram:"Hehe wayaga"

Reyhana: "Hahaha kallo ze koma kanki yarinya"

Ikram: "Jeki girki kar habeebinki ya dawo💕"

Reyhana: "Ke kai"

Ikram: "Ai tare mike girkin"

Reyhana: "Iyye lovayya😻"

Ikram:"Ha"

Reyhana:"Toh ki gaisheshi inya dawo"

Ikram:"Ok bye "

Daga haka Reyhana ta sauka daga chat d'in ta shiga kitchen domin yi musu girkin rana.

A wata hud'unnan abubuwa da dama sun faru,Zainab da kanta ta fad'a wa Ahmad ta janye aurensa da Umma ta sani ba yadda batai da ita ba suma yayyin Umma da mahaifiyarta suka sata a gama kowa yana mamakin 'kinta na auren Ahmad da suka isheta ma kuka take sa musu haka ba yadda suka iya dole aka rabu da ita suka ha'kura ,Ahmad dama haka yake so. Ta koma Zaria ma dan ta kammala karatunta.

Shi kuwa Sameer ya koma wajen Ikram a kai sa'a ta amince,lokaci d'aya aka yi aurensu,Sameer da Ikram,Ahmad da Reyhana. Sameer ana yin biki suka tafi America,yau wata uku kenan da yin bikin su duka.

Nasreen 'yar Ummienta da Papa(sunan da take kiran Ahmad kenan).

Sadiq abokin Ahmad shima sati biyu kenan da yin aurensa ,se Imran shima yana shiri.

2:30pm,Reyhana ta gama girkinta ta sake gyara fuskarta se turare da ta fesa mey taushin 'kamshi tayi kyau sosai dark blue d'in doguwar riga mey dogon hannu tasa se veil 'karami Pink purple data yafa.

Not more than 10min sega Ahmad ya dawo,kafin ya dannan door bell ta bud'e 'kofar,tsaya wa yayi fuskarsa d'auke da murmushi yana kallonta.

"Come in". Ta fad'a cikin sanyayyar muryarta.

Yana shigowa ta kar'bi briefcase daya ri'ko.

" Welcome back ".Ta fad'a tare da hugging d'insa,shima yayi hugging back.

" My pretty cute Azizaty ".Ya fad'a.

" Kinganki kua". Ya fad'a bayan sunyi breaking hug d'in.

"Kamar karna dena kallonki". Ya fad'a.

" Toh yanzu mije kayi shower,kaci abinci".

"As you said". Ya fad'a.

Bayan kamar 20min ya fito sanye da T shirt fara se jeans blue,tana dinning table ta gama jere abincin.

Kujera taja baya ya zauna tukun ta zuba abincin a plate d'aya." Kinci abincin ?"

"A'a". Ta amsa.

"Har 3 fah ,Allah sarki my Azizaty nasan ni kike jira"

"Bana so kike zama da yunwa fa". Ya fad'a.

" Don't worry ai bana jin yunwa tunda ba da wuri nayi breakfast ba". Ta fad'a.

"Iyye wannan baccin irin na da ne ya dawo koh".

" A'a"Ta amsa tana dariya.

"Zama de mu gano ki gama 'boye-'boyen". Ya fad'a.

" Toh yanzu de muci abinci ". Ta fad'a tare da saka musu spoon biyu a plate d'in.

Basu dad'e da gama cin abincin ba suka ji knock ,Ahmad ne yaje bud'e 'kofar ,ga mamakinsa yaga Nasreen tsaye ita da Nanny d'in makarantarsu.

" Nasreen 'karfe nawa har kin dawo meya faru ?"Ya tambaya.

Tsaye tayi tana kallonsa bata ce komai ba tayi wani kalar tausayi.

"Bata da lafiya tana ta kuka shine aka ce na kawo ta gida". Nanny d'in ta fad'a

" Toh mungode".Ya fad'a tare da ri'ko hannun Nasreen suka shigo ciki.

Reyhana se yanzu ta 'karaso taga Nasreen.

"Mey zan gani ,ita wannan mey take yi a gida 'karfe 3?"

"Wai bata da lafiya".Ya amsa.

" Zonan".Reyhana ta fad'a.

'Karasawa tayi India Reyhana take ,Reyhana ta d'ora hannunta a wuyanta taji ba zafi .

"Anya ba 'karya kike ba".Ta fad'a.

Girgiza kai tayi ta sunkuya ta'ki d'agowa su had'a ido dan dariya ce ma'kale a fuskarta bataso su gano ta.

" D'ago kanki mey kike 'boyewa?".Reyhana ta tambaya tare da d,'ago ha'barta.

Aiko tana d'ago ta ta saki dariya tana ja da baya."Dama wayo nayi wa Anty nace banida lafiya cikina yana ciwo tace a kawo ni gida".Nasreen ta fad'a tana dariya.

Ahmad ya ri'ke baki tsaye yana kallonta ,ya rasa wannan iron wayo na Nasreen 'karama da ita ta iya tsara babba.

"Aiko sekin koma yanzunnan". Reyhana ta fad'a.

" A'a".Ta ma'kale kafad'a kamar zatai kuka.

"Zonan". Ta fad'a.

" A'a rabu da ita ,abinda ta riga da ta tafi".Ahmad ya fad'a.

"Ni da kaina zan maida ta". Cewar Reyhana.

" Dan Allah ki barni bana so na koma".Ta fad'a.

"Ki barta kawai tunda ta riga da ta dawo,karki sake kinji". Ya fad'a.

Kai Nasreen ta girgiza tare da fad'in." Toh Papa".

Gefe ta ma'kale tana yiwa Reyhana gwalo."Sekije ki cire uniform d'in".Reyhana ta fad'a ta bar wajen.

Ba musu ta tafi d'akinta taje ta kwa'be kayan ta zira skirt da shirt ta fito da kayan wasanta dama abinda take so kenan.

"Ai kya samu kici abinci tukun ko".Reyhana ta fad'a.

" Bana jin yunwa".Ta fad'a.

°°° Bayan maghrib Ahmad ya dawo daga masjid,Nasreen tana ri'ke da wayarsa se game take tun sanda ya fita.

"Ki tashi kiyi Sallah na fad'a miki". Reyhana ta fad'a sanda ta fito parlour.

" Tashi kinji idan kin iddar seki cigaba da game d'in".Ahmad ya fad'a.

"Se a d'auken photo ko?" Nasreen ta fad'a.

"Eh". Ya amsa.

Da sauri-sauri tai alwala ta zira hijab tayi sallar sannan ta dawo ta zauna.

" Papa ayi mini".Ta fad'a.

"Toh zo ai miki". Ya fad'a

Matsawa tayi aka kyasta mata ,sukai tare daga baya Reyhana ma tazo.

" Banda me kuma". Reyhana ta fad'a.

"Ummie dani za'ai"

"No ke ba mey gudun makaranta ba,matsa min". Reyhana ta matsar da it's gefe.

" Rabu da Ummie zatai sake kinji". Cesar Ahmad.

Reyhana ce ta kyasta musu iya su biyu kowannensu fuskarsa d murmushi.

*Alhamdulillah,a nan na kawo 'karshen littafinnan AR💖 ,ina mi'ka godiya ta zuwa gareku masu voting, readers 'boyayyu thank you very much.Ina godewa Allah daya bani ikon kammalawa,ina fatan an amfana da abinda ke ciki.*

Nobody is perfect

Goodbye in this story, till we met again in another story .....

Jasko💕                            

End of current loaded text.