Ni Da Yaya Sadiq Book 1 Complete Hausa Novel
By M Shakur★ Gold
Book Page

Ni Da Yaya Sadiq Book 1 Complete Hausa Novel

Author: M Shakur★ Gold
Paragraphs: 1854
Starting position: 1
Reading position: 1 / 1854
Listen Mode
Login and upgrade to premium to unlock listening.
Reader Top
Ad slot ready: reader_top

     NI DA YAYA SADEEQ                 Shor love story 2021 typing free book

Story & Writer by        Siddiqahtul Khairy Yahya                        (S beauty ✍️)

 Da sunan Allah me rahama me jinkai ban kir-kiri littafin NI DA YAYA SADEEQ saboda wani ko wata ba nayi ne saboda na kawo gyara a cikin Al'umma ta hanyar rubuta domin fadakar dasu nishadantar dasu gami da iliman tar wa

Kasan cewar shine book dina na farko sai kunyi hakuri da errors typing din da zaku dunga cin karo dasu

Kuyi min comment Saboda tahanyar ne zaku bayyana min farin cikin ku game da wannan littafin

GARGADI Ban yarda wani ko wata su juya min littafi ba duk Wanda yai bada izini na ba ban yafe ba

              SADAUKARWA

Wannan littafin sadaukarwa ne ga mahaifiya ta Hajiya Rukayya Muhammad (kamfani)                                *P.W.A*📚✍️ _________________________________                    

 Chapter 01

بسم الله الرحمن الرحيم

_______A zaune nike a kan tabarma cikin baranda isaka na kad'a bishiyar mangwaron da ke tsakiyar gidan mu Ganyen ta na fad'owa 'kasa gunin burgewa. Dambu ne a gabana cikin wata 'yar samira inaci ina sud'e yatsun hannu na saboda dambun yayi min dad'i kamar kar ya'kare Kawata Ladiyo. Ce ta shigo gidan mu hannunun ta rike da goshin ta yana zubar da jini koda na d'aga kaina na kalle ta bance mata komai ba Na maida kaina kasa na cigaba da cin dambu na, Saida na cinye dambun tas Sannan na kora da ruwa, Baki na bud'e iya 'karfi na Nayi wata katuwar gyatsa tarashin mutunci, Irin wacce idan yaya Sadee'k ya na guri nayi yake buge min baki.

Kallan Ladiyo nayi Na ta'be baki nace "Ladiyo lafiya kika zo ki ka tsaya min a kai ko aiko ki a kayi?".

Ladiyo. Da Dama jira take in tambaye ta, saboda tasan in bani na tambayeta ba tana iya fad'a min na bata kunya tana kuka take fad'a min abinda ya faru. Tace "Kinsan yaron da jiya muka barar mai da markad'e ai Dazun Umma ta ta aike ni gidan su Zulai anso mata kud'in zubin a dashi,bayan na anso kud'in na had'u da yaron akan hanyata ta dawowa Ni bansani ba a she nan ne layin da yaron yake, shine yayi taimin ruwan duwatsu tako ina har wasu abokan sa suka taya sa Allah ya temake ni Baban Ramma Yazo wucewa sai yaga abinda ke faruwa. nan take ya tsawatar musu shine suka 'kyale ni, amma wallahi inaga da sai dai a d'auko gawa ta saboda jifan da suka min bana wasa bane, Ko gida banje ba nayo nan saboda ya bani sa'ko". Yace in fad'a miki "wallahi kema saiya fasa miki goshi".

Nace "Kan uban_nan yanzu dama acikin' kauyen nan a kwai wanda zaija dani har ni zaice zai fasama goshi To wallahi kaf kauyen Dande. Banga mai fasamin goshi ba amma tunda yace haka muzuba ni dashi shege ka fasa kafin ya fasa min ni zan fara zuwa gidan su in fasa na Babar sa inya so kinga yaji dad'in fasa min nawa da hujja".

Inna da fitowar ta kenan da Buta ri'ke a hannun ta da alama daga ban d'aki ta fito Tace "ke da wa siddi'ka. Ki ke yin wannan ashar d'in kamar bakya zuwa islamiya"? .

Nace "yo Inna bakiga Ladiyo bane?".sai alokacin Inna ta lura da Ladiyo da ke a tsaye gindin rijiya ta d'ora hannun ta a kai. Inna Tace "na ganta sai akai yaya"?.

Cikin 'kosawa da tambayar da Inna take min nace "yo wai ke Inna bakiga goshin ta bane a fashe jini yana zuba?".

Inna tace "na gani mana. tunda ta'ki rabuwa dake ai tana tare da wahala, gashi ta zama lusara bata iya ta'buka komi sai tsokana fal cikin ta tsokana kuma tame 'karfi ce ai".

Nace "yo Inna wanda yafasa mata goshin ne nima" yace "zai fasamin duk sanda muka had'u shine abin yabani dariya da takaici Har kika ji nayi wannan ashar d'in Idan duka 'kauyen nan gatansane wallahi sai naci ubansa duk abinda zai faru ya dad'e bai faru ba. Besan wace ce Siddi'kar Inna ba shiyasa amma ko yaran goye aka amaba ta masa suna na Nan take jikin sa yake fara rawa saboda karo dani babu dad'i".

Banyi aune ba naji anbige min baki Da masifa na d'ago kaina dan naga wani mara kunyan ne ina magana zai bigen baki.

Amma sai mukayi ido hud'u da yaya Sadeeq Turo d'an 'karamin baki na nayi. Yayin da shi kuma yai min dakuwa da hannu.

Yace "saidai ke ki ci uban ki, kamin shi yaci nasa, yau ina gida bazani gurin aiki ba Saboda haka kema babu inda zaki fita sakarya da'ki'kiya kawai ba arabi babu boko, sai yawan gad'a a dan-dali ke a cikin matan 'kauyen kin fita zakka saboda kinfisu wauta da tuma sanci. Inna na daure miki gindi kina yin abinda kika ga dama ko, Kina ganin kamar gata take yi miki To kisani Inna ta riga da ta gama cin kasuwar ta Ke kuma yanzu kika fara taso wa. Dan baki san komi game da rayuwa ba, kwata kwata ma nawa kike? ko 14 years old baki kaiba amma kin addabi mutanan gari kullum ana cikin kawo min 'karar ki ina bada ha'kuri".

Duban Ladiyo yai Yace "ke yakike da suna ma? Ladiyo yake nunawa da d'an yatsan sa manuni ya Ladiyo dake a tsaye hannun ta akan goshinta, tace " "sunana Ladiyo".

Yaya Sadeeq yace "oho koma dai maye sunan naki maza tashi kibi nan" yai mata nuni da hanyar fita gidan.

Yakuma cewa "ko a 'kofar gidan nan idan kika bari na kuma ganin ki to kashin ki ya bushe. Bare kuma in ga wa'innan 'yan 'kafafuwan naki a cikin gidan nan. Allah saina 'ba'b-'ba'bla 'kafa fuwan. Ina fatan kinji abinda nace miki idan kunne yaji gan-gar jiki ta tsira, oya maza zo kibi nan tun muna sheda junan mu"

Ladiyo jiki na 'bari ta bar gidan mu. A d'ari da hamsin.

Kallo na yayi muka had'a ido da shi ya wurgo min harara, Nima na rama cikin 'kun'kuni ciki-ciki nace "nima idan ido ne ba a fini ba bare ayimin barazana dasu kuma mu zuba ni da kai d'in.

Yah Sadeek yace "ke me kike cewa?".

Inna tai saurin cemai ba da kai takeyi ba tafi abinka".

Yah Sadeek yace "Inna kiba ta abinci na takawo min".

Inna taja dogon numfashi tace wai ni Garba me yarinyar nan taimaka ne haka? daka tsaneta. banason haka fa tun ba yau ba nasha fad'a maka Amma dake ka rainani bakajin magana ta. Ko kad'an saboda ni kaka ce To alhaji karami na nan zuwa wata ya kusan 'karewa idan kai ban isa da kai ba shi na isa dashi. Kuma shine mahaifin ka Idan yafad'a maka wata 'kila kaji nasa tunda ka 'ki jin nawa ni".

A sakarce yaya Sadeek ya kalli Inna yace "haba hajjaju makkatun mu karrama ranki shidad'e Ki dad'e kiyi 'kar'ko kiyi shekarun bishiyar dabino Ni na isa in raina ki duk da cewa nike aurenki amma ke ke bada umarnin Kuma yadda Kiki ce haka za ai nadena daga yau babu ruwana da ita."

washe baki inna tai tace " ko kaifa Garba shikenan ya wuce amma da kasa ka 'yar mutane a gaba se ramewa take shiga ciki yanxu zansa ta kawo maka abincin naka

💋💋💋💋💋💋 Hi guys don't forget to

Comment Shear Vote

_I love you all_

💋💋💋💋💋💋

   NI DA YAYA SADEEQ   love story 2021 typing free book_

Story & Writer by Siddiqahtul Khairy Yahya             (S beauty ✍️)

بسم الله الرحمن الرحيم

  Chapter 02           _________Inna tace, "Siddi'ka daure ki tashi ki kaiwa yayan ki abincin sa ya dawo daga aiki ya gaji ga yunwa". 'Daure fuska ta nayi ina turo baki nace, "ni dai Inna bazan kai mishi abinci ba duka na zai yi, baki ga yadda yake kallona ba kamar wani tsohon  maye, kwana biyu  be samu ya dakeni ba, kinsan halin muguntar sa ba sai nayi masa laifi ba, yana iya rufo 'kofa idan na shiga kinsan shi kullum cikin jin haushi na yake".

Inna tace, "Garba ko kunnan 'kashi ne dashi ba zai dake kiba, kina kallo dai nayi masa fad'a kuma a gaban ki akai, idan ko ya ta'ba ki sai na had'ashi da Alhaji 'Karami. Tashi maza kije ki kai mai yar albarka".

Nace, " yo ina  abincin nasa yake Inna?".

Inna tace, "yana kitchen mana inda kika d'auko naki".

koda na 'dauko abincin a saman kaina na d'orashi ina d'igir-gire. Inna tace "A'a fa kada tsautsayi yasa ki zubar mai kinga yana cikin fushi babu abinda ba zai iya miki ba".

Nace "haba Inna bazai zube ba sedai idan kece kike so ki zubar dashi, amma ai ba yau nikeyi ba kuma be ta'ba zubewa ba", Inna tace "Allah ya bada sa'a ta shige d'aki abinta" nace "amin hajiya Inna"

Ina tafe ina 'yan wa'ko'ki na ina tafa hannu, hanyar d'akin yaya Sadeeq na nufa saboda yana daga hanyar waje ne. Koda nazo ba'kin d'akin ban tsaya yin sallama ba  kuma ban buga kofar ba, duk da yasha yimin gargad'i a kan inde nazo d'akin sa kada nashiga sai nayi sallama ya bani izinin shiga, ko kuma na buga masa kofar. Ina tura 'kofar na bankad'a labule  nakutsa kaina ciki. Yanayin da naga yaya Sadee'k yasa nasaki wata uwar 'kara, har saida kular abincin kaina ya fad'i murfin kular ya bud'e dambun ciki ya watse.

A fusace yah Sadee'k ya nufo ni kamin in Ankara ya wanka min kyawawan maruka. Haske nagani wal a idona. Har saida gani na ya d'auke na wasu 'yan da'kiku,  babu riga a jikin sa kirjinsa a kwai yalwa taccen gashi baki sid'ik dashi kwance luf-luf, banta'ba ganin namiji a haka ba tunda nike  a rayuwa ta, shiyasa naji tsoro har kwanan abincin ya zube, ja da baya na fara yi, yah Sadee'k kuma yana nufo ni, na furgita dashi matu'ka. Saboda haka na fara  ihu iya 'karfina yadda Inna zata ji tazo ta cece ni. Takaici na ne yakama  ya kara kamasa, cikin zafin nama ya 'karaso inda nike belt din jikin wandan sa yaciro sai alokacin nai yun'kirin guduwa daga d'akin. Amma caraf yakama hannu na sannan ya maida 'kofa ya rufe harda samata kye da sakata, Duka na ya fara yi kamar Allah ya aiko shi, kota ina zabga min belt d'in yake yi. Ihu nikeyi da duka murya ta, saboda naga so yake ya kashe ni tun kamin lokaci na yayi.

Inna da dake cikin d'aki tajiyo ihuna da gudu ta fito tazo bakin 'kofar d'akin sa buga 'kofar tafara yi tana kiran suna na da'karfin ta. Ganin ba kiran suna nane mafita ba yasa tafara kiran sunan yah Sadee'k, Garba Garba kada ka kashe yarinyar mutane na shiga uku, dan Allah kaya'kuri ka 'kyaleta haka nan kome tai maka ai tadaku bazata 'kara ba daga yau insha Allah".

Tun ina iya jiyo muryar Inna tana magiya har nadena jiyo ta nasan ta ta gajine, saboda bata jure yawan magana yanzu sai hawan jinin ta ya tashi. Sadeeq kuwa kunnen uwar shegu yayi  kamar bashi Inna kema magiya ba, tuni Inna hawaye sun fara zarya a kan kuncin ta saboda tasan yah sadeeq zeyi d'anyen aiki,

Ni kuwa har muryata ta dashe ko  sautin ihun nawa ya daina fita, hawaye ne kawai suke zubar min.  Kuma har yanzu bai dena duka na ba saida yaiwa jikina rud'u rud'u. Sannan yacemin "shiiiiiiii"  yana wani irin huci kamar yayi dambe da 'kartai.

Murmushin mugunta yayi, Nikuwa a cikin raina nace, "mugu burin ka ya cika kaci zalina" wata doguwar ajiyar zuciya naja kamin na fara sauke numfashi da sauri da sauri". Yah Sadee'k yace "idan na'kara jin kinja ajiyar zuciyar nan wallahi saina sako  miki farkon dukan nan. Koma nayi miki mafiyin wanda nai miki yanzu". Ya cigaba da cewa "so nake kiyi shiru kamar bakya gurin nan ko numfashin ki kar inji saukarshi. Hakan ne kawai idan kikayi zaki taimaki kanki, kifita daga d'akin nan lafiya da 'kafa-funki batare da anzo an d'auke kiba".

Nasan halin yah sadeeq sarai ba 'karamin mugu bane, saboda haka nayi Kamar yadda yace "shuru nai kamar wacce ruwa yacita" numfashina na neman d'auke wa ina ta 'ko'karin dawo dashi ba tare da inason yah Sadee'k ya gane ba.  jinike kamar ana so a zare min raina saboda azabar dukan dana sha, gaba d'aya jikina rad'a-d'i yake min, ga kaina da nike jinsa kamar ze bar gangar jikina ya fad'i' kasa.

lura da yanayin yadda nike ciki ne yasa yaya Sadee'k  cewa " kad'an namiki ma wallahi saboda batun yauba nasha fad'a miki kidena shigo min d'aki kamar d'akin arna, bama d'akina kawai ba duk inda zaki shiga kishiga da sallama a matsayin ki na musulma, Amma dayike kunnen ki na 'kashi ne ina gama fad'a miki kike watsar da maganar anan, to wannan shine na 'karshe wallahi idan aka'kara ai koki baki sallama ba kika shigo zakiga abinda zan miki".

Yace, "Tashi kiban guri na gaji da ganin wannan mummunar  fuskar taki gashi kin tsura min ido kamar sa'anki ne yake miki magana".

Tashi tsaye nayi Ina layi ina bin bango har na iso bakin' kofar na bud'e. Ina fitowa naci karo da  inna dake faman sintiri. Kamar wacce tayi 'karya. Cikin sauri Inna takamo ni. zubewa nai a jikin ta babu numfashi ihu inna tafara tana kiran ya sadeeq da karfinta Garba inalillahi wa innah ilaihi rajiun shikenan ka kashe ta. Garba ka kashe 'yar mutane, bazaka fito ba mukaita asibiti ina magana kayi shuru. ya sadeeq yana jin Inna amma yai banza da ita kasan cewar yasan halin inna da zuzuta abu shiyasa ya'ki fitowa. Can dayaji ihun nata ya'ki karewa yasanya rigarsa jallabiya me ruwan madara Yafito. A zaune yaga inna dirshan, ni kuma ina kwance a jikin ta kamar matacciya, yayin da Inna keta faman jij-ji-gani  tana sun batu kamar wacce tafara ta'buwa.

bece wa Inna komi ba yawu cemu cikin gida yashiga ya bud'e fridge yad'ibo ruwa me sanyi acikin kofi, koda Inna tagan shi da kofi batasan meye aciki ba, ta bud'e  baki kenan zatai mai magana ya antaya min ruwan duka ajikina harda mugunta, wata doguwar ajiyar zuciya na sauke ina 'kan-'kame jikina ina 'kara shigewa jikin Inna, ta kaicin yah sadeeq yahana Inna magana. amma ganin ina motsi yasa tadanji sau'ki aranta. Tace "siddi'ka sannu, haka Inna taita kiran suna na tana min sannu, saidai na kalle ta da ido kawai saboda bazan iya magana ba.

da'kyar na iya d'aga han-nuna na mikawa Inna saboda na gaji da kwan-ciyar so nike in tashi, Inna ta fahimci nufi na saboda haka ta kama hannun nawa. Tana fadin "sannu Siddi'ka sannu kinji, Allah zesaka miki" sai a lokacin na iya magana cikin wahalal-liyar murya nace "Inna zan mutu inaji ajiki na karshena yazo" nafad'a ina rushewa da wani irin kuka me ban tausayi, itama Inna kukan tasaka, tana fad'in "bazaki mutu ba 'yar Inna saidai shi yamutu zaki tashi Insha Allah" hannun Inna na kama na d'ora a 'kir-jina nace "Inna nan d'ina  kusa da  zuciya ta zafi yake min".Inna tace "ciwo yake miki?" nace, "eh Inna, Ji nake yi  kamar ba ajiki na yake ba".

yah sadeeq da yake a tsaye tun sanda ya kwara min ruwa na far fad'o yake jin diramar damukeyi. Bakaramar  dariya muka bashi ba amma yasan babu halin yin dariya yanzu sai abin yayiwa Inna yawa. Dabara ce ta fad'o masa. Saboda haka  yaje d'aki ya dauko wayar sa yazo yake mana  video. A cewar "sa idan yashiga d'aki ya kalla abinsa yayi  dariyar sa san rashi".

Cikin muryan kuka Inna tace, "garba ashe rashin imanin ka ya kai haka. Kayi mata dukan mutuwa bai isheka ba kazo kana d'aukar ta hoto. Bakomi kana lokacin ka". Ta kuma fa shewa da kuka tace, "yanxu Garba  bazaka zo kafad'a min yadda zanyi da ita ba ko?. tunda ka illata ta shikenan burin ka ya cika?. to kiramin ubanka awaya nasan duk inda yake yaji ina nemansa zaizo yanzu da gau-gawa. Idan kuma baya garin zai turomin Wanda zai share min hawaye".

'Dan ta'be baki yah sadeeq yayi, Sannan yamatso inda nike, ya tsugun-na  han-nun-sa ya d'ora a kan wuya na, yaji da zafi sosai

Ya cewa Inna "ki d'auko mata hijabi inkaita asibiti naji jikin ta ya d'anyi zafi". Inna tace "au ya d'anyi ne ko Garba Allah zai saka mata mugu, kaje d'akin ta ka d'auko mata kowani irin hajabi ne". Yah sadeeq yace "Inna bafa dake zani asbitin ba a gida zan barki". Inna na salati tana tafa hanna-yenta tace. "Garba me kace? na d'auki yar mutane na baka katafi da ita kai kad'ai kaje kai mata wani abun nasan saboda tsabar ba'kin halinka ko gawarta ma bazamu gani ba. To ban yarda katafi da ga kai sai ita ba. Kafa ta kafar ka maza shiga ciki ka taho min nima da maya fina".

kallon mamaki sadeeq yabi Inna dashi sannan ya ta'be baki yace, " bari na fara fidda  motar waje  sai nazo na d'auko muku". Inna tace "da dai yafi maka saboda bazan bari kaje ka kuma cin zalin ta ba, Nima sai Allah ya tambayeni".

 

Fita daga gidan yaya sadeeq yayi.

Ina kuka nace, "inna wallahi banasan zuwa asbitin nan". Inna tace "ya zakiyi Siddik'a daurewa zakiyi dama ba a zuwa asbiti sai idan ba'ada lafiya. Duk ni naja miki da dakika ce bazaki ba na rabu dake ai da haka bata faru ba".

Yah sadeeq ne ya dawo yatar da Inna tana shere 'kwalla. Be ce mana komi ba ya wuce cikin gida, sai gashi ya dawo da hajabi na da maya fin Inna. Yana zuwa ya mi'kowa Inna yace "dan Allah ni kuna 'bata min lokaci ina da abin yi ungo saka mata"

Amsa Inna tai bata kula shiba saboda ya gama kaita bango. Saida tayafa maya finta sannan tafara 'ko'karin d'agani amma ta kasa, saboda shekaru sunja kuma tun ina jari-riya a cikin tsumma na take d'awainiya dani, saboda haka tace ma yaya sadeeq ". Temaka ka d'aga min ita nasaka mata hijabin. Yi yai kamar beji abinda Inna ta fad'a ba. Kome ya tuna oho. Se gashi yazo ya  dagani sama ta yadda fiskata  zata  kalli  Inna. Saka min hajabin tayi, yasan Inna  baza ta  iya d'auka taba saboda haka ya ajiye ni a 'kasa amma be sakeni duka ba. Yace "Inna muje ko,'ko'karin fara jana yakeyi, Inna tai saurin daka mai tsawa tace" wai Garba lafiyan 'kalau kuwa?"

Be ce mata komi ba yasa'ba ni a kan kafad'ar sa, Saboda yayi min mugun ta  yazuro kaina 'kasa sosai. jini na se dawo min kai yakeyi, a haka muka isa bakin motar, a gidan baya ya ajeni sannan yashiga gurin zaman direba. Inna  ma  baya tashigo tana mita. domin Allah ya mata mita koda yiki yawanci tsofaffi sunada wannan mitar, kaina nadora kan cinyarta ina matso kwalla bawani bab-ban asbiti ya kaini ba illah asbitin dake cikin 'kauyen mu asbitin shi kadai ne asbiti. kuma babu wasu kwararrun ma aikata acikin sa.

   

idan kunji dad'in labarin ku aikomin da

Comment        Shear            Vote

NI DA YAYA SADEEQ                   

Story & Writer by Siddiqahtul Khairy Yahya             (S beauty ✍️)                                03

_________Asbitin gaba d'ayan sa a lalace yake saboda ginin jar 'kasa ne wani 'bangaren ma duk ya rushe, d'a kunan  da ake kwantar da marasa lafiya guda 4 ne kawai, Sai office 1 da ma aikatan asbitin suke zama a cikin sa, gabaki d'aya asbitin gado biyu ne kawai a cikin sa,

a bakin asbitin yah sadeeq yayi faking, Asbitin bashida kofar shiga ko ta ina shiga a ke saboda ba a ke waye yake ba, ya d'auki kusan 10 seconds a cikin motar, kafin ya kashe ya fito, Saida yafara bud'ewa Inna  murfin 'motar ta fito, san-nan yazo ya bud'e bangaren da nike yad'an zuro jikinsa ciki ya mi'ko hannu ya janyo ni, Inna na fad'in "kabita a hankali ba tada cikak-kiyar lafiya". 'Dauka ta yayi irin d'aukar da a kewa jari-rai cikin Asbitin ya nufa dani,

Inna na biye  dashi a baya,

Da yike yah sadeeq sanan-ne-ne a gari bama iyaka kauyen mu kad'ai ba harda burni. Saboda babban d'an sanda ne, kuma jajurtwcce akan aikin sa.

wata nurse ce ta  hangomu da sauri ta 'karaso inda muke, cikin rawar jiki tace "yallabai cikin wancen d'akin zaka kaita zatafi hutawa babu mutane da yawa a cikin sa". Tafad'a haka tana nuna mai d'akin da yatsan ta manu-niya, "alright" shine abinda yah sadeeq kawai ya fad'a.

'Dakin da a kace yah sadeeq ya kaini shine d'akin da ake ji dashi a cikin asbitin saboda a kwai siminti da gado guda d'aya tak a cikin sa, mun tarar da mara lafiya a kan gadon  kwance, saboda yah sadeeq ya d'ora ni aka sauke mara lafiyar gunin ban tausayi gashi masu jinyar ta basa kusa,

"yalla'bai d'ora ta a kan gadon". A cewar nurse d'in data sa aka sauke mara lafiyar

Yah sadeeq beyi ma-maki ba saboda ya saba kawo ni asbitin kuma irin haka ne take  faruwa.

'Dora ni yayi akan godon, yana d'orani ya fice daga d'akin,

Nurse d'in ma tabi bayan shi tare da wa'inda suka cic-ci-'bi marar lafiyar da aka sauke a kan gado,

bai jima ba saiga shi ya shigo tare da  wata nurse, hannun  ta rike da wani d'an karamin faran tin silba, kan wani teburi na katako ta ijiye tiran silban, sannan ta matso kusa dani, ta d'ora hannun ta a kan wuya na, "a kwai zafi a jikin ta yallabai, zazza'bi ne ya kamata?". Nurse d'in tafad'a tana duban shi, amma ko tanka mata beyi ba sai yayi kamar ba dashi take magana ba,

"meke damun ki?". Nurse ta tambaye ni,

nace "duka jikina ciwo yake min, amma kirji na yafimin ciwo".

Fuska ta ta kalla da kyau sai taga shatun hannu tace "kamar dukan ki akayi ko, domin shaidar hannu ya bay-yana a kan kuncin ki rad'a rad'a".

Na bud'e baki zanyi  magana kenan yah sadeeq ya wurga min hara ra,

Ya kalli nurse d'in yace "ke maye aikin ki?".

"Duba mara lafiya". Ta fad'a bakin ta na rawa,

saida ya d'aure fuskar sa babu alamun wasa a tat-tare dashi yace "to kiyi aikin ki wannan be shafeki ba kiyi abinda yadace".

Cikin in-ina tace "to ranka  shidad'e na tambaya ne saboda nasan irin maganin daya dace na bata, amma kaya 'kuri naga kamar ranka ya 'baci".

Bai kuma bi ta kanta ba yafi ce  daka cikin d'akin, tasha fama dani sosai kamin na bari tasoka min allurar da zata samin abin 'karin ruwa, shima saboda naga yah sadeeq ya dawo d'akin ne.

Banfi minti 25 da samin karin ruwan ba, baccin wahala ya d'auke ni,koda na farka bayan wasu awanni da bazu wuce 2 ba

Naga momy zaune a kan wata farar kujera, da alama daka gida aka zo da kujerar mamakin ganin ta ne ya kamani, na mi'ke zaune na jingi na da filo a baya na, kallon ta nikeyi ina muts-tsuka idanu na, ban gama mama ki ba saida naga  Khadija, tashigo d'akin hannun ta d'auke da kular abinci, da kwano, Umar, na biye da ita a baya,

tashi Momi tayi tamatso da kujerar ta kusa da gado na ta zauna  tana kama hannu-na "sannu kinji Allah ze saka miki ya jikin naki". Momy ta tambayeni muryan ta d'auke da damuwa

madadin na bata amsa sai nace "wai Momy yaushe kuka zo kuma waya fad'a muku banida lafiya?, Inna dai bata da waya yah sadeeq kuwa nasan ko mutuwa nayi bazai kiraku ya fad'a muku  ba".

Momy tace "Babu wanda ya fad'a mana, daka kaduna muke hutun makarantar su Khadija ya 'Kare zamu koma Abuja, shine muka biyo tanan, can gida muka fara zuwa bamu sami kowa  a ciki ba,kun bar ko ina abud'e, hakan ne yasa naji a jiki na ba lafiya ba,  shine nakira yayanku sadeeq awaya.

shine ya shaidamin "bakida lafiya ne ya kawo ki asibiti".

Nace "mai wani asbiti?".

"Asbitin Dande". yabani amsa  daga haka muka yi sallama na kashe wayar.

Sanda mukazo  hajiya Inna ke bani labarin abinda yafaru tana kuka, gaskiya sadeeq bai kyauta ba,

Momy tace "Na kira sa a waya nayi  masa kaca-kaca, kuma nakira Daddyn ku a waya, na fad'a masa, ya ce "muzauna anan Danden  nanda kwana 2 zaizo".

Ina 'Ka'kalo hawaye  nacire hajabin jikina, nace "Momy kalla kigani fa wallahi babu abinda nayi  masa yayi min wannan dukan kuma". Yace "kad'an yayi min".

Salati Momy keyi tana tafa han-naye "yanzu sadeeq ne yayi miki haka?". Momy ta fad'a tana ri'ke ha'bar ta,

  gyad'a kaina nayi alamar eh,

tace "kiyi ha'kuri Daddyn ku ze zo nan da kwana biyu insha Allah,zai d'auki mummunan mataki yanda koda kud'i a kace Sadeeq ya dake ki baze dake kiba".

Khadija da tunda ta shigo ta aje kular hannun ta, ta sami gefan gado na ta zauna, sai alokacin tace min " sannu Siddi'ka yajikin naki  da sauki dai ko?".

"Babu laifi dai zance amma wallahi na daku gurin wancen ba'kin mugun". nace mata,

"ina ke miki ciwo yanxu to?". Khadija ta kuma tambaya na,

Nace "Babu sai d'an abinda baza'a rasa ba".

"Alhamdu lillah" Momy tace

yayin da  Umar yace "aunty Siddi'ka yajikin naki?".

"Dasuki" itace amsar dana basa,

ina mi'ka mai hannu alamar yazo kusa dani, ai kuwa ba musu yakama han-nun nawa, zaunar dashi a d'ayan gefen gadon nayi  suka sani a tsakiya,

dayi ke lokacin da nike bacci ruwan da ake 'kara min ya 'kare nurse d'in tazo ta cire min.

zubamin abincin Khadija tayi, tana fad'in "sister Siddi'ka daure dan Allah kici wannan babu yawa". Taliya ce fara da mai da yaji

nace "na'koshi"

da 'kyar Momy ta lal-la-'bani naci abin cin d'an kad'an, na ture kwanan

nace "nifa na  'koshi Umar zo kacinye sauran".

Sai alokacin na lura babu Inna, "ina Inna wai?". na tambaya ina kallon Khadija,

takoma gida nasaka driver ya kaita nace "zan zauna dake har sanda zasu sallame mu". A cewar Momy

"to Momy mukoma gida mana na warke". Nafada ina sauka daka kan gadon kamani khadija tai tana fad'in "wannan wani irin ciwo ne Siddi'ka?,🤔 Koda yike kedaman haka kike bakyason asbiti".

"haba Khadija ai kwata-kwata natsani asbiti wallahi inba dole ba me mutum zaiyi" nabata amsa da haka

Nace "Momy kira driver d'in Allah da gaske nike na warke".

Momy tace "bari a fara kiran likita idan tace zamu iya tafiya gida sai subaki  sallama".

dariya ce takamani sosai nike 'kyal'kyatawa,

"Lafiyan ki kuwa Siddi'ka".Momy ta tamba yeni,

nace "wallahi Momy kece ki ka bani dariya, baki karewa asibitin kallo bane halan to wannan asbitin da ki ke gani ba a sallamar mutum, idan aka kawo mutum yaji  sau'ki ka wai tafiya zeyi. Idan kaga dama ne ma sai kace musu zaka tafi, basa saida wasu magun gunan kirki, kuma basa   wani rubuta maka koda zaka siya wani gurin idan su basu da shi, idan ma sun rubata to abu 2 ne kawai fanadol sai farasitamol".🤣na'kara sa fad'a  ina 'kara 'kyal-'kyala dariya

Na cigaba da cewa "nifa Momy wallahi a gani na duk basu san aikin su ba, gwara gwara ma Aliya wannan tad'an Iya aikin, itace ma tasamin ruwa, idan fa aka kawo mutum bata nan sunan shi sorry ba'kara min ja-gwal-gwalo mutum ze sha ba".

sosai khadija ke dariya tace "ai ni ban zata ma asbiti bane domin sam baya kama da asbiti".

"'kwarai ma kuwa". Nabata amsa

Nace "kefa da a ka kawo ni wata a ka sauke a kan gadon a ka d'ora ni, nason don sunga yah sadeeq ne duk sanda ya kawo ni gado suke bani".

cikin mamaki Momy tace "wata fa ki ka ce aka sauke".

"eh mana Momy" nabata amsa

"to ina suka kaita?". Momy tayi tambayar,

Nace "wallahi Momy ban sani ba lokacin ina fama da kaina".

cikin hanzari Momy ta fara lalubar jakarta tana fad'in "da gaskiyar ki Siddi'ka bari na kira driver yazo ya kaimu gida kamin kema a sauke mana ke, tunda Sadeeq d'in ya tafi".

Ina dariya nace "hhhhmmmmmmm Momy da zamu shekara anan babu wanda ze sauke ni".

"saboda me? Yaya ko?". Khadija ta tambayeni tana kallon idona

  Nace " eh, nifa mutane har mamaki suke bani yadda naga suna tsoran yah sadeeq kamar wani mala'ika".

Momy tace "nidai duk da haka gwara mu koma gida, ko wani asbitin na kudi a canza miki ban yarda da wannan ba za a iya bawa mutum maganin da bashi yadace ba".

Nace "momy nifa na  warke babu wani asbitin da zan sake koma wa".

'Dau kar wayar ta tayi ta latsa nombar  Idi driver, bugu d'aya ya d'auki kiran kamar tana gabansa cikin ladabi yace "Hajiya na kawo Inna tun d'azun".

Tace "yayi kyau muma kazo ka d'auke mu ta sami sau'ki mara lafiyar".

Yace "to Hajiya". sannan takatse kiran

Ba a fi 15 minutes ba saiga Idi driver yazo

dayake d'azun har dashi aka zo yasan asbitin har d'akin da aka kwantar dani ya shigo,

ya kwashi  tarka cen da khadija tazo dasu yayi gaba,

Sannan mumu muka fito, da Aliya muka ci karo A bakin fita asbitin tana Murmushi tace "mara lafi sauki yasamu kenan".

Nace "eh". Tace "to bazaku sai magani bane?".

"muna da irinsu dayawa agida" nace mata

"to shikenan Allah ya'kara sau'ki" ta fad'a yayin da takai duban ta ga Momy tace "Hajiya ya me jiki?".

Momy tace "da sau'ki". Daga haka muka mata sallama muka futo cikin asbitin, muka shiga cikin mota Idi driver ya hau titi

Umar ne ke bamu labarin ban dariya a mota sai 'kyal-'kyala dariya mukeyi kamar wasu za-rarru Momy dai saidai tayi  Murmushi idan taji ya fad'i abin dariya,

yanxu ma wani labarin bafullatani yake bamu

  Yace " wai wani ba fullata ni ne, ya siyo lemu, shine aka samai lemun aleda, sai yasaka lemun a bayan keken shi koda ya fara tafiya a kan  kwalta, sai ledar lemun ta 'bule,  lemu d'aya yafad'i a kan kwalta, koda ba fullata ni yaga abinda ke faruwa lemun sa ya fad'i kan kwalta, amma se gudu yake yi, sai ya sauka a kan keken ya d'auko sauran lemun da suka rage a cikin ledar, ya watsar kan titi", yace "a kin banza a she ku kuna ma tafiya kuka bani wahala,  to muhad'u a gida". 🤣

Comment       Shear            Vote

    NI DA YAYA SADEEQ                       Story & Writer by Siddiqahtul Khairy Yahya             (S beauty ✍️)                           Page 04

بسم الله الرحمن الرحيم          ________Sosai muke dariya Khadija harda rike ciki, ni kuwa ba a magana don har tsalle nikeyi, a haka muka iso gida cikin farin ciki da nishad'i na manta da wani yah sadeeq saboda ganin su khadija

"Inna Inna". Na shiga ina 'kwala mata kira buta ce a han-nun ta da alamar ban d'aki zata, mama ki ne ya bay-yana 'kara ra a kan fiskar Inna,

rungume ta nai ina fad'in ya "dai tsohuwa ko baki murna da gani na bane" "ja ira". Inna tace tana jan dogon hanci na "banyi murna daganin kiba zaki ce nida nafi kowa san kisa mu lafiya, mamaki ni keyi saboda sanda naba roki baki san wake a kanki ba".

dariya nayi nace  "yo Inna ikon Allah ai ya wuce gaban komi".

"haka ne Siddi'ka ya jikin" Inna tace min Nace "jiki yayi sauki wallahi".

Inna tace "haka akeso wancen mugun kuma Allah zai saka miki kinji".

"To". Nace yayin da nike nufar cikin falo, ina shiga na zauna a kan kujera ina maida numfashi, kamar wacce tayi gudu saboda al'ada tace,

can sai ga Khadija tashi go

"ke haka ake tarban baki?". tace min

"ina ba'kin suke?". na tambaye ta

"gamu" tanuna kanta, duka nakai mata sannan nace "to ki godewa Allah domin na karrama ku".

"A hakan?". Khadija tace min Na bata amsa da "eh".

"bakida kirki Siddi'ka". khadija tafad'a tana zama kan kuje rar danike kai, nace "danayi me?".

Tace "bakisan me kikai ba ko"

nace "eh man".

"shike nan ya wuce tunda kin manta".Ta fad'a tana share zancen,

ta'be baki nai nace "kinsan wani abu khadija?".

"A a". tace min na d'ora da cewa "wallahi yaya Sadeeq bai daki banza ba zan rama bashi yaci, domin ni ba kanwar lasa bace".

Mi'kewa Khadija tayi alamar razana tana dafa kirjin ta, "zakiye me". Ta kuma tambaya ta. "ramawa". Nace mata

Tace "ke kuwa ta  yaya". Nace "kedai kitsa ya kiyi kallon ikon Allah".

da ido ta bini da kollo irin bakida hankali yarinya

Nace "kinamin kallon banida han kali ko to zan tab-batar miki da a cikin hay-yaci na nike amma tabbas yaya be daki bulus ba".

"hhhhm". tace tana cire gyalen ta, ta ajiye a han-nun kujera

Umar ne yashigo bakin sa da sweet yana tsotsa, la Umar zo kasam min". Na fad'a ina mi'ka mai hannu na, yace "za kisha ne?".

Nace masa "eh". Yace "nakawo miki naki, bari naje na  d'auko miki yana d'akin Inna".

Nace "to"

"nima katawo min dashi". Kadija tafad'a

bedad'e ba saiga shi yakawo mana, nan ya zauna mukai ta shirme daman idan muka had'u a guri babu dama

Ana idar da sallar magriba ina sulalewa nabar gidan 'yar kasuwa nanufa ina tafe ina gad'a ni kad'ai, a can na iske kawata Ladiyo, kaf kauyen Dande banida kawa sai Ladiyo saboda nafi san a kullum nice shugaba, bana son raini ko kad'an sauran duk nayi fad'a dasu saboda halin mu be zo d'aya ba, itama Ladiyo tana da hakuri ne kuma kome zan mata batayin fushi

Ladiyo nakwala mata kira daka nesa saida nasake kwala mata kiran akaro na biyu, tana waige-waige tajuyo inda nike baki washe ta nufo ni, tafawa mukai alamun munji dad'in ganin juna

"Ai nazaci bazaki futo ba". Ladiyo tace min".

"Saboda me". Nace mata

Tace "saboda abinda yayan ki yace d'azun wallahi na tsorata bazan 'kara zuwa gidan kuba". Wani dogon tsaki naja mastssttt

Nace  "kefa sakarya ce bakida wayau, yo  saiki yarda da maganar sa, shi ba mala'ika ba ba kowa ba, abinda ma yasa baki ganni da wuri ba banida lafiya ne saida aka kaini asbitin bakin gari".

Ladiyo tace "Siddi'ka baki da lafiya fa kika ce" d'aga mata kai nayi alamar eh

"meke damunki nidai banga alamar rashin lafiya atare dake ba". Tace min

"Ke wallahi kuwa". Nace mata "yah sadeeq ne yaimin dukan mutuwa saida akai min 'karin ruwa". Ido tazoro waje tana dafe kirjin ta tace  "dukan mutuwa fa kika ce".

Tsaki nayi nace "dube ta kamar ita a kaima dukan duk ta firgice". Tace "yo  dole na firgi ce, d'azu fa da yana min magana wallahi ba'kara min tsoro naji ba, saboda dana bar gidan ku kafin inkai gidan mu nayi fitsari gurin sau uku, kuma kinsan d'an Sanda ne, mugunta babu wacce be iya ba domin rannan tsallan kwad'o naga yasa wasu yara a layin ku zanzo gurin ki, zuwan da banyi ba kenan".  duk Ladiyo ce tayi wannan bayanin

ta'be baki nayi sannan nace "hhhhmm kinsan be daki banza ba ko domin wallahi bashi yaci abinda ma yasa nafito kenan neman mafita domin yau ba tsoka na zanyi ba".

Tace "ai kuwa naji dad'in ganin ki domin bakiga yadda su Mariya da Harira suke tsokanata ba wai inyi magana suyi min dukan tsiya tunda bakyanan".

"Me kika cemusu". na tambayeta

"babu komi". Tace min

kwafa nayi sannan nace "bari na gama da yah sadeeq sai na juyo kansu".

"Yanzu nidai fad'a min me zanmai na huce". Na kuma tambayar ta

Shiru Ladiyo tayi  a lamun tana nazari can tacemin "a dake dai baze dakun miki ba saidai muyi masa mugun ta dai-dai da dukan daya miki".

"mugun ta kuma?" nace mata

"eh". tacemin "kawo kunnenki kiji yadda zamuyi".

A kunne tarad'a mun aikuwa naji dad'in shawar ta domin nasaki raina tunda nasamu mafita, nayi tsokana iya tsokana se gurin tara na koma gida, a d'akin Inna nasamesu a nata fira da sallama na shiga,

Da ido kowa ke bina, "wai Siddi'ka ina kika je ne haka?, gurun mutane biyar suka kawo 'karanki,  Aisha ke basu hakuri da d'an kud'i". Inna ce ke wannan maganar

cikin in-ina nace "Inna daman naje....".

"Daman me" tace min

Nace "waye yakawo 'karata ban sani ba?". Ko kallo na Inna batai ba

ta'be baki nai na juyo na kalli Momy nace "wai haka momy ankawo Kara ta".

Momy tace "Hajiyan 'karya zata yi miki, wai Siddi'ka yaushe zaki girma ne kiyi hankali, kina girma kina 'Kara rashin wayau,  Allah ya shir yaki".

"Ameen" nace "ina abinci na?". Na tambayi Inna

"yana kitchen" tace min

Umar yace "nima banci abincin ba nace sai kin zo" "to yayi d'auko mana muci me aka girka?" na bukata,

Yace "fatan doya ne Momy ta girka".

Nace "maza d'auko mana". munaci ina bashi labarin inda naje da kalar tsokanar da nayi, sai cizon yatsa yake yi  yana fad'in "wai meyi sa baki min magana ba sanda zaki tafi? wallahi da dani za'ayi, da yanzu ba labari kike bani ba saidai ni na bada"

Nace "yo kaya'kuri bansan ai zaka ba na d'auka kai ma irin Khadija ne me tsoran tsiya". "wa ni?" Umar yafad'a yana nuna kansa "Allah ya kyauta ina namiji intsaya tsoro sai kace mace".

Comment          Shear              Vote                     NI DA YAYA SADEEQ

Story & Writer by Siddiqahtul Khairy Yahya             (S beauty ✍️)                

Page 05

_________Bayan gama cin a bincin mu da Umar na mi'ke ina hamma alamar bacci nike ji,

Khadija ce ta kalle ni tace "ba dai bacci za kiyi ba". Nabata amasa da "eh kwanciya zanyi".

"Dawuri haka" ta tambaye ni

Da "eh". Na bata amsa

"yo in banda abinki khadija ai Allah kad'ai yasan inda Siddi'ka taje bayan fitar ta gida kinga ko dole ta kwanta da wuri". duk Inna ce ke wannan maganar, ta'be baki na nayi nace "Momy zan kwanta saida safe". Wayarta ta kunna ta kalli a gogo 'karfe goma saura na dare, kallon Khadija Momy tayi tace "kitashi kibita dare yayi goma saura". Umar ma tashi yayi zai bimu amma Momy tace "bata yarda ba tare da ita zai kwana saboda ita batasan kwana ita kad'ai".

A kwai d'akin da idan sunzo suke sauka acikin sa, duk wani abun bu'kata Daddy ya zuba a ciki

saida safe muka 'kara yimusu Khadija ta rigani yin gaba, daka baya na bi bayan ta,

Jinayi kamar na taka 'kafar mutum dayike lungun d'akin a kwai duhu 'kauyen dande babu wuta, janna-reto muke kunnawa zuwa 'karfe goman dare a kashe, to yau yaya sadeeq be kunna ba, ban tabbatar da 'kafar mutum bace a gurin nataka hakan yasa na 'kara d'ora kafata a kai na murza, 'yar 'kara naji anyi alamun mutum ne, koda na waiga inda nike tsammanin zan sami Khadija wayam babu ita ba alamar ta, zaro ido na nayi da kyau gabana ne yafad'i saka makon ba'kin mugun da nagani, yana wannan Murmushin nashi na mugunta,

A d'an tsorace nace "la yaya". Ban 'karasa maganar ba ta ma'kale,

Saka makon bige min baki da yayi, ya sha'ke min wuya, ya had'ani da jikin bango

Yana fad'in me hali be fasa halin sa gwara na kasheki kowa ya huta,

Da iya 'karfin sa yasha'kemin wuyan ina son inyi ihun neman d'auki amma na kasa, cikin ikon Allah saiga Momy da Umar, sunzo wucewa hannun ta d'auke da hasken fitilar wayar ta, tana haskawa, mai zata gani wani 'kara ta saki saida wayar ta yafad'i a 'kasa

Inna da khadija rige-rigen fitowa suka yi saboda ihun Momy da suka ji,

Umar tuni ya das-kare a gurin, jikake tas tas 'karan marin da Momy ta wanke yaya sadeeq

Amma duk da haka ya'ki sakina don haka ta 'kara mai wani saida tayi mai mari biyar amma ko gezau, beyi ba dayike yah sadeeq namijin duniya ne, "to idan baza saketa ba sadeeq zan cireka cikin 'ya'ya na". Momy ta fad'i haka fiskar ta babu alamun wasa

jin wannan lafazin na Momy yasa Sadeeq yayi jifa dani ida nuwan sa jajur kamar Wanda yasha wani abun, yana huci

Kasa nafadi shirim jikina babu 'kwari ina fitar da numfashin wahala Inna da Khadija takaici ya hanasu magana, hawaye ne ke gan-gan garowa a cikin Idanuwan Momy, ta kasa magana hannuna ta kama muka wuce d'aki na, su Inna na biye da mu abaya

Kan gado ta d'orani, na kwanta yaraf kamar gawa, ruwan fridge me sanyi khadija ta d'ibo min ta d'aga kaina ta bani nasha ina maida numfashi,

Babu Wanda yatam bayi me ya had'amu, duk kuwa da cewa zuciyoyin su cike suke da son jin abinda ya hada mu, daga haka kowa ya tafi ma kwancin sa,

a raina sa'ka yadda zan wula'kan ta yaya sadeeq nikeyi, domin wallahi bashi yake ci wani mugun tsanar sa naji ya 'kara da d'uwa a zuciya ta,

da wannan tunanin bacci 'barawo ya sace ni

Kiran sallar asuban fari a kunne na akayi, banida nauyin bacci, tashi nayi na zauna gaba d'aya jikina ciwo yake min amma wuya na yafi min ciwo,

Tashi nayi tsaye ina mi'ka ko salati banyi ba, ba kuma dan ban iyaba saidan tsabar shagala, da wasa da yayi min yawa,

tsakar gida nafito babu kowa d'an Murmushi nayi saboda zanyi abinda zanyi babu wanda zai ganni a irin wannan lokacin ya Sadeeq ke fitowa yayi alwala, kamar yadda Ladiyo ta tsara min haka nayi, a binda kuwa Ladiyo tace min a kunne shine "na zuba masa garin karara da dakakken tarugu aruwan alwalar sa, da na wanka, nayi na'am da wannan shawarar da tabani, saboda nasan tanan ne kawai zan iya ramawa,

sad'a-d'awa nayi 'bangaren sa inda yake ajiye butar sa na nufa, "Alhamdu lillah". na fad'a yayin da na hangi butar sa, a jiye a gurin, da hanzari na 'karasa gurin

d'aga rigata nayi na war-ware siketin jikina, na ciro 'kullun ledar karara da nasaka Ladiyo ta sato min na Umman ta da take saidawa

Murmushin mugunta nayi, yayin da na d'aga butar naji ta cike da ruwa, bud'e murfin butar nayi, na zuba sannan nasaka hannu na na kar kad'a ruwan

Yaya Sadeeq baya barin sai zaiyi anfani da abu yanema yana tanadar sa ne tun kamin lokacin amfanin sa yazo saboda bayason bata lokaci

A jiyar zuciya nayi nabaro lungun, a hankali nike tafiya kamar mara gaskiya, Inna na hango idon ta akaina 'kyar da buta a gaban ta, da alamar alwala ta gama, Murmushi nayi na'kara sa gaban ta nace "Inna kin fito kenan?".

"eh na fito, daga ina ki ke?".ta tambayeni

"daka waje le'kawa nayi, alwala na fito sai yanayin garin ya bani sha'awa shine na le'ka waje" na fad'a mata haka kamar da gaske

"Amma mai yatada ki daga barci" Inna ta tamba yeni a karo na biyu,

wallahi Inna baccin ne ya'ki zuwa min sai naji an kira sallah shine nace "bari nayi sallar sai na kwanta".

Tace "to ya jikin naki?" nace Inna da d'an sau'ki amma na kasa bacci, dana rufe ido sai na dunga ganin kamar zai zo ya sha'keni". Saboda yace "saiya kasheni".

Inna na salati tace "yanzu Garban ne yace saiya kashe ki!?". "Eh Inna shi fa ai ba 'karamin mugu bane". Na 'kare maganar ina yin hanyar ban d'aki,

Na bar Inna da mamaki

Bandaki nashiga nayo fitsari, na fito nazauna a kan kujerar tsakar gida, nafara alwala kenan saiga Yaya Sadeeq nan, nayi kamar ban ganshi ba, na cigaba da yin Alwala ta, ta gabana yazo ya wuce, bayan shi nabi da kallo ina Murmushi, a cikin zuciya ta nace "zaka bawa yan garin ku labari, zaka san kayi da 'yar halak".

bandaki yashiga yajima aciki, can saiga sa ya fito, a lokacin nagama Alwala ta amma ban tashi a gurin ba,

Tashi nayi na koma d'an nesa da inda ya tsugunna

Alwala yafara yi ganin ya manta beyi kus kuran baki ba naji sanyi a raina, d'aki na koma na tsaya a bakin hundo, ina kallon sa,

yana wanke fuska ne naga ya mike kamar wanda aka tsungula gabansa yakama yana murzawa😂 bansan sanda daria ya kwace minba can kuma yafara kifta ido se yanzu yake tunani tabbas yaji ruwan wani iri lokacin dayeke shakar hanci, abinda yasa baiyi wani tunani ba yaga butar sa ce shi kad'ai babu wanda yake amfani da ita, sosai yake murza idonsa ati shawa na biyo baya haka yaita fama 💃 d'aya hannun rike da gaban sa yana murzawa 🤣

Dariya nike ina tsalle abin nema yasamu sosai Yah Sadeeq yazama karamin mahaukaci gashi har an shiga masallaci amma shi ko alwalar be samu ya gama ba

Sosai abin ke damun sa musamman gabansa yafi sosa gurin, a haka Momy tafito ta same sa, watsi tayi dashi kamar bata ganshi ba, jin motsin da yayi ne yasa ya d'an bude idon sa, saboda yaga waye, wata a zaba ce ta 'kara shigar masa ido har saida ya saki 'yar 'kara, tsaki Momy taja tagama abinda za tayi nan tabar sa tanai masa kallon mahaukaci, 🤣

Khadija Khadija yah Sadeeq ne ke 'kwala mata kira, barci take yi, ganin yana kiran ta nayi saurin zuwa bakin gadon ina dukan ta,da magagin bacci a idon ta "lafiya?". Tace min 'yar dariya nayi nace "yah Sadeeq ke kiran ki". tashi tayi zaune tana zaro ido kamar ba me magagin bacci ba "yana ina?". tace "tsakar gida". na bata amsa

Nace "amma fa kiyi a hankali don naga kamar yasamu ta'bin hankali"

jin yana 'kwala mata kira dakarfi yasa ta fad'uwar gaba babu shiri ta sakko daga kan godon, tayo waje, yadda taga yaya sadeeq d'in a tsakar gida ba 'karamar kunya yabata ba, gani Yaya tafad'a sanda ta 'karasa gunsa,

"d'auko bokiti a d'aki na ki zuba min ruwan wanka, ki kai min ban d'aki". Sadeeq ya fad'i haka.

Da "to" tabi shi kamar yadda ya umarceta haka tayi, a binda khadija bata sani ba ina la'be lungun bayi tana aje ruwan nazuba mai karara da dakakken tarugun nan, nai fitowa ta, tsaye na ganta gurin sa tana cemai "yaya na kai maka ruwan".

"Kama hannu na to" yace mata, hannun na sa takama har bayi ta kaisa, sannan tafito

Idanun sa a rufe suke har yanzu cire jalla biyar jikin sa yayi, ya bar karamin wando jikin sa, tunawa yai da babu sosan wanka da sabulu, kiran sunan Khadija yafarayi nikuwa daman ina kusa da bayin, khadija kuwa tayi alwala ta tafi d'aki sallah, "kawo min sabulu". Yace

daman Yah sadeeq bai wanka da so so ko kadan sai sabulu kawai, Murmushi nayi naje na dauko mai sabulu wanda na badeshi da zallan tarugun dana ga Inna ta daka sa ta shanya asama jiya,

hhhmmmm nace "ai wallahi tunda ka ta'bani sai kayi daka sani, bayan na dauko sabulun taka kujera nayi naje fa mai sabuln cikin bayi

Komawa gefe nayi na zauna inajin raina fes banida wata damuwa,

har gari yafara wayewa babu sadeeq babu labarin shi nikuma na'ki tashi domin ko sallah ma banyi ba

Ya sadeeq kuwa yazama abin tausayi cikin bayi yarasa wannan wani irin bala'i ne, shida yayi wanka domin yasamu sau'ki amma sai a kasin haka, susar jikinsa yake iya 'karfin sa duk da idan yasosa yanajin wani mugun rad'ad'i a jinkin sa, amma bashi da wani zabin da yawuce susar,

har 7 am be fito ba Inna ce zata shiga bayin na kalle ta nace "Inna fa da mutum".

"Waye?" tace min "yah Sadiq ne" na bata amsa,

Inna tace "me yake yi agidan har yanzu da bai fita gurin aiki ba, naga da an idar da sallar asuba yake tafiya".

Nace "to Inna kika sani ko anyi musu canji ne kinsan ana canza su ai".

"haka ne" Inna tace min, d'an matsa wa nayi kusa da ita, sannan nace "Inna amma fa yau yah Sadeeq wallahi kamar mahaukaci, domin tun asuba yake abayin nan, kafin yashiga ya dad'e anan tsakar gida yanayin wasu a bubuwa masu kama da na mahaukata". Zaro ido inna tayi na d'aga mata gira, nace idan baki yarda ba, Ki je ki tambayi Khadija ko Momy saboda dukan su sun ganshi a cikin yanayin,

♾️♾️♾️♾️♾️ Nagaji da typing atara gobe in Allah ya kaimu domin jin yadda za a kwashe tsakanin Sidda'ka da sadeeq kucigaba da bibiyata nikuma zancigaba da nishadantar daku

NI DA YAYA SADEEQ                      

Chapter 06

بسم الله الرحمن الرحيم

_____Jin jina kai Inna tayi, sannan ta nufi hanyar d'akin da Momy take, ta 'kwan-'kwasa musu kofa, ta d'an jima a bakin 'kofar, kafin Momy ta bud'e ta fito, "ina kwana hajiya". Momy ta gaisar da hajiya

cikin sakin fuska Inna ta amsawa surukar ta "ya ba'kun ta?".

"Lafiya lau". Momy ta bata amsa,

"to alhamdu lillah". A cewar Inna

ta dora da cewa "kiya 'kuri na tashe ki kina tsaka da bacci".

"babu komai Inna" cewar Momy,

Inna ta cigaba da cewa "daman Garba ne wai tun asuba yake ban d'aki". Har yanzu bai fito ba, Siddi'ka tace "yau kamar bashi ba yana tayin wasu abu irin na taba'b-'bu" shine nace "bari na tada ki muje bayin mugani ko lafiya".

Momy tace "Hajiya Inna badon karkice na raina ki ba da bazani ba tunda shi bayajin magana".

Inna tace "Ha'kuri zaki Aisha muje mugani ko lafiya kinga da ya idar da  sallar asuba yake tafiya gurin aiki, amma yau shuru".

"To". Momy tace badon ranta yaso ba, tabi inna ban 'dakin

Koda su Momy suka 'kara sa bakin bayin sunan shi Inna takira "Garba Garba". kamar babu kowa a ciki, saboda bai amsa ba, saida Momy tace "sadeeq wai lafiyar ka?".

Da wata iriyar  murya yace "wallahi Momy nima ban sani ba".

Tace "au daman kana jin Hajiya na kiran ka kayi shuru, saboda ka raina mutane, ai sai ka fito ka bawa mutane guri, saboda gari ya waye".

Yace "Momy bazan iya fitowa ba".

"saboda me?". Ta tambaya

Momy wlh yau Ban san me ke shirin faruwa dani ba, ko nayi gamo ne tun nafito sallar asuba na had'u da bala'i ko sallar ma banyi ba". 🤣

Salati suka hauyi Inna natafa hannu kace "baka yi sallah ba tom wai me kake yi a cikin bayin ne haka?". Cewar inna

Cikin jin zafin tambayar da Inna tayi mai Sadeeq yace "Wai baki ji nace ina cikin bala'i bane, amma kike sake tamba ta".

Momy ce ta daka mai tsawa "rufe min baki anan gurin ko na ci maka mutun ci, kuma kafito kabawa mutane guri suna son shiga bayan gida".

Sadeeq yace "Amma Momy...".

Katse shi tayi da "ko baka ji abinda nace maka bane?".

"naji". Ya fad'a a ta 'kaice,

d'an matsa wa suka yi nesa da bayin,

Ni kuwa da tun-tuni nike zaman jiran fitowar sa, da naji Momy tace "ya fito". Sai Na 'kara gyara zama na a kan kurer tsakar gida

Saida ya d'auki tsayin minti biyar kafin ya cire sakatar, ya bud'e 'kofar ya fito, babu ko riga a  jikin sa, sai d'an gajeran wando, basu Inna kad'ai ba hatta ni da niyi  zaman jiran fitowar sa, saida na tashi tsaye saboda yadda yayi wani iri, kamar ba yaya Sadeeq d'an gayu da 'kwalisa ba

Yayi wani wuji-wuji dashi idanuwan sa sunyi jawur  se muts-tsuka su yake ga jikin sa duk ya karce sa da farce, harda shedan jini, ba 'karamin ciwuka yajiwa jikin sa  saboda susa ba, hatta da fiskar sa bai bari ba akwai alamun karta, duk ya fad'a fuskar nan yayi zuru-zuru,

mamaki ne kwance a kan fuskokin su Momy

Momy tace "Wai sadeeq me ke damun ka haka kamar me borin jini?".

"Momy nima bansani ba". Ya bata amsa

Yanzu yaji sau 'kin 'kai-'kayin da jikin sa ke yi, sai dai rad'ad'in da fatar jikin sa ke mai,

"to ai saika je ko jallabiya kasa mutafi asbiti". Inji Inna,

"A a Inna ba sai kunje ba don asbitin gari zani kuma da nisa ku zauna a gida". Ya fad'a yana tafiya

ta kusa dani yazo wuce wa, saida muka yi  ido hud'u  dashi  na kwashe da dariya🤣

kallan tsana yayi min, sannan yanufoni dagudu na mi'ke nanufi bayan Momy ina haki, biyoni yayi shima,  da hannu Momy ta da katar dashi san-nan tace "amma walahi Sadeeq kaji kunya kanwar kanwar ka itace abokiyar yinka, ba dole ta raina ka ba, Wallahi ka bada maza wuce kabani guri, kamin ki'kam a gaba kamar wani soja, Ko wannan iftila'in daka fad'a be isheka ishara karabu da yarinyar mutane ba". Momy ta fad'i haka tana nuna mai hanya da hannu

Badon yaso ba saidan yabi umarnin mahaifiyar sa,

had'a ido muka yi dashi nayi masa gwalo ina 'kara yin dariya ciki ciki😄

Yace "Zan kamaki  yarinya wallahi zakiyi bayani".

Inna tace"Ai gashinan alhakin tane wannan abin da ke faruwa da kai, saboda Allah ba azzalimi ne ba saidai bawa ya zalinci kansa".

"Kwarai ma kuwa".  Momy tace

Jikin sa babu 'kwari  ya wuce mu, tashi nayi nima nakoma d'aki, saboda na gabatar da sallar a subahi, sai a lokacin nayi sallar takwas saura, ina idar wa ko kan sallaya ban sauka ba nahau rawa da juyi, saboda na rama a binda sadeeq yayi min gado na koma saboda yau bazan je 'yar kasuwa yin tsokanar safe ba bacci zan koma

♾️♾️♾️♾️♾️ Abangaren sadeeq kuwa koda yaje asbiti, kulawa ta mu samman suke bashi saboda asbitin su na 'yan sanda yaje har gado aka bashi sannan aka saka mai ledar 'karin ruwa, saboda yana bukatar ruwa ajikin sa

Harda allurar bacci a kamai saboda ya sami hutu

♾️♾️♾️♾️♾️ Koda na farka daka bacci 'karfe sha d'aya saura11:00am naji dadin baccin sosai domin ya ragemin damuwa

Kamar yadda nasaba idan natashi bacci mi'ka nayi  babu ko salati, na sauka daga kan gadon, na d'auki brush d'ina na fito tsakar gida nayi, san-nan nanufi falon hajiya, acan na iske su Khadija suna cin waina da miya,

zama nayi kusa da Momy nace "ina kwana Momy".

"lafiya lau". Tace min "kin tashi lafiya?".

Nace "eh Momy lafiya lau". Saboda ni bana son doguwar gaisuwa

Tace "ba inda ke miki ciwo?".

kai na d'aga mata "madallah" ta ce masha Allah haka ake so

Inna na kallah naga ta tasa kwad'an zogale da kuli a gaban ta sai kaiwa baka takeyi,  d'an Murmushi na sakar mata,  ita ma ta maido min

Kana na gyara zama, na saka hannu a kular wainar su Khadija, ina ci ina lumshe ido saboda dad'i

Nace  "Inna wai wannan wainar wane gida ce".

Tace "ta gidan su fulera ce matar d'an tsoho".

"Haba koda naji". Nafad'i yaka yayin da nike kai lomar waina a baki na

"Kice kinyi santi" Murmushi nayi kawai na cigaba da aikawa cikina

Umar ma cewa "yayi ni rabon da naci Waina me dad'in wannan wallahi na manta".

"Umar duk santin ne haka". Inji Khadija

Yace "ai kokema kinyi tunda naga kun-nen ki d'aya sai rawa yake yi".

Kowa a d'akin saida ya dara

♾️♾️♾️♾️♾️ Bayan Sadeeq ya farko daka nan-nauyan baccin da ya d'auke sa,  jikin sa babu kwari ya tashi, a za filo a bayan sa yai kana ya jingi na, yana jin gaba d'aya jikin sa na mai ciwo, ga wata yunwa da ta ad'da beshi da kasala

Likatan ne yazo ya zauna agaban shi dayike a bokin sa ne kuma shima d'an sanda ne, yace "wai Sadeeq dame kai amfani ne?".

d'an shiru yayi kafin yace "nidai a binda nasani natashi da a suba lafiya ta 'kalau amma bayan na d'auki buta ta, naje bayi na dowo nafara jin yana yi na yana can zawa, koda na fara alwala ko fiska ban gama wan kewa ba, tsarkin da nayi yafara damu na, Sai nasa aka kai min ruwan wanka, to na 'kar-'kare maka zance, daka zuba wannan ruwan a jikina kid'an ya sauya salo, sai azabar ta 'karu bayan na sa a mi'ko min sabulun wanka, ba ba nasha wuya fa  sosoi, tun asuba nike a cikin bayi nine har 'karfe takwas saura, wannan raunin duk ni najiwa kaina, saboda 'kyai-'kayin da jikina yake min idan ban sosa ba bana jin dad'i".

Dariya sosai Dr Farooq yakeyi, Sadeeq yace "Kai Farooq banason iskanci fa nifa ban baka labari don kayi min dariya  ba, sai dan kayi  aikin ka".

Dr Farooq yace "ba ba wallahi labarin naka ne gunin ban dariya, sai kace a cikin shirin film".

Duka Sadeeq yakai wa Dr Farooq d'in, amma sai ya kau ce yana fad'in "shege kasamu kenan d'azun kamar wani lagwani kana ta num-far fashi kamar baza ka kai aniji ma ba".

Sauko wa Sadeeq yayi daga kan gadon, Dr Farooq yai saurin mi'kewa, d'akin suka fara za gayewa, Farooq d'in ya'ki barin sadeeq ya kamasa,

Dan kansa Sadeeq d'in da ya gaji ya ha'kura, ya janyo kujera ya zauna yana maida num-fashi, ruwan sanyi Dr Farooq ya d'auko a ciki firiji ya mi'ko masa, yana fad'in "maganin d'an iska kenan gobe ma ka 'kara". Sadeeq d'in amsa kawai yayi be kula sa ba

NI DA YAYA SADEEQ                        بسم الله الرحمن الرحيم

             Chapter 07

_______Ya ansa gorar ruwan ya fara  sha, saida ya shanye ruwan tas sannan yace "malam kayi min ba yanin matsala ta nasan dai ba waccar matsalar bace".

"Eh ba ita bace" Farooq ya bashi amsa

"Amma a bisa bin ciken danayi ya nuna kayi amfani da abu mai saka fatar jikin d'an Adam 'kai-'kayi acikin ruwan da kayi amfani dashi, sannan shima wannan rad'a d'in da kake ji kayi amfani da abu mafi zafi ajikin fata, shiyasa yake maka wannan rad'ad'in". Dr Farooq ne yayi wannan bayanin

Shuru sadeeq yayi kamar meyin nazarin wani abu, be tuna komai ba, Dan haka ya ta'be baki yace "Nidai nasan ban saka komai cikin buta ta ba amma zanyi bincike, saboda abin da mamaki".

"DA dai yafi". Farooq ya bashi amsa ya kuma cewa "katashi muje akwai magun-gunan da zan rubuta maka zasu temaka sosai, wajen  rage maka rad'a d'in da kake ji".

♾️♾️♾️♾️♾️ Ina zauna a kan kujera a tsakar gidan mu, ina dakan kayan miya yamma ne lilis, saiga Ladiyo kawata nan Ta shigo jiki duk kwata, tun daka nesa nike d'aga mata hannu, saboda kada ta 'karaso inda nake, bazan iya jure shakar warin kwatar da ke jikin ta ba Ida nuwan ta  jawur dasu, alamun taci kuka ta 'koshi,

saida nayi dariya mai isa ta san-nan nace "ya akayi ne Ladiyo Ki kayi wanka da kwata a jikin ki kamar sabon shiga hauka".

takaici na ne  ya ishi Ladiyo na dariyar da nike mata, kamar jira take na tambaye ta

Cikin shash-she'kar kuka take cemin "Umma ta ce, ta aike ni na kai mata ni'ka, bayan nakai annu'ko min akan hanyata ta dawo wa gida na had'u da su Habibalo, itada Larai sukai ta zagi na, na'ki kula su ni kuma, nayi 'ko'karin ganin na cigaba da tafiya ta, amma suka hanani wucewa, wai sai nayi dambe". can saiga Atinen Malam Bala nan Shine tace "wa na kama wai jiya ni dake munwa 'kanwar ta duka".

"Ha'kuri na fara bata amma suka samin dariya, wai wallahi sai sun rama wa  'kan warsu dukan da da kika yi mata, shine suka had'u suka yimin dukan tsiya, san-nan suka jefani a cikin kwata". Ta 'karasa maganar hawaye sabbi suna zubo mata ta ciga ba da fad'in "basu tsaya iya nan ba saida Suka zubar da 'kullun wainar da na markad'o".

Wata muguwar dariya ce ta 'kwace min saida nayi mai isa ta

San-nan nace mata "wallahi Ladiyo ke sakarya ce ki katsaya kamar kayan wanki suka jib geki 🤣Baki iya koda mintsilun su ba, Hhmm ai da ni ce koda ya 'kushi da cizo saina rama, kindai san hali na".

"Ni yanzu da ki kazo ki ka fad'a min inyi miki me? ai da zuwa gida ma ki kayi  Umman ki ta miki dukan da zata miki da tuni ya wu ce, amma a nan kina 'karawa kanki laifi ne a gun umman ki, kuma kin santa da jaraba".

Wani sabon kuka Ladiyo ta kuma  fashe wa dashi,

ni kuwa sai 'kyal-'kyala dariya ni keyi harda rike ciki abin nema ya samu

dundu naji an d'uma min a baya na, koda na waigo Inna ce na gani,

tsuke baki na nayi nace "Inna kin samin 'kashin mundi-ri'kin ki ai saiki karya ni".

Cikin jaraba irin ta tso-faffi Inna tace "jaira ba ke kika ja mata dukan ba, amma tana fad'a miki kina yi mata dariya".

Ta juya ta kalli inda Ladiyo take tace "kema ai da naki laifin, Ladiyo kina san kiyi tsoka na amma ba kida 'karfi, kuma tsoka na ta mara tsoro ce, tunda ba zaki iya cire tsoro ba, sai kidena biye wa Siddi'ka idan ba haka ba wataran karyaki za ai".

Jin Inna tace za'a 'balla Ladiyo yasa na 'kara kwashewa da dariya

cikin takaici na Ladiyo tace "ke ai  sunce idan suka kama ki 'balla ki za suyi, Ko waccen su tace tana da cikin ki".

Wani 'katon a shar nayi, Inna dake kusa dani tace "A uzu billah".

Naci gaba da cewa "ke ma kin San kaf 'kauyen nan, na ga gari uban kowa, na wuce ayi min harara bare zagi, kinga ina za aje ga duka, ke dai da ki ke sakarya sai kita tsayawa tunda sun gano lagwanki".

Momy dake jinmu tunsanda Ladiyo ta shigo gidan, tazo ta mi'ko min kud'i 1000k tace "ungo mi'ka mata ta kaiwa  mamar ta".

Saida na amsa kud'in san-nan nace "wallahi Momy dan  kece da bazan iya zuwa inda take ba, ba kuji yadda gidannan yad'au ka ba?".

Duka Inna ta'kara kai min a karo na biyu, amma sai na kauce ina fad'in "ba zaki 'karasa ni tun kafin lokaci na yayi ba da saura na".

"Sha-'kiyi ya". Tace min har Talle ne zai yiwa audi gori?".

"tab wai me kike nufi? ni kika yadawa magana ko wa? Yo ai ko ke ba zaki nuna min wanka ba bare Ladiyo". Na 'karisa fad'a ina murgud'a baki

Hanci na na toshe da dan kwalina san-nan na nufi gurin da Ladiyo da take tsaye, nesa kad'an da ita natsaya nace "mi'ko han-nun ki" mi'ko han-nun nata tayi, na saka mata kud'in nace "yau Allah ya 'kwace ki wajen Umman ki, da kinci duka biyu".

Godiya Ladiyo tayi wa Momy sosai, zata wuce nace mata "mu had'u a yar kasuwa anjima". da "Tom" tabani amsa

Inna kuwa sai mita take wai Ladiyo bata da wayau, Momy na bata ha'kuri tana cewa "sha'a nin yara kenan sai  ha'kuri".

♾️♾️♾️♾️♾️ A bangaren Sadeeq kuwa yana dawo wa  gida ana kiran sallar magriba, d'akin sa yabud'e ya ajiye ledar maganin da Dr  Farooq ya rubuta ya siyo, saboda ba suda shi a abitin su kuma yace "zai rage masa zafin rad'a d'in da kaye ji".

  Fitowa yayi daga gidan, yanufi masallaci, anan yayi alwala aka gabatar da sallar magriba da shi, bayan an idar mutane sun fara raguwa ya mi'ke, saboda ya biya bashin sallolin da ake binsa, ai kuwa ya fara jero sallolin saida ya idar dasu  kaf, ashe a kwai wani mutum da ya lura da Sadeeq d'in, tun sanda yafara sallar, ba 'kara min mamaki yayi ba da yaga matashi me jini ajika irin sadeeq ya tsaya yana had'a sallah

Beyi 'kasa a gwuiwa ba, yaje ya mi'ka masa hannu suka yi musabaha, kana yace "yalla'bai Allah yasa dai lafiya naga sai salloli kake jerowa kuma ga dukkan alamun ba nafila bace farrila ce, saboda tun sanda ka fara nike lura da kai".

shiru sadeeq  yayi, saida ya gama 'karewa mutumin kallo tsaf dat-tijone dan gashin kansa ma a kwai fur-fura, gwauran numfashi Sadeeq ya sauke, saboda bai san ya dat-tijan zai d'auki lamarin ba, amma zaifa d'a mai gaskiya tunda shi ya bu'kaci jin dalili

Bayani sadeeq d'in ya shiga yimai dallah dallah, a kayi sa'a dat-tijan ya fahimce sa, Fatan samun lafiya yayi masa, daga bisani ya mi'ka masa hannu suka kuma yin sallama dat-tijan ya tafi

♾️♾️♾️♾️♾️ Ni kuwa ban samu fita daka gida ba sai bayan sallar Isha'i, koda Allah yabani sa'a nafita daga gida, ina tafe a   hanya ina tsokanar duk Wanda naci karo dashi, raina fes saboda Izuwa yanzu nayi tsokana har ba a dadi, nafi tare masu yin talla kuma nace "dole sai munyi dambe". Duk wanda ya'ki biye min ayi sai na zubar masa da abin tallar na ruga da gudu ina dariya

Hankali na kwance nike tsokana ta yanzu haka wata me gyad'a na tare, nayi nayi da ita muyi dambe amma ta'ki tace "ba abinda ya futo da Ita kenan ba". Saida nayi shewa kamar ina gidan biki nace "yo ni abinda ya fito dani kenan ko kina so ko bakya so sai munyi dam-ben nan". Na 'karasa fad'a ina 'ko 'karin kama tiren gyadar, ban lura da kowa a gun ba ido na ya rufe, naji caraf an dam'ke min hannu, koda na waigo da kaina saboda nayi masifa, sai naga yayan yarinyar ne fuskar sa a murtuke babu alamar wasa yace "yau me ra bani da ke a gurin nan sai  Allah, zakici ubanki daman na dad'e ina Addu'ar irin wannan ranar sai gashi kin kawo kanki har gida, saboda kin addabe yaran unguwa ko ina yara labarin ki suke yi, kuma gaki 'yar 'karama bare nace jiki gareki kike tsorata su dashi".

Sai yanzu na 'karewa layin kallo a she a 'kofar gidan su yarinyar nike

Inada taurin kai bazan ta'ba iya bashi ha'kuri ba, ko da kuwa zai kashe ni, cikin 'karfin hali nace "dalla malam ka sakeni ko nayi maka sharri".

ya d'aga han-nun sa da zummar ya mare ni, sai yaji ance "'kara mata".

Sai da gaba na yafad'i, saboda me muryan ko a mafar ki naji yayi magana sai na gane, bare kuma a zahiri

sauke hannun sa yayi, ya fasa mari na, ya maida duban sa izuwa inda yaji maganar, saiga yah Sadeeq ya bayyana cikin takun sa na isa da 'kasaita

Har inda muke ya 'karaso  bai tambayi ba'asi ba, yaciro belt d'in wan-don sa yace wa matashin "ungo wannan kazane ta dashi nakega kamar zaifi shigan ta kuma han-nunka baze maka zafi ba".

A tsorace matashin  ya kalli yah Sadeeq saboda ya shaida shi kuma yasan ni kanwar sa ce

Cikin in-inar magana matashin yace "yalla'bai nama ha'kura tunda kayi magana". sai a lokacin ya sakar min hannu

Da alamar yah sadeeq ba haka yaso ba, so yayi a daka ni, dan yabud'e baki zaiyi magana kenan na falla da gudu ina cewa "Allah ya isa ban yafe ba ku duka 'kartan banza, masu fad'a da 'yar cikin su". 😄

Duk kansu sunji a binda nace saboda na d'aga murya ta sosai, kuma dama haka nike so, shi dai matashin mamaki abun ya bashi, a cikin ransa yake cewa "yalla'bai guda nama wannan rashin kunyar ina ga shi, tabbas tunda nawa yalla'bai babu wanda bazan mawa ba".

Yah sadeeq yanada Alheri bashida rowa yana so ya kyauta ta wa na 'kasa da shi, saboda haka ya ciro kud'i daga aljihun sa ya bawa matashin 'yan Naira Ashirin sababbi gada gal

Matashin ya ansa yana mai godiya 

Ban dawo gida ba sai 10:00 pm saura kamar dai jiya, bana kallon gaba na a guje na shigo cikin gidan, yah Sadeeq da d'auko kular a bincin sa kenan, na buge sa abinci ya zube, koda na lura da abinda nayi d'aki na na shige aguje  na saka saka ta, ina maida numfashi

su momy sunga abinda yafaru

Gurin Inna ya koma "Inna ina abincin yarinyar nan?". Ya tambaye ta

"gayi can". Tanu na masa wani kano dayike arufe cike da shinkafa da miya harda d'an naman kaza, d'auka yayi zai fita

Momy tace mai  "dawo mata da abincin ta kafin na  sa'ba maka". Inna ce ta katse ta da fad'in "haba Aisha yanzu ai itace da laifi bakiga yadda ta zubar mai da abin-cin sa  ba, kuma idan banatan ba mai zaici? kinsan Garba baicin abin-cin waje sai na gida, gashi dare yayi bare a sake girka masa wani".

Ta cigaba da cewa "mutumin ma da ba lafiya gare sa ba". yanzu fa yake ce mana "saida aka 'kara masa ruwa da yaje asbiti kuma ance saiya ci abinci sannan yasha magani". "tunda ba tajin magana ita ta kwana haka, yi tafiyar ka Garba kaje ka ci abin cinka". Yace "na gode Inna" ya fice daga falon

khadija kuwa cewa tayi "wai Inna ina Siddi'ka ke zuwa ne haka idan tafita sai  dare take dawo wa kuma ba'a sanin sanda take fita".

"Ina kuwa zata in ban da yar kasuwa, ai nan take zuwa taita tsokanar mutane Sam bata san zaman gida, karatun ma yanzu taki shi kwata kwata, babu muhammadiya babu na zamani".

"Allah ya kyauta" khadija tace "amma wallahi Sam Siddi'ka bata wa kanta adalci ba saboda a wannan zamanin ilimi shine kan gaba".

Momy ce tace "ai gobe Daddyn ku zai zo inaga da ita zamu tafi, Hajiya saidai kiyi ha'kuri, tunda bazaki bimu ba, ko yar aiki sai a d'auko miki, amma karatun Siddi'ka yana da mutu'kar muhim-manci, idan ba abar ta tayi ba tom nan gaba bazata gode mana ba, zata d'auke mu a matsa yin azza-lumai ne".

jin jina kai Inna tayi alamar gamsuwa tace "Allah yasa haka shine mafi alkairi".

Umar ne yazo ya buga min 'kofa daga ciki nace "waye anan?". "Umar ne". Yace

Na bud'e masa ya shigo na maida 'kofar na rufe, kamar dai jiya, yau ma tambaya ta yayi labarin abinda yafaru, na kuwa bashi labari harda had'uwa ta da yaya Sadeeq, yayi dariya sosai amma yace min "yayi fushi tunda ban nemeshi ba sanda zan tafi".

Ha'kuri nashi ga basa da cewa "nima bansan zanyi nisa ba naje siyo alewa ne, naje da kai gobe".

Yace "uhm abinda gobe Daddy zaizo kuma gida zamu tafi

Ji nayi gaba na na fad'uwa, amma saina daure nace "da gaske gobe Daddy zai zo?". Umar yace "eh wallahi nima a bakin Momy naji". Nace "to Allah ya kawo sa lafiya".

"Ameen" Umar ya fad'a

"ina yaya Sadeeq?". na tambayi Umar

Yace "ya d'auki a bin cin ki ya tafi d'a kin sa, kin san baida lafiya".

ban san sanda dariya ta 'kwace min ba,  saboda na manta da abinda yafaru, sai  yanzu da Umar ke fa d'in baida lafiya na tuna,

"wai lafiya yarki. Aunty Siddi'ka?".

Nace 'kalau Umar wani abu na tuna, shiyasa kaga ina dariya".

"Muje tunda wancan mugun benan ko Indomie na girka don yunwa nike ji".

NI DA YAYA SADEEQ                   بسم الله الرحمن الرحيم                       Chapter 08

_______Yana yin tsarin ginin gidan mu 2 bedroom ne amma a ko wani d'aki anyi kofar da mutum zai iya bi ba sai yabi ta falo ba, sai d'akuna biyu da suke a tsakar gida d'ayan na hanyar waje shine d'akin yah Sadeeq,sai wanda idan su Momy sun zo suke sauka a ciki, a kwai kitchen a tsakar gidan da bayi,

Inna bata son amfani da kitchen din d'aki tafi sabawa da na waje,

amma ni nakan yi amfani dashi idan zanyi jagwal-gwa-lo na

Kitchen d'in na shiga na bud'e durowar da nasan muna ajiye Indomie a cikin ta na dauki guda d'aya

Gas na kunna, ruwa na fara tafasa wa nazuba Indomie d'in sannan nakawo tarugu 1 nasaka nazuba mangyad'a a ciki ina juyawa, sai ga Khadija tale'ko kitchen d'in cikin zolaya tace min "ga yaya Sadeeq can afalo".

yace "mai kwatar ki yau sai Allah". Inna tayi bacci tun d'azu, Momy kuma ta tafi d'aki, daga ni sai Umar ne a falo.

hantar ciki na ce tafara kad'awa jikina yafara rawa na kasa magana, bani da tsoro amma ina tsoran had'uwa ta da yaya sadeeq saboda ba da wasa yake min ba, amma duk da haka idan rashin kunya ta, ta tashi yi masa nike

Ad'an kid'ime nace "bari na fasa ihu tun kamin yacin min kinga su Momy za suji su zosu zo su cece ni".

Saka tafin hannaye na nayi na toshe kunnuwa na, saboda inyi 'karar iya karfi na, zan 'kwal-lara 'kara kenan Khadija tayi saurin toshe min baki da tafin hannun ta, tana 'kyal-'kyala dariya

Tace "nad'auka ked'in jaruma ce a she ba haka bane kamar ba kece shekaran jiya kika cemin sai kin rama dukan da ya miki ba, taya zaki rama kina wannan tsoran?".

"Kedalla malama sakeni nayi ihun neman agaji".Nace mata

Tana dariya tace "tsokanar ki fa nikeyi".

Sai alokacin nasaki ajiyar zuciya, nabi ta da duka ta fita tana dariya,

koda na duba Indomie na har ta dawu ta fara kamawa, kashe gas nayi, anan kitchen d'in na zauna, a cikin tukunyar naci, inaci ina santi saboda tayi mini dad'i kuma nayi mata irin  dahuwar da nikeso

Bayan na gama ci ne na bud'e baki na sosai na saki wata uwar gyatsa babu ko alhamdu lillah Na mi'ke tsaye nayi  mi'ka

D'aki na na wuce inda natar da Khadija na sharar baccin ta hankalin ta kwance, kan gadon nim.

Washe gari ban farka da asuba ba sai Misalin 8:9am Khadija babu irin tashin da bata yi min da asuba ba, akan nayi sallah amma na'ki sai ma 'kara gyara kwanciya ta da nayi, Kamar yadda nasaba tashi haka nayi babu ko addu'ar tashi daga bacci, na sauka a kan gadon, brush d'ina na d'auka, ina tatsa makilin ne Khadija ta shigo fiskarta d'auke da  murmushi, da ganin bakin ta a kwai magana, "au ashe kin tashi daman ke nazo tasa wallahi". Ta fad'a tana matsowa kusa da ni

"eh na tashi" nace mata "wai yanaga kina ta murmushi ne?".

Tace "ba dole ba Daddy fa yazo" shi yace "na taso ki saboda ya tambaye ni kina ina". Nace kina bacci".

"amma wannan karon yazo dawuri gaskiya" nafad"a ina ajiye makilin d'in hannu na

Tace "Eh". naji yana cewa Inna "da karfe 2:pm jirgin su da zai wuce lagos zai tashi shiyasa yayi sammakon zuwa".

Jin jina kai na nayi, alamar gamsuwa "to bari nayi sallah" nace tare muka futo  ta nufi d'akin hajiya Inna

Ni kuma na nufi rijiya na janyo ruwa na zuba a bokitin wanka, na kai bayi saida na fara yin wanka sannan na d'aura al'wala

Tawul na d'auro ajiki na, amma irin 'katon nan ne, kuma na wanke kaina babu ko d'an kwali haka na fito daga cikin bayin

Adai-dai lokacin yah Sadeeq ya shigo cikin gidan, had'a ido mukayi, saida ya 'kare min kallo tsaf, sannan yaja dogon tsaki, shasha ya fad'a afili, kana ya wuce ya shiga cikin falon

Saida ya wuce sannan nima na wuce d'aki na, wata doguwar rigar atamfa na ciro mai launin blue da ruwan hoda, baseline na shafa a jiki na sannan na saka atamfar, na d'auki hijabi na nasaka na gabatar da sallar asuba

Bayan na idar na  nufi falon hajiya, ina jin gabana yana fad'uwa, narasa mai yisa amma tun jiya da Umar yace "Daddy zai zo" gaba na ke fad'uwa amman yanzu bugun zuciyar tawa yafi tsanan ta

Daurewa nayi, na shiga cikin falon baki na d'auke da  sallama, nasamesu su duka harda yaya sadeeq d'in, suna karyawa, Daddy da Inna da yaya Sadeeq suna cin d'an wake,  Khadija Momy Umar. Kuma  waina suke ci

Daddy ne ya dube ni yace "wa'alaikum'ssalamu d'iya ta shigo ga wuri ki zauna, ya nuna min tsakanin sa da na yaya Sadeeq, na 'karasa  na zauna a tsakanin nasu

Sannan nace "ina kwana Daddy".

"Lafiya lau". Yace min "na same ku lafiya?".

"lafiya lau Daddy, ya hanya?". nace

"Al'hamdu lillah ". yace min, yana mi'ko min cokali yace "bimismilah me sunan manya".

Ina lura da yanayin yah Sadeeq ya canza tun sanda na zauna, ya wani d'aure fiska sai mutsu-mutsu yake yi, ina saka cokali na cikin kwanan yana cire nasa yami'ke tsaye, Daddy ne yakalle sa, yace masa "ya-ya ana cin abinci ka tashi". na 'koshi ne Daddy".

"dawo ka zauna sai mun cinye da kai".

Badan ran Sadeeq  yaso ba, haka ya dawo ya zauna ya maida cokalin sa, ina lura da yadda yake cin d'an waken kamar yana cin magani.

Misalin karfe goma 10:00am Daddy zaune a kan kujera Inna na kusa da shi Momy na 2 cter, ni da Khadija na zaune  a 'kasa kusa da Momy, yah Sadeeq kuma na gefen Daddy zaune a 'kasa kanshi a 'kasa yana danna wayar sa

Daddy yayi gyaran murya

Sannan yafara da cewa "da farko ina 'kara jad-dada godiya ta ga Allah ma d'aukakin sarki da yabani damar aiwatar da wannan 'kudirin nawa, tsira da aminci ya tabbata ga fiyayyen halitta annabin mu Muhammad (S. A. W). Bakomai ne yasa na taraku anan ba, saidan ke Siddi'ka me sunan manya, ya fad'a yana kallo na, ina san yau d'in nan na  ai'watar da 'kudirin mahaifiyar ki akan ki, Ina fatan zaki yimana biyayya, nasan baki da matsala, saboda mun isa dake ne zamuyi abinda mukesan yi yanzu, ina so kisan bakida Wanda ya fimu a kaf fad'in duniya, bazamu ta'ba cutar da ke ba".

Tun da Daddy ya fara magana gaba na ke fad'uwa, shin wani kalan 'kudiri ne wannan da har Daddy yace 'kudirin mahaifiya ta ne". Banida wannan amsar saboda haka naci gaba da sauraran abinda Daddy ya cigaba da fad'a

"naso ace sauran 'yan uwanku suna nanan, amma duk da haka kuma kun isa shaida,  kuma akwai abokai na guda biyu wa'inda tare dasu  zamu tafi lagos, nayi magana dasu, saboda muhimmancin abinda zan tattauna daku zasu biyo tanan".

Kallon Hajiya Inna yayi yace "Hajiya ko  akwai abinda ki ke san fad'a".

Tace "eh ina da abin fad'a". yace "to muna saura ranki".

Tace " 'Karami". Haka Inna ke kiran Daddy karami "ni abinda ke damu na yadda, Garba ya tsani Siddi'ka, kamar ba 'kanwar sa ba, Kaf 'kauyen nan babu wanda bai san da zaman 'kiyar-yar Siddi'ka a gun Garba ba, a gaban kowa nuna wa yake, a gida bai 'kyale ta ba, motsi kad'an tayi ya make ta".

Wani gwaran numfashi Daddy ya sauke, sannan ya fara yiwa Yaya Sadeeq fad'a ta inda yake shiga ba tanan yake fita ba sosai Daddy yayi wa yaya Sadeeq fata fata

Sannan ya maida kallan sa I zuwa ga Momy yace "Aisha fa kina da abin da zaki ce".

murmushi tayi irin  na su na manya tace "ai kai da Hajiya kun gama fad'an duk abinda zan fad'a, sai dai a'kara yiwa sadeeq fad'a a kuma ja mai kunne, sai muyi  musa fatan Allah yasa alkairi".

"Ameeen" Inna tace yayin da Daddy yace "alhamdu lillah".

Daddy yace "mai sunan manya matso nan kusa dani kinji". Jikina a sanya ye na matsa kusa na zauna a d'ayan bangaren da ke kallon yaya Sadeeq  sai ban kamin harara yake a sace nayi kamar bansan yanayi ba

Dafa kaina Daddy yayi yace "Allah yayi miki albarka". "ameen". Nace

Sannan yaci gaba da cewa". Siddeeqah daga yau yayan ki Sadeeq zai dunga amsa matsayi buyu a gurin ki wato yayan ki kuma mijin ki insha Allah yau ne zan aiwatar da abinda nasan kanwata zatai farinciki dashi wato auran ki da Sadeeq"

duk da ban wani san maye *Aure* ba amma naji sam ba aimin adalci ba

a tare nida yah Sadeeq  muka mi'ke tsaye, duk kannin mu idan mu a waje alamar rashin fahim ta.

" Koma ku zauna" Daddy ya fad'a, jikin mu babu 'kwari haka muka koma muka zauna, Khadija ma dake zaune mamaki ne yacika ta shiko Umar ko ajikin sa Inna kuwa da Momy daman sun san da batun

"'Kwarai kuwa abinda kukaji nafad'a haka ne ba mafarki kuke yiba, domin wannan shine burin 'kan wata Aminatu". 'Kwalla ce ta cika idonun sa yayin da ya kasa 'karasa maganar Handkerchief yaciro cikin aljihun sa yana share 'kwallar da ta zubo masa

Da irin murayan kuka, Daddy ya cigaba da cewa "auren ki da Sadeeq shine burin ta, bamu sani ba ko a raye take ko amace, kimanin shekaru goma sha biyu da wasu yan wattani akai kenan tun tana goyen ki". ya nuna ni "nasan kunsan komai ba sai na 'kara tada muku da zancen ba, saboda bana son na tada mana hankula".

tuni inna tafara shash-she 'kar kuka Momy ce keta faman bata ha'kuri

Da 'kyar aka shawo kan Inna tayi shuru

Ba 'karya Dady yayi ba duka family an san labarin 'batar mahaifiya ta amma bamu san yadda al'amarin ya faru ba

Daddy yaci gaba da fad'in "Siddi'ka sai dai kiyi ha'kuri, naje  har gidan ku da 'kyar nasa mu ganin mahaifin ki, na je masa da batun auren ki, yace min shi babu ruwan sa  yama manta dake cikin 'ya'yan sa  ba tun yauba ai ya fad'a mana ya bar mana ke, idan yanka ki zamu yi, muyi, shi baya da matsala babu ruwan sa". ya 'kara da cewa ai tun ranar da Amina  tabar gidan nan  na manta da duk wani abu da yashafe ta yanzu haka abinda yasa bazan sa karnuka su fidda min kaiba saboda baka sani ba, amma yanzu tunda kasani kada in'kara ganin ka akoafar gidana kai ba kai ba ko Siddi'ka d'iyata ce tazo sai nasa kar nuka suncin ye naman ta d'an ye, saboda haka Get out in my house".

  jiki na babu 'kwari Siddi'ka na fito daka gidan ku

Ban ta'ba jin tsanar mahaifina irin na yauba kuka nike sosai ina tir da halayen sa kowa a d'akin jikin sa yayi sanyi Daddy ne ke shafa min kai yana bani hakuri

"Siddi'ka ki cigaba da ha'kuri Allah zai miki canji da mafi alkairi, ki cigaba da kai kukan ki gurin Allah saboda shi Allah baya barin zalinci". Kuma kamar yadda nace "yau za a d'aura miki aure da sadeeq idan anyi sallar juma'a babu fashi".

SADEEQ ne zaiyi magana Daddy ya katse sa da fad'in "zan sa'ba maka sadeeq, Ko na tambaye ka ne?".

bazan iya musa wa su Daddy ba, amma shin maye aure nashi ga uku nake fad'i a zuciya ta, yayin da nike jin bugun zuciya ta yana dad'a 'karuwa

NI DA YAYA SADEEQ                      بسم الله الرحمن الرحيم               Chapter 09

_______Na shiga uku ni Siddi'ka Suleiman, anya su Daddy suna 'kauna ta nasan kaf duniya babu wacce Sadeeq ya tsana kamar ni, amman wai yau ni ce zan zama matarshi

"Kutashi kutafi Allah yayi muku albarka". Daddy ne ya fad'a haka

Sadeeq yariga ni tashi saboda ni jikina babu kuzari

"kai Sadeeq" Daddy yace "ka kira abokanan  ka na kusa a waya ka shaida musu".

Murya acan cikin ma'ko garo Sadeeq ya cewa Daddy "ba sai sun shaida ba". Yana gama fad'ar haka ya fice

A masal-lacin juma'an dake garin buruku aka d'aura auran SADEEQ ALIYU MAI GORO da amaryar sa SIDDI'KA SULEIMAN d'umbin jama'a sun shaida d'aurin auren duk da kasan cewar babu ango da abokanan sa, Daddy ne yayi wakil cin Siddi'ka, inda d'aya daga cikin abokan Daddy da suka hallar ci taran, mai suna Alhaji Imran yayi wakilcin Sadeeq, auren da aka d'aura abisa sadaki dubu tamanin, lakadan ba ajalan ba, yayin da Alhaji Imran ne ya biya sadakin

A kwai 'yan 'kauyen Dande da dama, dasu ka samu halartar zuwa masallacin, saboda su gabatar da sallar juma'a da yawan su mamaki suke saboda kowa yasan tsamar dake tsaka nin Sadeeq da  Siddeeqah amma wai yau ya zama mijin ta ko da shike daman ance idan zaka yi 'kiyayya kada ka tsanan ta haka ma soyayyar.

Da haka taro ya watse koda Daddy ya dawo gida anne mi Sadeeq anra sa kuma an kira wayar sa a kashe

Siddi'ka kuwa tun sanda ta shiga d'aki take raira kuka, rarrashin duniya anyi mata amma ta'ki barin kukan kamar ma dad'a zuga ta suke yi, haka suka gaji da lal-lashin ta suka  zuba mata ido, saida Daddy yafa d'awa su Inna zai shigo dasu Alhaji Imran Sannan yaje ya shigo dasu, a falon Hajiya Inna suka zauna daman su Hajiya Inna sun girka shinkafa da miya Khadija ce keta hidama da ba'kin Daddy Sai da suka ci suka sha sannan Inna tazo suka gaisa

Suka yi mata Allah yasanya alkairi anan Daddy yayi mata sallama yace "su zasu wuce Abuja a can jirgin su zai tashi izuwa lagos

"To bari na kira maka Aisha d'in ko". Inna ta fad'a tana 'ko'karin mi'ke wa

cikin sosa kai Daddy  yace "ai na sallame su suma nan bada jimawa ba zasu wuce" mamaki ne yakama Inna saboda ita dai bataga sanda 'karami yayi magana da Aisha ba

Hajiya Dady ya kira sunan ta "da mai sunan manya zasu tafi nayi maganar yar aikin za a nemo miki nanda kwana biyu".

"Wace yar aiki! 'karami duk yaran dake ci'kin Dande basu isa ba har sai an nemi wata, ai ko Ladiyo 'kawar Siddi'ka na yiwa iya-yen ta magana tunda yarinyar ta iya aiki, kuma ta ma girmi Siddi'ka d'in, Nasan baza ta 'ki ba, sai ta dunga zuwa tana tayani d'an wanke wanke da shara tama dunga d'ebe min kewar Siddeeqah d'in, idan wata yayi kana yima ta d'an ihsani".

"babu damuwa" Daddy yace yana mai ciro kud'i daga aljihun sa masu tarin yawa, 'yan dubu dubu ya mi'ka mata

"q'Karami kud'in wancen watan ma daka bani suna nan ban taba suba saboda duk abinda nike so akwai a gidan nan da ka bar shi kawai a gurin ka Allah yama albarka".

Hannun ta Daddy ya kamo yasa ka yan bandir d'in 1000 guda biyu "haba hajiya ki karba koda sadaka ne kinayi dasu  idan ki ka ga mai buka ta".

Godiya Inna tai ta kwara rowa 'Karami tanayi mai addu'ar Allah yatsare

"Ina mai sunan manyan take ne Hajiya?". Daddy ya tambaya

"ai tun sanda ka fita ta shiga d'aki tana rusa kuka mun gaji da lal-lashi ne muma".

"Wani d'akin?".

"na can karshe". Ta bashi amsa

Tashi yayi ya cewa abokan sa "minti biyar".

A kan gado ya same ni kwance nayi rufda ciki 

Siddi'ka Daddy ya kira suna na cikin sas-sanyar murya

Inaso kisan duk abinda ha'Kuri bai bawa bawa ba a rayuwa rashin sa ma ba zai ba da ba, kuma wannan shine burin mahaifiyar ki, tin sanda aka haife ki tace "idan Allah ya raya ki d'an ta Sadeeq shine mijin ki ko bayan baran ta mu cika burin ta, A halin yanzu bamu san awani hali Amina maman ki take ciki ba, zai iya yuyuwa tana nan a raye nesa damu, zai kuma iya yuyuwa Allah ya d'auki ranta, amma muna nan muna addu'a idan har Amina tana a raye Allah ya bayyana mana ita, nayi hakanne a yanzu saboda bani da tabbacin zan 'kara wasu shekarun a raye, nasan ko bayan babu raina na cikawa kanwa ta burin ta za tayi alfahari dani, kiyi mana biyayya amatsayin mu na iyayen ki bazamu taba cutar da ke ba zakiga ribar abun nan gaba".

Duk maganar da Daddy yayi na kasa d'ago kaina, Ko motsin kirki na kasa ina nan a yadda ya shigo ya sameni, jin shirun da nayi ne naji ajiki na ya fita daga d'akin, kaina na d'ago ina 'karewa d'akin kallo Bansan mai nike nazari ba amma inajin kamar raina zai fita

Umar ne yashigo hannun sa d'auke da kular abinci har kan gadon ya hau yace "aunty Siddeeqah please kada kicemin a a don soyayyar da kikewa goggo Amina ki tashi kici abincin nan nasan dai kina mutu'kar santa kuma duk 'yar da aka ce tayi abu dan iyayen ta to indai tana son su za tayi".

Jin Umar ya ambaci mahaifiya ta na tashi zaune saboda babu 'yar da zata'ki mamar ta "mi 'komin kular". Nafad'a murya ta a dashe

Koda na bud'e shinkafa ce da miya har da nama a ciki, cokali nasa na fara cin abincin amma kwata kwata bemin dad'i ba ji nike  kamar ba asaka  magi aciki ba

"Umar wai haka abincin nan yake?". Na tambaye sa

"mai yayi?" shima ya tambaya

"naga kan infara ci yana ta zuba 'kam shi yanzu kuma da nike ci wallahi ji nayi kamar inacin magani".

Kallo na yayi muka had'a ido dashi yace "aunty Siddeeqah inaga bakin ki ne domin kowa ya yabi girkin nan yadda yake da kamshi haka yake da dad'i abaki ma".

"To iya magana". Nafad'a ina tura masa kular abincin

"Kaddai har kin 'koshi". Yace yana kallo na

"na 'koshi mana tashi kasa momin ruwa".

"To" yace ya fice daga d'akin, jim kad'an sai gashi da ruwa a cup

yace "Momy" tace "kiyi wanka yanzu gata nan zuwa".

"To". nace

dama akwai bayi a d'aki na amma tsabar neman rigama yasa bana shiga, kuma da sabo dan munriga munsaba da bayin tsakar gida tun kafin  a maida mana gidan mu ginin zamani.

Yaukam ciki na shiga wanda nike tsokanar ko sunan sa ma bana son inji ankira min

Ban wani dad'e ba na fito daka bayin kaya na tarar abakin gadon da alamar sababbi ne harda bra da fnt, dakakkiyar shadda ce marun kalo dinkin doguwar riga taji aiki mai kyau da birgewa wanda ya dace da ita.

Ina cikin mamaki saiga Khadija ta shigo fes da ita cikin wata tsaleliyar atamfa "cikin zolaya tace "amarsu har yanzu baki shirya ba Koda yake daman shirin amare ance yana da dad'e wa, sai kiyi kishirya dan ke kad'ai muke jira".

a kwati na na nufa saboda na d'auko kayan da zan saka,

  da mamaki Khadija tace "Siddi'ka baga kayan ki nan ba akan gado". Momy tace "su zaki saka".

Hau shin kowa nake ji cikin masifa nace wa Khadija "naji to sai ki ban guri".

Sai da ta 'kyal-'kyale da dariya sannan tace "amarsu kada in 'bata miki rai naji ance ba'a san a 'bata ma amarya rai, musamman ranar d'aurin auren ta, idan ni baki bud'e min ba zaki bud'e ma yayana".

Khadija tagirme ni da 2 years nasan ba zata rasa sanin aure ba tunda ita abirni take kuma tana zuwa makaran ta, sa'banin ni da nike yawan gad'a a gari.

Tana fita na rufo 'kofar sai da na shirya tsaf sannan nafito sai 'kam shin turare ke tashi Da alamar kan a kawo min kayan sai da aka fesamusu turaruka masu 'kam shin gaske da tsada

buga 'kofar naji a nayi koda na bude Umar ne hannun sa d'auke da jaka da takalmi da gyale duka masu ruwan madara Yace "Momy tace in kawo miki ki saka idan  kin shirya ki fito".

Kar 'ba nayi takalmin irin mai tsinin nan ne ni kuma banason irinsa koda nasa tafiya d'aya buyu na turgud'e

Wata yar karamar jakace kalar dai ta amare a hannu na rike ta, yayin da gyalan na yafa sa a saman kaina.

A gaskiya ina son kwalliya a rayuwa ta saboda haka nike tafiya ina taku d'ai-d'ai duk da ban iya tafiya da takalmin ba lokaci zuwa lokaci ina turgud'ewa Amman hakan bai hana ni yin yanga ba, naman ta da wani lamarin aure

Afalo nasami su Momy duk sun shirya

"Momy wai ina zamu haka?". Na fad'i  haka ne sanda nike zama kusa da Inna

"Abuja". Momy ta bani amsa

zaro ido na nayi nace "Abuja kuma Momy shine zaku tafi da ni?".

"Eh" kawai tace min narai-narai nayi da ido 'kwalla na zubo min Daman koda nai wanka banyi kwalliya ba ko hoda ma ban shafa ba, saboda haka na cigaba da yin kuka na ina share 'kwallar da bayan hannu na

Inna ce ta kama  hannu na tana matsar kwalla, ba tare da tace min komai ba

Cikin kuka nace "Inna kada kibari atafi dani mana Inna nasaba dake, bazan iya rabuwa ba dake ba, nasan wannan tafiyar ba irin wacce na saba yi bane saboda haka jiki na ke bani, nidai gaskiya bazan je ba".

Cikin sanyin murya Inna tace "to ba gasu Khadija ba acan kuma akwai su Jiddah, baki da damuwa zaki saba kuma duka 'yan uwan ki ne".

"Siddi'ka inaso na ingan ta miki rayuwa ne, saboda 'Karami yace min idan ban bar ki kinyi karatu ba nan gaba dani zakiyi kuka".

Ina sharar 'kwalla nace "Inna ni ba zanyi kuka dake ba ki yarda dani da iya gaskiya ta nike magana".

Daga haka bata 'kara ce min komai  ba

Momy ce ta kama hannu na ta yima Inna sallama ina kuka ina kallon Inna haka na baro ta

daman driver mu yake jira a bakin 'kofar fita naci karo da Ladiyo data ke 'ko 'karin shiga gidan mu

A d'an tsora ce ta kalleni sai tayi baya

Bance mata komai  ba nashi ga mota idan ta naga ya kawo 'kwalla kuma ta bani tausayi, ganin haka nayafito ta da hannu aikuwa da gudu tanufo ni

"Siddi'ka ina zaki haka ko sallama babu?".

"Birni mana".

"inda kike zuwa?".

kai kawai na d'aga mata

"Amma shine  wannan karan ko sallama babu?".

"nima bansan da tafiyar bane  ladiyo kuma karatu zanyi a can d'in ba yanzu zan dawo ba".

"Karatu fa kika ce Siddi'ka, mai zakiyi da makaran ta?".

"Nima bansan me zanyi da ita ba  Ladiyo amma dai an cemin tana da mutu'kar amfani kuma nan gaba zai temaka min zanji matukar dad'in karatun".

Cikin sanyin murya Ladiyo tace "to  Allah ya bada sa'a Siddi'ka don Allah kada kimanta dani".

Tabani tausayi sosai nasan kaf kauyen nan Ladiyo ba tada kama ta kuma nima banida kamar ta Wata ran ma ni zanyi tsoka na amma sai inja mata duk da haka bai sa ta rabu dani ba

Nace "Bazan manta dake ba Ladiyo zan dawo gare ku Ina yi miki fatan alkairi kema".

"Ki shiga gurin Inna kice injini taba ki kayan sawa na gabaki d'aya".

"To" tace tayi min  godiya mukayi sallama ta shige gidan mu

A lokacin su Khadija sun shiga mota driver yaja muka d'au hanya

NI DA YAYA SADEEQ                      بسم الله الرحمن الرحيم

                 Chapter 10

                GARIN ABUJA

   _______bamu wani tsaya akan hanya ba Dan Momy tace "duk mai uzuri yayi ha'kuri har sai munje gida saboda ance mata hanya babu kyau". Da misalin 'karfe 3:25pm muka isa garin birnin tarayya Abuja, tun daga unguwar zaki san ba irin unguwar nan ce ta kowa da kowa ba sai d'an wane da wane tunda ga wajen gidan Daddy zaki san gidan manya ne saboda ko fulawowin kansu da aka zagaye gidan dasu abin kallo ne, ba sai ka shiga daga ciki ba, yawancin gida jen un'guwar ginin gidan sama ne, idan ki kaga wannan sai kiga duk yafi kyau, amma kina ganin wani sai kice wancen bai kai wannan ba to haka dai gidajen unguwar suke, na wane yana wane na wane,

Ba yau na saba zuwa ba amma har yanzu  na kasa ri'ke sunan un'guwar Saboda ita kan ta sunan un'guwar na 'yan gayu ne kuma da turan ci ne 🤔 Gidan su Khadijan ma yana d'aya daka cikin 'ke rarrun gida jen saman dake un'guwar, shiyasa nike son zuwa saboda ina son bene a rayuwa ta

Driver d'in mu yayi  horn adaidai bakin 'katon get din gidan

Mai gadi ne ya le 'ko ta 'karamar 'kofa ganin motar Momy ne yasa shi saurin bud'e get motar mu ta sulala cikin gidan mai gadi ya maida get ya rufe

Daka bisani yazo da gudu ya bud'e wa Momy cikin ladabi yake yi mata sannu  fuskar Momy a sake  ta amsa masa "mun same ka lafiya?". "Lafiya lau hajiya". Mai gadi ya fad'a yana sadda kansa 'kasa "masha Allah babu dai wata matsala ko?". Momy ta kuma tambayar Habu mai gadi, yace "eh Hajiya babu wata matsala komi yana tafiya daidai".

"A kwai kayan mu a bayan mota kashigo mana dasu ciki  kaida Idi". Da "to" suka amsa su duka

A kasalan ce muka fito daka cikin motar muka shiga cikin falo ko waccen mu tasan d'akin ta dan haka muna shiga ko wacce tayi inda tasan nan ne dakin ta yake

A sama d'akin danike sauka yake don haka na haura abina amma dana murd'a hannun 'kofar sai naji a kulle yake gam

'Dakin Khadija dake kallon nawa naje shima a kulle yake sai dai naji motsi da alamar ita tuni tana ciki 'kwan-'kwasa 'kofar na shiga yi, daga can ciki tace "waya?".

"Siddeeqah ce". nabata amsa

Jim kad'an sai gashi ta bud'e 'kofar jikin ta d'aure da tawul da alamar har ta cire kaya wanka zata shiga

"Khadija mukul-lin d'aki na nazo ki bani".

"To" tace ciki ta komo sai gashi ta fito hannun ta rike da mukullin na amsa nayi gaba a bina

"Matar yaya a huce gajiya lafiya". tace min, da gudu na na juyo dan na doke ta amma sai ta maida 'kofar ta rufe tana dariya

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ A bangaren Sadeeq kuwa yana barin d'akin Inna bai zarce ko ina ba sai gidan abokin sa Farooq bai kirasa a waya ba amma yayi sa'a saboda ya same sa ne yana 'kokari fita, nan dai ya bashi hannu suka gaisa Farooq yace "yanayin ka ya nuna kamar kana cikin damuwa, kuma ba ka saba zuwa gida na a irin wannan lokacin ba, kodai kai da mutuniyar taka ce? Saboda nasan labarin gizo baya  wuce na 'ko 'ki, da fita zanyi na gaji da zaman gidan, amma tunda kazo mu shiga ciki ka fad'a min abinda ke tafe da kai".

To bayan sadeeq ya shiga cikin bedroom suka wuce, saboda yanayin tsarin gidan irin me ciki da falo ne sai bayi da kitchen kuma duka haka gidajen kusa dashi suke saboda duka gida ne na yan sanda, wasu ma da matan su a ciki shima Sadeeq da nasa dan yana da Inna shiyasa bai damu da kwanan nan ba, kusan unguwa ce guda aka bar ma 'yan sanda ita, shi yasa da wuya kaji ance wani abu ya faru a cikin ta ko kamar ace anyi fashi ko an sace wani, saboda a zagaye take da masu tsaro kamar barikin sojoji shima Sadeeq saboda ansan shine kuma akwai nasa 'ban garan a ciki shiyasa da yazo ake bude mai get ya shigo abin sa

Kan gado Sadeeq ya fad'a yana maida numfashi, Farooq ya zauna a kan wata kujera dake bedroom d'in yace "ba ba kaifa nike jira kace wani abu mana ka wani baje a kan gado sai kace wata mace".

Tashi Sadeeq d'in yayi ya zauna ya shiga jero ma abokin nasa d'anyen hukuncin da su Daddy suka yanke, Farooq ya san Sadeeq ba zai ta'ba yi masa irin wasan nan ba musamman ma da yasan cewa Sadeeq da Siddi'ka babu jituwa a tsakanin su saboda haka ya gyara zama yace "Alhamdu lillah gaskiya naji dad'in wannan had'in kuma da kace d'an yan aiki wallahi sunyi dai dai, Ko ba komai zaka daina tsangwamar Siddi'ka, kuma sha'kuwa mai 'karfi zata shiga tsakanin ku, saboda haka ka tashi muje a d'aura auren da mu a kwai wata  sabuwar shadda na da nasa aka d'inka min da niyar yau in sata to sai bayan na anso ta daga wurin taila na canza ra'ayi".

Kwanciya Sadeeq d'in ya gyara a kan gadon yace "d'an iska mayen mata to ai sai kaje in yaso d'aurin auren ma sai ayi da kai, amma ni nan daka ganni babu inda zani wallahi, wai ni za'ama aure kamar wani 'karamin yaro, arasa ma wa za a had'a ni da ita sai 'yar 'karamar yarinya wacce ko gama sanin inda yake mata ciwo batayi ba".

Dariya ce ta kama farooq saboda haka yay ta da rawa abin sa saida ya gama ya fara lallashin a bokin nasa akan ya tashi ya shirya suje d'aurin auren, amma Sam Sadeeq yace "bai san da maganar ba". Farooq yana ji yana gani dole ya 'kyale shi amma ba dan ransa yaso ba

 

Wayar sadeeq d'in ce ta hau ringing cikin hanzari ya d'auko wayar daga aljihun sa ganin sunan Hisham yana yawo akan screen d'in yasa shi jan dogon tsaki yace "kagani ko Farooq abinda nake gudu kenan yanzu haka kira na yayi ya cemin ashe nayi aure ko gayyata babu". Kiran ne ya katse, yayi saurin kashe wayar gabaki d'ayan ta wannan dalilin ne yasa da Daddy ya kira wayar Sadeeq d'in yaji ta a kashe

Sadeeq ya ci gaba da cewa "ai ni yanzu na shiga uku Daddy ya gama jamin abun kunya a gari, ni ba mai laifi ba da sai na ringa yawo da abun fuskar da zan sauya kama".

Farooq dariya harda ri'ke ciki yace "wallahi aiki ya ganka yanzu ma aka fara nidai d'an kallo ne, saboda ko na baka shawara ba lallai ne kayi amfani da ita ba amma bari na gwada baka".

Sadeeq yace "wallahi Farooq na tsani yarinyar ne ji nike da ma na mutu na huta da dai nayi rayuwa da ita amatsayin mata ta".

"Kana ruwa aboki na, to kai wai me yarinyar nan tayi maka ne haka da ka tsane ta".

"haba Farooq wai har kana bu'katar 'karin bayani, bayan komai a bayyane yake, kasan nafi san na auri wayay-yiyar mace mai aji da yanga wacce ta gama digiri dinta in so samu ne ma ta fara aiki koda kuwa wani iri ne sannan kuma kada shekarun ta suyi 'kasa da 25 to ko bata da masifar kyau in dai tana da wa'innan abu buwan da na lissafa maka zan aure ta".

Zai ci gaba da magana Farooq ya dakatar dashi ta hanyar fad'in dakata malam "ai na d'auka ka bar wannan banzan tunanin da kasa a ranka zaka ro'ki Allah ne yayi maka za'bi mafi alkairi ashe ba haka bane, to ina so kasan har yanzu Siddi'ka yarinya ce ba a haka zata ci gaba da rayuwa ba ko kana da ya 'kinin cewa baza ta canza ba? Ya fad'a yana kallan Sadeeq d'in".

"Eh Farooq". Sadeeq yace yana d'aga murya "bazata canza ba a haka zata gama rayuwar ta🤔 saboda irin zuciyar uban ta gare ta, kuma bugu da 'kari rashin jin maganar ta yayi yawa, kaf 'kauyen Dande babu wanda bai san ta ba ko ina idan na wuce kallo na ake ana nuna ni kamar anga barawo saboda an san ni yayan ta, nasan ma dan suna jin tsoro na ne da tare ni zasu dunga yi, nafisan yarinya natsats-tsiya mai kunya".

"Hhhmmmm Sadeeq nidai shawara ta anan ita ce kabi komi a hankali kada kayi gag-gawa, amma ni banga laifin Siddeeqah ba rashin jin magana da kace yarinta ce take damun ta, wataran idan akace tayi zata ce ba tayi ba, sharri ake mata".

"Sa'ar Jiddah ce fa mai yisa Jiddah bata yin duk wa'innan abu bu wan da Siddi'ka keyi?".

"To ai Sadeeq kasan yara kowa da kalan 'kuruciyar sa idan ka bibiya a kwai abinda ita Jiddahn ta keyi Siddi'ka kuma koda kud'i akace tayi ba zata yi ba, kuma idan ka lura Siddi'ka goyan kaka ce duk abinda tayi sai ace daidai tayi ba a nuna mata tayi kuskure, amma da ina tabbatar maka da sai tafi Jiddah han kali".

Ta'be baki Sadeeq yayi yace "wallahi ina raga mata ne saboda gwaggo Amina, amma yanzu tunda ta shigo gona ta zan koya mata darasi😢 zan nuna mata tayi babban kuskure da Daddy yace zai aura mata ni bata ce A a ba".

Kafad'ar sa Farooq ya daka sannan yace "Allah ya bawa mai rabo sa'a". Ya fice a d'akin

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾           GARIN ABUJA

Koda na bud'e d'akin na same shi a tsaftace kamar yadda nayi zato saboda duk zuwa haka nike samun shi

Da sallama d'auke abaki na, na shiga sannan na maida 'kofa ta na rufe da d'an mukulli Kan gado na fad'a ina maida numfashi, wash nagaji matu'ka Baccin gajiya ya d'auke ni ba tare da nayi sallar la,asar ba daman sai da muka yi azahar agida muka taho

Hankali na kwance ni keyin bacci na na manta dawani auren yaya sadeeq da yake kaina.

A cikin bacci na nayi  wani mummunan mafarki wanda ban taba yin irin sa ba tun da nike arayuwa ta, ban fahimci me mafarkin ya 'kunsa ba tsabar rud'anin dake cikin sa. A firgice na farka amma nakasa yin salati saboda ban saba ba, ina ta zaro ido na alamar tsoro nakasa firta koda kalma d'aya ina son in tuno abinda nagani acikin mafarkin amma na kasa, sai wani masifaf fan ciwon kai daya saukar min a lokaci daya, sosai tsoro ya shigar min har banason nayi motsi saboda sai naga kamar za a kama ni.

Bugun zuciya ta ne ya 'karu yana bugawa da sauri da sauri sakamakon buga 'kofa ta da naji anayi

Kara du'kun-'kune  kaina nayi a cikin bargo,  daka waje naji ana fadin "Ummi ce ki bud'e".

Jin muryan Ummi da nayi yasa nayi  han zarin saukowa daka kan gadon jiki na 'bari na bud'e mata 'kofar ta shigo, rungume ni tayi  tana ihu Bata lura da yanayin da nike ciki ba turanci ta fara su burbud'a min bayan tasan bawani ji nike ba amma tsabar iya yin Ummi takeyim shi Jin ban rungume ta ba kamar yadda muka saba yasa tasake ni, tana kallo na

tace "sisi kamar bakya hayyacin ki meke damun ki".

"Bacci na tashi". nace mata bansan maye dalilin 'boyewa Ummi gaskiyar abinda yasa yanayi na sauyawa ba

"Haba koda naji". ta fad'a tana kama hannu na, muka fito daga d'aki na, d'akin ta muka shiga wanda ya kasan ce a tsaki yar nawa da na Khadija

"Amma yakamata kiyi wanka sisi kicanza kayan jikin ki, kin ma yi kokari da kika yi bacci dasu a jikin ki ni yaushe zan iya".

"Ai ke ki ka ce Ummi  ni kin san na saba ko a kauye kayan da nasa dasu nike yin bacci duk sabun tar su bana sauyawa izuwa na bacci duk da ina dasu".

Wata uwar 'kara ta saki a razane na kalle ta "la fiyan ki 'ka lau kuwa Ummi?".

"lafiya ta lau sisi naji kin anbaci kauye ne kinsan ni da 'kauye amana don Allah yi ki fito wanka kizo ki bani labarin Dande".

Ban kuma cewa da ita komai ba, na nufi bayin wankan ta masha Allah shine abinda na fad'a bayan na bud'e bayin naga ko mai na cikin bayin fari ne 'kal kamar a zuba abinci a kasan a lashe saboda yadda kasan tayil din ke she'ki ga wani sihir taccen 'kamshi da yake tashi,

A han kali na d'aga 'kafa ta na shiga bayin duk da banyi addu'a ba amma na shiga da 'kafar hagu cikin kwamin wankan na shiga na kunna famfon ruwan zafi da na sanyi na dad'e a cikin ruwan d'umin sannan na fara wanka ina gamawa na d'aura tawul din dana gani rataye.

Ina fitowa ana kiran sallar magriba saboda haka na koma ciki na d'auro alwala na fito

A gefen gado nasamu Ummi  zaune tana buga game a laptop

Saida ta dube ni tace "gaskiya sis kin dad'e sai kace kina  canza fata gashi kuma kina nan yadda kike".

Ban kula ta ba na nufi durowar kayan ta saboda suna yimin dai dai, bayan na bud'e na ga wata doguwar rigar yadi mai laushi me run madara fitet ce ba tada wani kwalliya amma duk da haka d'in kin nada kyau, ban wani damu da saka bra ba nafi sa haf bes, sif d'in haf bes din na bud'e na ciro d'aya sannan na bude na fant na d'auko sabo wanda na gansa da 'yar takar darnan a jiki alamun ba a sa ba, da yake duk nasan inda suke harda na siket din ciki haka na fiddo duk abinda nikeda bu 'kata

Sannan na nufi gaban madubi na zauna kan kujerar dressing mirror na fara shafa mai ina gamawa na d'auki tura rukan ta masu 'kamshi da tsada na fesa a jiki da kaya na duk kuwa da wasu ba akaya ake fesawa ba amma saboda ni ban sani ba haka nai ta fesawa, saboda a lokacin Ummi ta shiga bayi, doguwar rigar na saka na dakko dadduma don rama sallahr da ake bina sannan inyi wacce muke cikin  lokacin ta.

Ina cikin yin sallar Ummi ta fito daman dad dumar na kar kata ta yadda mutane biyu zasu iyayin salla akai

Ko da na idar ban wani tsaya yin addu a ba na cire hijabin

Na sauko kasa na tarar da duka 'yan gidan kowa yana nan harda Aunty Bilkisu da yaranta guda biyu Samahir da Shakran, Khadija da Umar ga Momy sai Jiddah da ke ta faman danna waya ko me take danna wa? oho ahankali na 'karasa saukowa daka kan benan, gurin Momy naje na rungume ta nace "Momy ya gajiyar hanya". Ina mai hawa kan cinyar ta na zauma

Tace "Siddi'ka rigima ni ban san yaushe zaki girma ba saboda wani abun idan kika yi ko Umar auta ba zaiyi ba".

Momy nidai naji saboda bazan ta'ba girma da hawa cinya ba".

"Sarkin san jiki" Aunty Bilkisu ce tafadi hakan

"La Aunty Balki bari inzo mu gaisa".

"Wai bana hana ki cemin Balki ba suna na bil'kees". Ta fad'a tana gyara sunan mu ka  kwashe mata da dariya

Dai dai nan Ummi ta sauko muka dasa firan da ita Samaheer ce kan cinya ta ina yi mata wasa tana 'kyal-'kyala daria

Suwaiba mai aikin gidan ce ta shigo tace "Hajiya na kam mala yana kan dinning".

"to" Momy tace sannan ta kallo mu

"Oya kutashi muje muci abinci dan nasan kowa anan yana jin yunwa".

Kamar jira muke duk muka mi'ke muka nufi dinning kowa ya zauna muna ci muna d'an ta'ba fira taliya ce sai faten dankin turawa da yaji hanta sai farfesun naman kaza mai yaji, babu laifi Suwaiba ta iya girki dan idan Daddy baya nan ita take yin duk wani abu da za aci ko a sha, sa'banin idan yana gida Momy ke girkawa mu taya ta.

bayan mun gama cin abinci muka dawo falo muka 'kara dasa sabuwar fira har aka kira sallar isha'i duk da Jiddih tunda na sauko magana bai had'ani da ita ba saboda ita tanada jin kai ga san nuna ita wata ce, ni kuwa ba zan d'auki iskanci ba dama ba shiri nike da ita ba saboda abu kad'an ke had'a mu mu fara dambe kowa bai san raini

NI DA YAYA SADEEQ                    *بسم الله الرحمن الرحيم*

Chapter 11

____Bayan mun idar da Sallar isha'i wata firar muka cigaba da yi, idan Khadija tayi nata nima sai nayi nawa hakama Umar, yayin da Jiddah ke faman cika tana batsewa tana jan dogon tsaki, ko ita da wa oho,

yanzu haka Umar ne ke bamu labarin wani Almajiri daya shiga bara gidan wata amarya sai mijin ta yace "almajiri kawo kwanon ka". Sai amarya ta leko ta amsa kwano, ta zuba masa abincin, Koda ta miko mai kwano sai ya amsa yatafi zauran gidan yana kuka, sai mijin amaryar yabiyo almajirin, ya tambaye sa meye dalilin kukan nasa "ko abincin ne ba zai isheshi ba?". Sai almajiri ya girgiza kai, sai mijin amaryar yace "to maye kake ma kuka?". Budar bakin Almajiri sai yace "shi ba komai ya sashi wannan kukan ba illah yana tsoran agama aure kyawa wan mata kafin lokacin su yai_

" Idan ke/kaine ya zaki/ka yi", haka ya jefe musu tambaya aikuwa nan sukaita tafka muhawara suna shirme

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Sadeeq kwan ce a kan gadon farook yana cikin Instagram sai kallon hotuna yake, kwatsam idanuwan sa suka sauka akan hotan wata yarinya, acikin zuciyar sa yace "daga ganin ta tanada aji kuma ba zaka ce mata 'karamar yarinya ba domin zata iya kaiwa 25 years old da haihuwa". Kara shiga account dinta yayi nan take hotunan ta da take dorawa suka bayyana sosoi Sadeeq ke kallon hotunan, sunan account din ta ya kalla yaga anyi rubuta kamar haka *Zuby officially*

"Wow" ya fada afili Suna mai dadi Zuby haka yaita maimaita wa bata da wani kyau a fuska kuma bawani haske gareta ba amma dagani ta 'kara daman da yake sa hasken fata, 'kirjin ta cike yake da dukiyar Fulani tana da dirin jiki

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Abuja Ba muyi wata dinner ba kasan cewar bamu dade da cin abincin ba shayi Momy tasa Suwaiba ta hado mana yaji ni'inal da kayan kamshi, mukai ta kurba kamar wasu larabawa 😂 Bayan mun gama kowa ya watse amma nikam sarkin tsoro d'akin Ummi nayi tana 'ko'karin rufe kofar nai saurin turawa Da mamaki tace min "sisi yadai?". "Anan zan kwana" na fad'a yayin da nike shigowa ciki, ta maida kofar ta rufe

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Ahaka rayuwa ta cigaba a gidan Momy, tsakanina da Jiddah babu jituwa zan iya cewa tun nazo gidan magana bai shiga tsakanin mu ba, kuma babu Wanda ya lura a gidan saboda tun asali kowa yasan bama wani shiri, Yau kimanin kwana bakwai kenan da aurena da Sadeeq amma har yau ban sashi a cikin ido naba gashi su Khadija har sun koma makaranta

Muna falo nida Momy a zaune sai Suwaiba dake faman zirga zirga ta kai ta komo tana kokarin hada abincin rana kafin su Khadija su dawo, "dauko min waya ta a bedroom dina" cikin sauri na mike domin Momy batasan simi simi Bayan na dawo nace "Momy gashi nasamu wayan ma tana ringing". "Kawo mugani waye ya kirani" ta amsa tana shafa screen d'in wayar sannan ta kara a kunne "Wa'Alaikumussalam". shi ne abinda naji Momy tace kafin tace "lafiya lau". Ta kara da cewa "wallahi Sadeeq zan cimaka mutunci fiye da yadda kake zato kasan dai yanzu ba kamar da bane kanada nauyi a kanka amma kayi burus da mu dama gwada ka nayi naga hankalin ka, to maza maza kazo gobe inason magana da kai na fada maka idan kuwa ba haka ba zanyi mummunan saba maka".

Cikin fushi Momy tace "bazan saurare ka ba Sadeeq baka da abinda zaka fada min na yadda, kaima kasani domin bakada wani uzuri kayi abinda nace maka kawai".

Tana gama fadar haka ta kashe wayar

Jim kad'an saiga wani kiran ya sake shigowa daga yadda naga Momy ta daga wayar na gane yaya Mubarak ne d'an yayan ta, na sanshi sosai ya nada mutunci da yana nan ne da zama amma yanzu yatafi India saboda ya karasa karatun sa a can, kallo na tayi kana tace "bani ruwa mana mara sanyi nasha". "To" nace na mike cikin natsuwa koda na dawo har ta kammala wayan

NI DA YAYA SADEEQ                      *بسم الله الرحمن الرحيم* Chapter 12 ____Washe gari da misalin 'karfe 11am na rana a lokacin Su Khadija suna makaranta, Momy ma ta fita ma'kota gidan wata 'kawarta Hajiya Nafisa, amma tace ba zata dad'e ba, zaune nike ni kad'ai a falo kan kujera ina kallon TV Ya Sadeeq ne ya shigo bakin sa d'auke da sallama koda yaga ni ce zaune a falon sai ya gimtse bai 'karasa sallamar ba ya d'aure fuska kamar bai ta'ba dariya ba, ni ma nayi kamar ban ganshi ba, tsawa ya daka min "dan ubanki baki iya gaisuwa bane ko nan d'in gidan uban ki ne? Ko da yike shima ubanki' tarbiyar bata ishe sa ba bare kuma kema ya baki".

Inajin zafin gorin da Sadeeq yake mini har cikin raina a lokuta da dama

ya cigaba da cewa "idan ba mummunar 'kaddara ba mai zanyi dake kucaka ki kalle ki, ki kalle ni, kin tafka babban kuskure da kika yarda Daddy ya hada auren nan zan shayar dake madarar azaba gida na zai zame miki tamkar kabari ke koda sunana ki kaji an ambata sai gaban ki yayi mummunan faduwa, saboda bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane, ki fara tunanin yadda zaki rubuta littafi mai suna *NIDA YAYA SADEEQ* saboda irin zaman da zakiyi a cikin gida na ya isa ki rubuta".

Duka wannan maganar da Sadeeq yayi kaina a 'katsa wasu hawaye masu zafi suna gan garo mini, narasa mai nayi wa Sadeeq da har ya tsane ni haka? Ban ta'ba tunanin tsanar da yake ce wa yayi mini ta kai har haka ba, Ban tanka masa ba illa mi'kewa da nayi na nufi hanyar sama na fara taka steps kenan ya da katar dani ta hanyar fadin "na tsane ki Siddi'ka na tsane ki, kuma bazan taba sonki ba a duk sanda ki kaji nace ina sonki to kada ki ta'ba yadda dani saboda yaudarar ki zanyi ba gaskiya bane". 😭

Hawaye masu 'kuna suka cigaba da gangaro min a haka na 'karasa haura steps din, Suwaiba da ke faman dafa abinci a kitchen taji duk abinda ya faru tsakani na da Sadeeq

'Dakina na shiga na fad'a kan gado, hawaye mai zafi yana zuba daga ido na, ni da kaina ina jin tausayin kaina saboda a sani na da yaya Sadeeq bai ta'ba cewa zaiyi baiyi ba duk abinda yace zaiyi to sai ya aikata sa.

A cikin kukan na d'aga hannaye na sama na ce "ya Allah ka bayyana mahaifiya ta a duk inda take a fadin duniyar nan, ya Allah kasa tana a raye saboda inaso na rayuwa tare da ita, ya Allah kada kabama wani bawan ka sa'ar cutar da ita". Mama. Na fad'a haka yayin da na d'aga kaina sama ina kalla, "bansan maye dalilin ki na cewa ko bayan babu ranki a daura wa 'yarki aure da Sadeeq ba, nayi alkawarin ni Siddi'ka zan zauna da Sadeeq koda kuwa hakan na nufin zai zama ajali na ha'k'kin ki ne nayi miki biyayya a sanda kike a raye da kuma sanda rai yai halin sa, tabbas zan bi duk wani umarnin da kika bani, Mama ta ina sonki". Na 'kare maganar da wani irin kuka mai tsuma zuciya

Allah sarki Siddi'ka ni kaina ta bani tausayi ban san sanda na saki waya ta tafad'i a kasa ba saboda ido na ya cika da hawayen 😭 tausayin halin da take ciki da 'kyar na samu na daidai ta kaina na d'auki waya ta na fita daga d'akin naja kofar na rufe

Momy ce zaune ita da Sadeeq a falon 'kasa, sai zazzaga masifa takeyi "Sadeeq kabi duniya a hankali ko ta d'aga ka zata aje ka, Wallahi Sadeeq ina guje maka ranar da zakayi ladama amma kuma ladamar zata kasan ce da ita gwamma babu saboda ka makaro, ka kasa d'aukar kaddarar ka a yadda tazo maka".

Shi dai Sadeeq jin Momy kawai ya keyi amma baiga wata ranar ladamar da zata zo mai ba kuma ma ladamar ba akan kowa ba sai akan Siddi'ka yaji takaicin kalaman Momy, saboda har cikin ransa ya ke jin kiyayyar Siddi'ka

tace "dama akan maganar makarantar Siddi'ka ne yasa nace kazo tunda kai ba kayi hankalin haka ba, kasan dai an koma hutu, so nike ka kaita makarantar su Khadija saboda akwai koyarwa sosai kuma kaga tana da saurin d'aukar abu bazata sha wuya ba".

Yana sosa 'keyar sa yace "Momy gaskiya ni boarding school zan kaita acan katsina nama gama komai yanzu haka ranar lahadi zan kaita".

Momy bataji dad'in abinda Sadeeq ya aikata ba tare da ya nemi shawar ta kona Daddy ba, saboda haka tayi mai fad'a sosai kuma tace "bata yadda ya kai Siddi'ka boarding ba".

da yake Sadeeq ya iya dad'in baki kamar d'an siya sa yasan kalaman da zai fad'a ayi saurin yarda dashi, nan take ya siye Momy da da-d'a-d'an kalamai har ta amince masa

A zahiri Sadeeq 'karya ya keyi saboda bai yi mata register ba dama yana da burin yin hakan saboda bai son ya kaita jeka kadawo yasan su Momy zasu takura masa amma boarding sai idan anyi hutu tazo, ko babu komai zai samu sau'kin abun Bugu da kari yana san ya shigo da batun auren sa da Zuby nan bada jimawa ba, saboda a halin yanzu soyayya mai 'karfi ta shiga tsakanin su sun aminta da junan su har sunyi alkawarin aure duk da basu taba ganin juba ba yau Sadeeq zaije ganin ta saboda itama anan garin Abujan take, saboda hud'uwar da zaiyi da masoyiyar sa ne 'karfin zuwan nasa Abujan domin yana matukar 'kaunar Zuby kuma yana da muradin ganin ta.

Momy ce ta katse shurun da cewa "kuma aji nawa za a sata?". "Momy yadan ganta da yadda suka gwada ta kinsan yarinyar kwata kwata ba tada 'kwa-'kwalwa yanda kika san dusa haka kanta yake Allah dai yasa ko JS1 ne su d'auke ta".

"Js1 fa kace Sadeeq! Ina laifin 2 idan 3 bai samu ba, to ban lamun ce ba banyarda ba kayi duk yadda za kayi ta gama prmry School fa, kai kan ka shaida ne akan makaranta da ta gama, kuma kada na 'kara jin kace bata da 'kwa-'kwalwa zan sa'ba maka".

"Uhm" dai Sadeeq yace wa momy

Daga haka ya mi'ke "Momy ni zan fita a kwai wani aiki da zanyi zuwa anjima zan dawo zan kwana biyu anan kafin na koma ".

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ 𝑫𝒂 𝒃𝒂𝒛𝒂𝒓 𝒌𝒖 𝒏𝒊𝒌𝒆 𝒓𝒂𝒘𝒂 𝒎𝒐𝒔𝒐𝒚𝒂 𝒏𝒂💃 𝒊 𝒍𝒐𝒗𝒆 𝒚𝒐𝒖 𝒂𝒍𝒍

                 Addua   

_Ya Allah ina rokonka da dukkan kyawawan sunayen ka ka kiyaye duk wani musulmi daka shiga mawuyacin hali kabamu lfy me amfani kasanya mana haquri da juria ya Allah ka kwantar mana da hankulanmu ya Allah kada kabamu ikon butulcemaka koda ka jarabcemu 🙏_

NI DA YAYA SADEEQ

٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·

Chapter 13

_____A gaggau ce yayi faking motar sa ya fito ya shiga cikin gidan yayi sa'a babu kowa a falon sai TV da aka bar sa a kunne yana 'kira'ar alQur'ani mai girma, darect sama ya haura bai zarce ko ina ba sai d'akin sa, yana shiga ya aje wayo yinsa ya cire a gogan hannun sa sannan ya fad'a bayi bai wani d'auki lokaci ba ya fito d'aure da towel a 'kugun sa da wani a hannun sa yana tsane ruwan jikin sa gaban madubi ya zauna mayuka ne kala kala da tura ruka masu 'kamshi da tsada ya shafa wannan ya mutstsuka wancen saida yabi yagama shafa ko wanne. Sannan ya fesa body spray mai sanyin 'kamshi wata dakakkiyar shadda fara ya d'auko wanda aka 'kawata ta da ado da dinkin zamani hular zanna bukar ya ciro ya a je a gefe sannan ya d'auko agogon hannu da safa da ba'kin takalmi mai sheki, a tsana ke ya shirya abin sa tsaf sannan ya d'auki wayo yin shi ya fito. Da sauri sauri yake sauka akan step d'in tun kan ya 'karasa saukar yake jin hayaniyar su Momy bai so haka ba, saboda yanzu saita tsare shi da tambayar ina zashi "Momy". Sadeeq ya fad'a alokacin da ya 'kara so cikin falon gaba d'aya yaran gidan sun sha jinin jikin su saboda basu san ya zo ba Siddi'ka kuwa batayi mamakin ganin sa ba, bakin ko waccen su na rawa suka fara gai dasa ya amsa fuska ba yabo babu fallasa "yaushe kadawo gidan sadeeq? Kuma ina zaka haka kaci wannan kwalliyar sai kace sabon ango". Yana sosa 'keya yace "wallahi Momy ban jima da shigowa ba bikin wani aboki na zani anyi daurin auren jiya yau ake dinner shine nike ta sauri kada nayi latti". "A dawo lafiya".

Tun a hanyar sa ya kira gimbiyar ya shaida mata ya taho 'kara kwatan ta mishi unguwar tayi, da misalin 'karfe 8:17 ya isa cikin unguwar daganin ta ma'aikatane a cikin ta saboda gidajen kusan duk iri d'aya ne kamar quarters haka unguwar take

Bayan yayi faking a gefen wani gida, ya d'auko wayar sa da ke ajiye a gefen sa yad'an shafa screen d'in sai ga number tafito da suna Baby a jiki call ya danna sai da ta fara ringing sannan ya kara a kunne

Ringing biyu ta d'auka ajiyar zuciya ya sauke yace "Baby na" daga can 'bangaren cikin shagwaba tace "my heart kazo ne?".

Ce wa yayi "akasi aka samu Baby na bayan na gama waya dake sai ga kira da ga office din mu wai ana son gani na to babu yadda na iya kin san aikin gwaumnati shine na juya a kalar tafiyar yanzu haka ina hanya ban isa ba ha'kuri na kira na baki".

Zuby da ta gama shiryawa, zuwan Sadeeq d'in kawai take jira, batasan sanda kwalla ta fara zubo mata ba cikin shagwa'ba take fad'in "amma my kasan dai bazan ji dad'i ba wallahi har Abbah na sanar masa kuma yana gida inason ka gaisa da shi ga Mamq da tun sanda ka shaida min zaka zo na fad'a mata tasa aka shirya maka abinci yanzu mai kake so na ce musu?". ta kara sa maganar tana fashe wa da kukun shagwa'ba

Tun Sadeeq yana dariya ciki ciki har saida ta fito fili saboda yadda Zuby ke shagwaba gunin ban dariya ga kuma kasala da ya rasa ta maye ta saukar masa duk a lokaci daya

"Haba my wai dariya nabaka?". Niyar fashewa da wani kukan take yi, yayi saurin cewa "gani a 'kofar gidan ku kisa mai gadi ya bud'emin get, ko ba shine mai ba'kin get ba?". Shuru tayi saboda bata yadda da abinda yace ba Jin shurun yayi yawa Sadeeq yace "ko in koma ne?". "Wai da gaske My kana 'kofar gidan mu?". "Na ta'ba yi miki 'karya ne?".

"A a". Ta bashi amsa

"to kisa abud'e min get".

Ihu ta saka 'kamar 'karamar yarinya ta cilla wayar kan gado

SADEEQ da kallo yabi screen din wayar yana mamakin Zuby d'in wani lokaci idan tayi abu saita koma kamar Baby amma duk da haka tana matu'kar burge sa saboda son ta a kullum 'kara dad'uwa yake yi acikin zuciyar sa A yanzu haka yanajin idan ba ita bazai iya rayuwa da wata 'ya mace a matsayin matar sa ba.

Mai gadi ne ya wangale get d'in Sadeeq ya sulala da motar sa ciki kana ya nemi guri yayi faking

Bai fito daka cikin motar ba wayar sa ta hau 'kara a kasalan ce ya d'auka ya kara a kunne Daga d'ayan 'bangaren tace "My ga Rahmatu nan yar aki zata kaika falon baki".

"Banga kowa ba ni".

"to baby ka fito daga cikin motar mana zaka ganta". Ta fad'a tana 'kara gyara tsayiwar ta a jikin balakona saboda tun sanda Sadeeq ya shigo Zuby ke le'ken sa har kawo yanzu da take waya da shi tsaye take ko motsin kirki bata yi sai Murmushi da take yi zuwa zuwa mai wuyan fassaruwa

Daya bud'e murfin motar saida ya d'auki 10 seconds sannan ya fito da 'kafar sa guda bayan wasu seconds din ya fito da d'ayar Zuby dake la'be a balakona mamakin jan ajin Sadeeq tayi, saboda ko ita da take mace bata da kalan sa.

"Wow" shine abinda Zuby ta fad'a a lokacin da taga Sadeeq ya fito, "gaskiya gayannan 'karshan had'uwa ne kamar shi yayi kanshi Sadeeq ka riga ka shigo hannu bazan taba bari ka kubuce min ba, ban taba jin ina son nayi aure ba sai akan ka zanyi iya bakin kokari na wajen jan hankalin ka kuma zan kiyaye duk abin da zai sa ka gane wace ce Zuby bazan bari wata kawa ta ta sanka yanzu ba, gaskiya saboda gudun matsala inason asa bikin mu kusa saboda kada yan gulma su yimin cikas". Zuby ce ta fadi haka bayan ta gama 'karewa Sadeeq kallo

gaskiya Sadeeq namiji ne irin mazajen da suke da wahalar samu a wannan zamanin saboda ya had'a duk wani abu da ake san namiji ya mallaka Allah ya bashi yana da tsayi na misali ga kyau da hasken fata ga kudi da ilimi hankali ya iya daukan wanka ya iya soyayya mai daukan hankali duk shigar da yayi sai ta yi masa kyau shiba siriri ba shiba dan lukuti ba gaskiya masha Allah gayan ya hadu ajin karshe ne🥰

Wata matashiyar mace da bazata haura 35 years aduniya ba, ta 'kara so gurin sa cikin girmama sa tace "ranka shidade nice Zuby tace na kaika falon baki".

Sadeeq da wani lokaci magana take masa wuya bai amsa mata ba sai nuni da yayi mata alamar babu damuwa ta kaisa, tana gaba yana bin ta a baya har suka isa cikin wani madai-daicin falon da yake d'auke da manyan kujeru masu ruwan orange da baki sai chanis kafet da aka shimfid'a a tsakiyar falon shima ba'ki ne da d'ishi d'ishin orange a jikin sa sai 'katon TV da ya mamaye jikin bangon falon a gefe guda a kwai 'yan 'kananun tebura zagaye da babba a tsakiyar su, gaskiya d'akin ya had'u wani abun ma bazai fad'u ba

bayan Sadeeq ya shiga ya nemi kujera ya zauna a kan 1cter jim kad'an sai ga ramatu ta shigo hannun ta rike da katon tirai da aka jera kulolin abinci masu kyau da ban sha'awa a kan babban teburin ta jera kulolin sannan ta fita ta kuma dawo wa da wani 'katon turai din mai dauke da fruit, da kunin aya da zobo ta kuma jerawa ta fice Can sai ga ta ta kuma dawo wa da jok din ruwa a tirai da kofuna biyu bayan ta ajiye ta dauki kofi daya ta zuba mai Ruwan sannan ta saka wani farin abu a ciki kamar 'kankara nan take ruwan ya fara canza color, daga fari ya koma ja haka dai yai tayi sannan ta mi'ka masa Amma sai yaki amsa da taga bashi da niyar amsa sai ta ajiye ta fice acikin ranta take cewa "ko ina Zuby ta samo wannan kyakkyawan saurayin tunda Zuby ke kawo samarin ta bata taba kawo mai kyau da hankali da nutsuwar wannan ba". Abinda ya daure wa ramatu kai yadda Sadeeq din yayi shigar kamala yana kama da mutanen kirki a fuska to mai yakawo sa gurin Zuby, saboda Mama ta san duk wani abu da Zuby ke aikata wa wani lokacin ma ita ke bata karfin gwuiwa sabanin Abban ta da bai san komi ba

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Gaba daya mutanen gidan zaune suke a falon sama amma kowa da abinda yake yi saboda Umar littafi ne a gaban sa yana homework yayin da khadija da Siddeeqah suke fira Momy kuwa laptop ce gaban ta tana danna wa sai Jiddah dake faman danna waya tana cika tana batsewa Ummi kuma Session flm take kalla sun dauki tsawan lokaci a haka

Bayan Momy ta gama abinda ta keyi ne ta dube ni "Siddee'ka". saida naji 'ya 'yan hanjin cikina sun kad'a saboda fargabar abinda zata cemin da hanzari na dago kaina muka hada ido nace "na'am Momy". "dazun da rana nayi magana da Sadeeq akan maganar makarantar ki". Yace "ya samami ki admission a makarantar kwana har ya gama komai ranar lahadi zai zo ya dauke ki ya kai ki

Ba Siddeeqah kadai ba har su Khadija sai da suka dago kai suka kalli Momyn domin su dad'a tabbatarwa basu ga alamar wasa afuskan ta ba duk da Momyn daman ba mai irin wasa da yarannan bace amma kuma tana jansu a jiki ta yadda duk wani abun da yashige musu duhu suke zuwa neman shawara gurin ta. "Momy makaranta kwana fa ki kace". Siddeeqah ta fada murayan ta a sanyaye

"Eh". Siddeeqah wallahi makaran tar kwana Sadeeq ya nemo miki naso na hana amma sai yace "ya kashe kudade masu yawan gaske saboda sunan wata a ka cire aka sa naki". Sannan yace "acan sai kin fi dagewa kiyi karatu idan kina gida wasa ba zai barki ba".

"Momy Daddy fa shima ya yarda ko bai sani ba?". Khadija ta tambayi Momy

Sai a lokacin Momy ta tuna ba tayi waya da Daddyn ba dan sanda ta kira sa ta nason suyi maganar yace "mata suna meting idan sun gama zai kira ta".

"A a" Momy tace "zuwa anjima idan ya kira ni za muyi maganar".

"Momy mai yasa yah Sadeeq zai mini haka gaskiya ni Momy ba zani ba gwara in koma 'kyauye gurin Inna ta na hakura da karatun bazan wani yi kuku da ku ba".

"Taso kizo kusa dani 'yata". Jiki na babu laka na tashi na koma kusa da ita na zauna na tsaida idanuwa na akan fuskar ta, hannun ta ta daura a kan kafad'a ta cikin lallashi tace "Siddeeqah ha'kuri zaki yi saboda ilimi gishirin rayuwa ne idan Sadeeq yayi haka ne don ya kunta ta miki to insha Allah aniyarsa ce zata bisa saboda ke gaba ta kai ki. Ki kwantar da hankalin ki babu abinda zai same ki sai alkairi".

"Momy kuma wace makarantar?". Ummi tayi tambayar "Katsina" yace "zai kaita wai akwai kanwar Farooq a can" yace "makarantar tana da koyar wa sosai kuma suna da kula da dalibai".

Jikin Siddeeqah yayi mutakar sanyi duk da bata taba jin labarin makarantar kwana ba amma dai batason tayi nisa da gida ita da take so duk bayan 2 weeks tana zuwa Dande ganin Inna Gashi yanzu za a kaita wani garin ba garin da take ba

Da kyar Momy ta sha kanta ta amince ba dan ranta ya so ba sai dan ganin girman Momy da take yi, Momy ta cigaba da bata baki da kal momi masu dadi da sanya ya rai har ta amince

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Zuby ce zaune a kan kujerar dake kallon ta sa, kura mata ido yayi ko kiftawa ba ya yi.

Cikin shagwaba tace "muni na kake kallo ko banyi maka ba ko?".

"ko daya ina kallon irin baiwar da Allah yayi miki ne Kin kuwa san wani abu?".

"A a". Tace mai

"Ban taba ganin mace mai kyau irin kiba, gashi tun da nike a rayuwa ta ban taba haduwa da wacce na ke so har naji ina mura din auren ta ba sai ke, gaskiya ki kara godewa Allah bai rage ki ta ko ina ba a lokacin da naga kina tafiya sai kikai mini kama da wahainiya hatta muryan ki abar so da kauna ce idan kina magana kamar ana busa sarewa, ga...".

"Ya isa haka my kada kasa na kasa bacci yau amma ka zuga ni da yawa har kasa naji kaina yayi kato".

Duk kuwa da ba karamin dadin kalaman shi taji ba wani d'a na miji bai taba yaban ta haka ba duk kuwa da ita mutum ce mai san a dunga kuranta mata ana zuga ta shiyasa tace "Sadeeq dina na musamman ne".

"Ai kin wuce haka Baby na saboda kedin zara ce".

Cikin zolaya tace "Allah My kafi kyau a fili ka daina wahalar daukan picture's saboda yana rage maka kyau".

"Bawani nan kodai ban miki bane?".

Zaro ido tayi waje gami da dafa kirji tace "wane mutum inji mutuwa".

"amma kinsan labarin zuciya atambayi fuska ko?".

"fadamin nason daman dan sanda akwai ku da karantar yanayin mutum".

Zai yi magana kenan wayarsa ta hau ruri DCP Kamal yagani yana yawo a kan screen d'in cikin girmamawa ya kara wayar a kunne bayan ya daga ya gaida ogan na su. Ko mai yace masa daga can ban garen oho, Shi dai Sadeeq din yace "okay angama ranka shidade okay okay ahaka dai suka karasa wayar

Ya a je yana kallon Zuby da ta kura masa ido ko kiftawa ba tayi.

"Ya dai" yace mata yayin da yahura mata iskar bakin sa, sai a lokacin taga rashin dacewar hakan kunya ta kamata tayi sauri ta sadda kan ta kasa tace "kamar ana neman ka A gurin akin ka ko?".

Gira yadaga mata alamar "eh" "to bari na kira Mama ku gaisa sai na kaika gurin Abba daga nan saika wuce".

Bata jira amsar sa ba ta wuce bata wani dauki lokaci ba ta dawo tare da wata dattijuwar chocolate din mata ita ba doguwa ba ita ba Gajere ba tsaka tsakiyar.

Cikin mutunci Sadeeq ya russuna ya gaishe ta ta amsa mai cikin kula da jin dadi Sannan sukayi sallama ta wuce

"gaskiya Mama nada kirki". Sadeeq yace wa Zuby

"Allah da gaske?".

"Ehman ashe ita kika biyo".

Zuby dan dadi har rufe fuska take yi wai yau ita ake yaba haka 💃

"muje na kaika bangaren Abba ku gai sa". "Muje to" ya fada yana mike wa tsaye

Ta wata kofar suka bi sai gasu a cikin wani madai-daicin falon da babu tarkace a cikin sa da wani datti jo zaune a kan kujera hannun sa da jarida yana karantawa fuskar sa sanye da siririn glass bayan sunyi sallama suka karasa ciki a kan kafet Sadeeq ya zauna ha gaida sirikin nasa Abban Zuby yaji dadi sosai da yaga sadeeq ne zai auri tilon gudan jinin sa bayan sun gaisa suka dan taba fira Zuby kuwa bakin ta ya ki rufawa farin cikin ta ya bayyana a fili, basu dade ba Sadeeq ya yi masa sallama.

babu laifi Abban Zuby yana da haske fata wata kila agurin sa Zuby ta dauko hasken fatar

Har bakin motar sa Zuby ta rakosa tana yi masa shagwaba kala kala da kyar ya samu ya lallashi ta ta barshi ya tafi

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ "Ku tashi kowa yaje ya kwanta dare yayi sai kuma idan Allah ya kaimu gobe" Momy ce ta fadi haka yayin da take kallon 'ya 'yan ta "to" duk suka ce masu tarkace suka dauka Ummar da dakin sa yake a kasa ya shige haka Jidda ma nata a kasa yake itama ta ce "Momy good night" tuni mu uku muka dun guma zamu haura sama amma sai Momy ta kwala min kira "Siddeeqah na manta zo ki dauki abincin yayan ku ki kai masa ban garan sa tunda saman zaku haura gab yake da shigowa

*Ash wash kash*😂 _Na gaji hhhmmmm idan ban ga ruwan comments ba za a dade banyi typing ba_ 😂

*Kada ku manta* _Comment kyauta ne haka ma share da vote_😂

Taku har kullum _Sbeeuty✍️

NI DA YAYA SADEEQ                    بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 14

_____"To". Nace wa Momy na nufi hanyar kitchen bayan na shiga na d'auko kular abinci da zobon da Momy ta hada mai akan wani madai dai cin tirai na d'oro su sanda na fito babu kowa a falon har Momy ta wuce d'akin ta saboda haka nima na haura sama sai da na fara zuwa daki na na sauya kaya na, saboda izuwa yanzu nima na fara sabawa da kayan baccin idan ba dasu ba bana jin dadin baccin saboda haka na sauya izuwa wata farar doguwar riga mai kauri ta bacci akwai wata yar baza mai kamar leshi a gaban ta ina sau yawa na nufi bangaren ya Sadeeq da yake dan nesa da mu saboda saikin bi ta wata kofa sannan zai sada ki da bangyaran sa dake dauke da falo da d'akuna 2 sai bayi da kitchen, nayi sa'a saboda kofar shiga a bude take ina murmushi na karasa ciki saida na gama karewa falon kallo sannan naja dogon tsaki ina ta'ba baki na ce "shi ko kunya baya ji daki sai kace na mace". A bude na bar kofar sannan na wuce bedroom din sa da shiga ta naga gado a gyare luf luf dashi ya lailaye zanin gadon sa ji nayi ina sha'awar hawa gadan saboda haka na ajiye kular abincin a kan wani teburi nayi sufa kan gadon😜 ina 'yan tsalle tsalle na ina dariya ni kadai

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾

Tafe yake a kan hanya tunani ne fal a cikin zuciyar sa ya sa'ka wannan ya warware wancen duk da tuki yake yi amma yayi zurfi a cikin tunanin sa ta yadda bai san mai yakeyi ba Allah ne ya tsare sa da kuma kasan cewar ba akan babban titi yake ba ringing din wayar sa ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya lula firgigit Sadeeq yayi saida ya dafa kansa "ya Salam ni Sadeeq mai ke damu na haka wani irin tunani ne kuma akan me nike yin sa mtssss" .yaja dogon tsaki ba shida amsar tambayar sa saboda haka ya lalubi wayar sa da yaji tana ringing bai wani tsaya ya kalli sunan wanda ke neman sa ba yana dauka ya kara a kunne. Daga d'ayan bangar akace "wallahi aboki baka da mutunci daka zuwa Abuja ganin Princess sai ka manta damu, munafuki amma da anyi magana kace baka son yarinya ka tsane ta".

"shege akace maka kowa mayen mata ne irin ka ka rasa dawa zaka hada ni sai da yar karamar yarinya wacce ko...".

"haba malam kada kacika min baki daga karshe kazo ka fada tarkon karamar yarin ya".

"Wa ni?!". Ya fada yana nuna kan sa da yatsan sa Kamar Farooq din yana ganin sa "Allah ya kyauta ai na fada mata duk sanda taji nace ina son ta kada ta taba yadda dani saboda ba da gaske bane".

Farooq baiji dadin yadda abokin sa yayi su'bul da baka ba saboda haka yace "uhm Sadeeq idan Allah ya tashi kama ka bazai maka kadan ba kuma gaskiya bazan ji tausayin ka ba koda zanji sai ka ji jiki, saboda duk abinda ka Shuka shi zaka girba dama na kira ne naji ya kake ya Momy tunda duk kuna lafiya sai da safe".

"Kaga Farooq kada ka kashe a kwai maganar da nike so muyi".

"Ina jin ka to"

"yanzu haka fa a hanya nike naje naga gimbiya ta, gaskiya babyn ta hadu tafi kyau a fili nike fad'a maka komai yaji zam-zam hhhmm nasan ba lallai ka yarda ba tunda kaki ko hotan ta ka gani amma tun na ganta na shiga wani yanayi".

"Haba Sadeeq daman wannan ce maganar da kace za muyi?.

"Eh amma da akwai d'ayar nafi zumud'in wannan shiyasa na fara fada maka ita" kuma kasan nace "Momy ce take nema na ashe akan makarantar yarinyar nan ne to shine nike so ka nema mata admission a makarantar da Sadiya take saboda na cewa Momy na gama komai tafiya ta rage".

Shuru Farooq yayi na wasu yan da'ki'ku alamar nazari can ya numfasa yace "haba Sadeeq wai meke damun ka meyisa kake son ka kuntatawa yarinyar mutane wani irin makarantar kwana ana zaune 'kalau don Allah kajanye wannan maganar kaji tausayin ta Har yanzu fa Siddeeqah yarinya ce karama na tabbatar ma batasan maye aure ba da tasani wallahi da...". Bai karasa maganar ba Sadeeq ya dakatar dashi da cewa "malam don Allah ba shawara na tambaye ka ba Dan kaga na biyo ta hanyar ka shine zaka tozartani idan baza kaimin ba kawai ka fadamin"

"Allah ya huci zuciyar ka". Farooq ya fada kana yace "aji nawa za a sata?".

"Ko js1 ne asata ba matsala ta bace zan fi son haka saboda na more soyayya ta da Baby na kan tagama karatun"

Farooq nason yace wani abu amma gudun kar yakara laifi yace "babu damuwa zanyi kokari insha Allah ko js2 su kaita".

Daga haka sukayi sallama

Bayan Sadeeq ya gama faking din motar sa ya fito jinsa yake wani iri saboda haka ya haura sama bai kai ga shiga dakin ba yaga kofar abude yayi mamaki bai gama tsinkewa ba sai da ya shiga bedroom din sa ran sa a mugun bace ya karasa kan gadon da niyar fusgo ta amma sai yaji kamar an soka masa kibiya a cikin sa bai san sanda ya zube a kan gadon ba numfashin sa nafita da sauri da sauri Siddeeqah garin juyi ta wurga wa Sadeeq kafa ransa bace ya wurga mata harara, tuna aikin banza yayi tunda bacci take yi ya shiga kwala mata kira "ke ke uban wa ya ce ki shigo nan?"

Siddeeqah da kamar a mafarki taji ana kiran ta a firgice ta bude idanuwan ta suka sauka akan na Sadeeq dake mata kallon tuhuma fuskar sa a murtuke babu alamar wasa yace "dan uban ki uban wa yace ki shigo min daki?".

Siddeeqah gaba daya ta rike ce bakin ta na rawa take fadin "lah yah...!".

"Yayan uban ki zakiyi bayani wallahi bazaki sauka ba sai na yi ball da ke".

'Kokarin tashi yake amma cikin sa ya kara murde sa nan take ya rike cikin yana kiran sunan Allah a rude Siddeeqah ta 'karasa gurin sa ta kama hannun sa "yaya yaya meke damun ka haka me yasameka?".

A wahalce Sadeeq yace "cikina". Kama hannun ta yayi ya dora a kan marar sa ji tayi kamar akan shocking ya d'ora mata hannun saboda haka tayi sauri ta janye yaya bari naje na kira Momy saboda ni bansan mai zan maka ba, zata sauka kenan Sadeeq ya kama hannun ta idon sa a rufe yake cewa "kar ki tafi ki banni kizo dan Allah kada ki tafi" cikin karfin hali ya janyo ta ya matse ta a jikin sa yana fitar da numfashi da sauri da sauri

Gaba d'aya jikin Siddeeqah rawa yake ta kasa fahimtar mai Sadeeq din yake nufi da haka kokarin saka mata hannu a riga yake Allah ya bata sa'a ta kwace daga rukon daya mata tace "karamin mara mutunci, ashe daman kai dan iska ne to bari kaji ni ba yar iska bace inace daga waje kake to ba kaje gurin 'yan iskan naka bane?"

Sadeeq jin maganganun yayi kamar ta watsa mai garwashin wuta saboda zafin su gashi baya jin zai iya tashi bare yayi maganin rashin kunyar ta

Saida ta rike 'kugun ta ta dawo gaban sa ta dan jujjuya tayi fari da idanuwan ta tace "karamin d'an iska to duk abinda kayi min sai na fada wa Momy saboda tun muna yara ake jamana kunne akan mukula da maza shine a waje ba a lalata ni ba yanzu kai ka lalata ni" take ta fashe da kuka tana fadin "na shiga uku yaya Sadeeq yayi min ciki innalillahi wa innah ilaihi rajiun Allah kagani ni ba yar iska bace shine ya taba ni waiyo Allah Momy zata yanka ni yaya Sadeeq ka cuce ni azzalumi Allah sai ya saka min". Ta kara rushewa da wani irin kuka mai ban tausayi

Sadeeq bai fahimci mai Siddeeqah take nufi ba shidai yasan ana ce musu ko hannu suka bari namiji ya rike musu zasu dauki ciki to yana ga shiyasa yanzu take cewa yayi mata ciki😂 bai san sanda dariya ta kubuce masa ba, sai yanzu yake kara tabbatar da yarintar Siddeeqah kallan ta yayi suka hada ido tana rike da 'kugu tana jijjiga 'kirji a yanzu yaji saukin murdawan da marar ke mai saboda haka ya kamo ta cikin zafin nama tana ta zizzille wa, bayan ya daidai ta natsuwar sa ya koma mata Sadeeq din da tasani ada yace "ke dan uban ki ni kike cewa dan iska?" ta tsorata da yadda taga yanayin sa saboda haka ta shiga yi masa magiya da bige bakin ta Yace "babu ruwana ki daina buge bakin ki idan kina so kada na zane ki to kija bakin ki kiyi shiru da abinda ya faru a tsakanin mu ko Khadeeja kada ki fadama mata bare Momy idan kika yi haka kin tsira saboda nima bani nayi miki ba aljanu na ne suka miki kuma kin san aljani bai san a dunga talla da abinda ya aikata. Sai ya makantar da ke ko ya kurman taki saboda haka kija bakin ki kiyi shiru kuma ki tabbatar babu wanda ya ganki a lokacin da zaki fita daganan ".

Bakin ta narawa tace "to yaya". Sai alokacin ya sake ta ta nufi kofar futa daga bedroom din duk ta daburce dan kwalinta ma acan ta manto shi gashin kanta yayi yar batsa, sai yanayin ta ya nuna kamar bata cikin hayyacin ta tafiya take tana sand'a a haka ta fito daga ban garen sa tana gaf da shiga dakin Ummi taji ance "daga ina kika fito?". A dabur ce Siddeeqah ta juyo ta kalli Momy da ta tsura mata idanu, cikin in ina Siddeeqah tace "daga dakin yaya nike dazun dana kaima sa a binci na tsaya kallo har bacci ya kwashe ni sai yanzu da ya dawo ya tashe ni". "Amma ya na ganki a furgice yayi miki wani abu ne?". Da sauri Siddeeqah tace "babu abinda yayi min saboda daga bacci na tashi". Saida Momy ta kare mata kallon tsaf tace "kada ki boye min idan yayi miki wani abun fa kada daga baya azo asami matsala ki fada min gaskiya". Siddeeqah naso ta fadawa Momy abinda ya faru tuna kashedin da Sadeeq yayi mata yasa tace "Allah Momy babu abinda yayi min ki yadda dani Momy". Badan Momy ta yadda ba tace "jeki kada ki manta da adduar bacci". "To Momy saida safe" "Allah ya tashe mu lafiya

Ina jiran kyawawan comment dinku fans 💖💕💋

NI DA YAYA SADEEQ                  

˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

          Chapter 15

_________Washe gari da misalin 'karfe 11:00 gaba d'aya mutanen gidan zaune suke akan dining ana breakfast har da Daddy saboda jiya da daddare ya dawo, kasan cewar yau din asab ranar hutu ce babu school a tsanake muke breakfast d'in mu tunda ya doso gurin 'kamshin turaren sa ya dake hanci na ya bud'e ilahirin gurin da sanyan yan 'kamshin sa d'aga kaina nayi ai kuwa karaf muka yi ido hud'u dashi tsura masa manyan  idanuwa na nayi ko kifta su bana yi, gaskiya yaya Sadeeq karshen had'uwa ne kansa na fara kallah gashin nan na kansa ya gyara sa sai kyalli yake yi masha Allah sajan nan nasa bakinkirin dashi a gyare gunin ban sha'awa da dan gemun sa da bai wuce kamu daya ba 😜yana sanye cikin wata riga blue mai layi layi hannun ta anyi masa ninki biyu da wani botiri mai kyau da 'kyalli sanye yake da wandon jus lite blue mai kyau da tsada kasan bai kama sa sosai ba, ban san sanda na bude baki da hanci ba na cigaba da kallon sa ashe  Momy ta lura da ni kawai magana ce bata yimin ba shikuwa gogan da ya 'kara so kan dinning din sai yazo yayi kamar zai wuce ta kusa dani ya take min yatsun kafa ya   murza da karfi yayi gaba kamar bashi ne ba

Wata uwar 'kara na kwalla ina yarfe 'yan yatsun hannu na gaba d'ayan su ido suka zuba min da son jin mai ya same ni? Wasu hawaye ne masu zafi suka fara kwaran yo min saboda naji zafin murje min yatsun 'kafa da yayi "Sadeeq mai kayi mata". Daddy ya fad'a yana duban sa zaman shi kenan akan kujera ya fito da ido waje alamar firgita yace "ni kuma Daddy yanzu fa na iso ko magana banyi mata ba". Jinjina kai Daddy yayi alamar gamsuwa ya waigo ya kalleni yace "mai sunan manya me  ya sameki ne?". Ina shash-shekar kuka nace "yaya ne ya murje mun yatsun kafa na kuma ban san mai nayi masa ba".

Gaba dayan su maida kallon su sakayi ga Sadeeq da ya curo waya yake dannawa a hasale Daddy yace "ai kaji abinda tace". Fuskar  tausayi yayi ya dube ni yace "yarinya kiji tsoran Allah zaki mutu ki fad'i gaskiy saboda ni kinga da na shigo ma ko kallan ki banyi ba, ko dai aljani ne yayi miki siffa ta ya taka miki 'kafa saboda ace ni ne?".

Ido Siddeeqah ta 'kura mai sai alokacin ta tuna yace yana da aljani idan ko hakane aljanin ne ya taka ta Allah sarki bai san yayi ba ashe

Kallan ta ta mayar akan Daddy tace "kamar yadda yaya Yace ko aljani ne yayi siffar sa inaga hakane saboda wallahi...".

"Ya isa". Jiddah ta fad'a tana wuci kamar wacce aka mata wani abun ta d'ora da cewa "malama kada ki raina mana hankali na dad'e da sanin ke makaryaciya ce ba tun yau ba saboda kinga Momy da Daddy suna goyan bayan ki sai ki dunga 'kullawa yaya sharri ke ga annamimiya kina shiga tsakanin d'a da uwa wallahi..."

Tau tau! 'karan marin da Siddeeqah ta wanke Jiddah dashi kowa a wurin mamaki yake! banda Sadeeq saboda yafi kowa sanin halin ta shammatar ta ta kuma yi ta dad'a mata wani tas! 💃Gaba daya ji da ganin Jiddah sun tsaya dauke sai wasu taurari da take gani can kuma duhu ya rufe ta

ran Siddeeqah a 'bace ta cukwuikwuyi wuyan rigar Jiddah "wallahi yau koni ko ke sai naji dalilin da yasa ki ka kirani da annamimiya".

Tuni idanunun Jiddah suka furfito waje saboda sha'kar da Siddeeqah tayi mata daman ita ba wata mai 'karfin azo agani bace sai tsinanniyar tsokana da kin ma'kure ta ta koma fuskar tausayi, gashi ita kuma Siddeeqah babu hakuri wani lokacin har jira take ka taba ta tayi rashin mutunci, yau jin zuciyar ta take asama saboda haka ta fara kaiwa Jiddah naushi a baki tana fad'in "wallahi saikin fad'a min inda na had'a  d'a da uwa idan ba haka ba mai...".

"ke sake ta kafin na tashi na 'babballaki". Sadeeq ya fad'a yana nufo inda nike ni kuwa bil ha'k'ki naushin Jiddah nike abaki yanzu haka na fasa mata yana zubar jini

"Kada ka sake ka buge ta zan 'bata maka rai saboda tayi min dai-dai tunda ba da ita ake yi ba ta ara ta yafa yanzu Khadija da Ummi da basu sa baki ba ai ba ayi dasu ba". Momy ce tayi wannan maganar zaiyi magana Daddy yace "nima ai tayi min dai-dai saboda haka ko kallon banza ban yarda kayi mata ba".

Khadija dai bazan ce taji dad'i ba saboda ita bata san fitina kana kallon fuskar ta kasan ba a yanayin jin dad'i take ba Ummi kuwa saboda farin ciki bakin ta ko rufuwa bai yi har kai naushi take kamar ita ke dukan saboda ba wani shiri take yi da Jiddahn ba kasan cewar ta ba 'yar Momy ba yar yayan Momy ce wato kanwar Mubarak da ke 'kasar India karatu tun sanda mamar su ta rasu ta dawo gurin Momyn da zama a lokacin tana da 7 year's old kuma ita ma sa'ar su Siddeeqahn ce a ran ta tace "da jiya na biyema Jiddah da da ni za a fara soboda sanda ta shiga kitchen ta tarar da ita tana hada tea bata tanka mata ba ta hau fad'ar magan ganu kamar yadda ta saba.

Umar har yafi Khadija damuwa saboda shi harda guntun hawaye.

A lokacin da ya 'kara so inda muke caraf ya d'auke ni daga kan Jiddah zai aje ni Momy tace "a a kasan fad'an Siddeeqah baya 'karewa indai aka taba ta to sai ta rama, kaita sama cikin dakin ka idan Jiddahn ta shiga dakin ta sai Siddeeqahn ta sauko".

Ina ji ina gani yaya ya haura dani sama ba dan raina yaso ba, dan ni da so samu ne a bar ni da ita na koya mata hankali saboda tana da raini da jin kai ni kuma bana jure wa dan ko babba ba 'karamin nauyin sa ni keji ba idan har yaga yayi min ban rama ba.

Kamar yadda Momy tace bai dire ni a ko ina ba sa a cikin falon sa ya maida kofar ya rufe da dan mukulli sannan ya zare ya saka a cikin al'jihun sa ya nemi kujera 2 cter ya kwanta ya lumshe ido

Sosoi bakin Jiddah ke zubar jini tuni Daddy ya wuce ban garen sa saboda yadda Jiddahn ke rusa ihu kamar wacce aka aikoma sa'kon mutuwa

Khadija dur 'kushe gaban Jiddah cikin tausaya mata take mata sannu kana daga bisani tace "sannu Little sister zaki iya tashi mu tafi asbiti saboda aduba lafiyar ki?".

Bata gama rufe baki ba Momy ta kara so daga tsaye tace ai daman ance jiki magayi gobe sai ki kara, ke kuma kin zo sai faman sannu kike mata ba ita tajawa kan ta ba? Maza d'auko mayafin ki kije ki" cewa "driver ya tada mota saboda ku kaita ayi mata dressing din bakin ta".

"Wallahi Momy ko da ita ce da laifi bazan iya jure kallon ta cikin wani hali ba na kyale, itama Siddeeka saboda 'yar uwa ta ce amma baki ji yadda zuciya ta ke mini ba a lokacin da abin ke faruwa".

Ko kala Momy bata kuma cewa ba.

Duban Umar Khadija tayi tace "kaje ka cewa Idi driver ya tada mota sannan idan ka dawo ka dakko mini gyale na dana Jiddah".

NI DA YAYA SADEEQ                 ˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 16

______"To" Umar ya fad'a yana mai mi'kewa jikin sa babu 'kwari Khadija sai sannu take ma Jiddah da bakin ta ya kumbura yayi suntum sai zubar jini yake Umar bai wani jima ba ya dawo "Aunty Khadeeja na fad'a masa bari na haura sama na d'auko muku mayafin" "To" Umar khadija ta fad'a tana rungume 'yar uwar ta a 'kirji A haka Umar yadawo ya iske ta ya mi'ka mata ta ansa ta yafa sannan ta yafa ma Jiddah "zaka bimu ne?". "Eh zani". "To muje ko". Tafad'a tana d'aga Jiddah daga jikin ta "sannu sister daure ki tashi na kamaki sai mutafi asbiti ayi miki dressing kada abinda kike rainawa yazama babba da 'kyar Jiddah ta iya kama hannun Khadeeja tana waiyo waiyo ta samu ta mi'ke kallo d'aya zaka yi mata ta baka tausayi saboda yadda bakin ta ya kumbura da taimakon Allah da na Khadija suka fito falon a lokacin Idi driver ya tada mota Habu mai gadi ne ya hango su cikin sauri ya 'kara so inda suke ya bud'a masu 'kofa yana yiwa Jiddah sannu Umar kuma ya zagaya ta d'ayan bangaren ahankali Jiddah ta shiga khadija ta mara mata baya Habu mai gadi ya wangyale musu get suka fice

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾

Tsaye Siddeeqah take ri'ke da kugun ta sai zum 'bure zum 'buren baki take yi a cikin ran ta take fad'in "kai kuwa matar ka ta bani ayi mutum dun kum ba za ayi fira da shi ba sai kace wani boss kullum fuska daure" "ke mai ki ka ce ina wasa dake?". Abinda Siddeeqah bata sani ba ba acikin zuciyar ta tayi maganar ba sarai sadeeq yaji mai tafad'a

'ko'korin tashi yake yazo ya cimmata sai wayar sa ta shiga naiman dauki da kamar bazai duba ba saboda wannan yarinyar ta 'bata masa rai amma sai wata zuciyar tace "ya duba dai yaga wake neman sa". Haka kuwa akayi dauko wayar yayi daga kan hannun kujera, Baby shine sunan da yake yawo akan screen d'in, take ya saki murmushi  harda d'an cije leban sa na 'kasa ya gyara kwanciyar sa da kyau Baki bud'e Siddeeqah ke kallon sa a tunanin ta aljanin ne ya motsa Amma sai taga ya d'aga wayar ya kara a kunne baiyi magana ba daga can 'ban garan aka ce _"Amincin Allah ya tabbata a gare ka ina fatan wanda nafi so da kauna a duk duniya ya wayi gari lafiya koda yike naji a jiki na kana cikin koshin lafiya saboda inajin duk wani yanayi da ka ke ciki a jiki na_".

Sadeeq kusan suman kwance yayi saboda shi a rayuwar sa yana son kula wa musamman a bangaren soyayya zai iya 'bata lokaci mai yawa wajen tsara kalaman soyayya saboda shi a yadda yake gani idan bai ba ma soyayya hakkin ta ba bai more rayuwar sa ba

Bakin sa washe kamar tana ganin sa yace _"gimbiya sarautar mata ina fatan amincin tare dake"_ "Na gode My". Jiya na gaji ban san sanda bacci ya dauke ni ba dan Allah kaya kuri ban kira naji yadda ka iso gida ba".

"Kada ki damu baby Allah ya kare miki ni da kariyar sa na zo gida lafiya kema fatan dana baro ki babu abinda ya taba min ke".

Zuby na dariya tace "kana nufin har na kai a bani irin wannan kulawar sai kace wata gimbiya?".

"Haba ke kuwa ai kin wuce gimbiya a gurina ko kin mata da auren ki nike so nayi? Nan da kika ganni akan abinda nike so bani da sakaci ina basa kulawa ta musamman".

Cikin kissa da kisi sina Zuby tace "yanayin muryan ka ya nuna min baka karya ba kana jin yunwa".

Sai alokacin Sadeeq ya tuna ashe bai karya ba,

ni kuwa duk sona da gulma dole na kyale Siddeqa saboda na kasa fahimtar yanayin ta har yanzun a tsaye take idon ta akan Sadeeq kyam shi kuwa bai san tana yi ba ya tafi duniyar masoya

Ya cigaba da ce wa "wallahi Baby na manta". "My kamanta fa kace yanzu fa 12:00 gaskiya ka daina barin mun kanka da yunwa saboda ba kan ka ke bari ba ni kake bari idan kuma kanason na cutu ai shikenan".

"Haba Baby na na daina insha Allah zan dunga kula miki da kaina kamar kina gani na dazun ma har zan karya sai wasu 'kannai na suka kama rigama har sukayi doke doken juna to shine duk naji raina babu dadi".

"Ayyah my sorry kasan sha'anin yara sai ana hakuri da su amma gaskiya ka tashi ka je ka ci abinci idan ka gama bayan sallar azahar saika kirani mu daura daga inda muka tsaya".

"To ranki shidade na gode da kulawa I love you". 💖 "I love you too" "By" "okay by take care for me". zuwa yanzu Siddeeqah ta nemi guri ta zauna amma wannan karan ba shi take kallo ba da yatsun hannun ta take wasa saboda yadda take jin ranta babu dadi.

Shi kuwa Sadeeq har cikin zuciyar sa ya manta da wata Siddeeqah a d'akin sa shiyasa ya saki baki ya yi ta suru tu

Kallon sa tayi tace "yaya zanyi fitsari" banza yayi da ita kamar bai ji mai tace ba

Can da taga fitsarin zai iya zubo mata tace "yaya yafa matse ni zai zubo".

Sai a alokacin ya dago kai suka had'a ido, bai kula ta ba ya tashi ya shiga bedroom din sa bai jima ba ya fito hannun sa rike da mukkullin mota ya nufi 'kofar fita  batare da yace mata komi ba  ganin haka tayi sauri ta mike kafar ta a matse ta soma tafiya alokacin shi har ya bude kofar ya fice

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾

Kwance take akan gadon da ake kwantar da marasa lafiya anyi mata dressing din bakin ta kuma an sa mata ledar 'karin ruwa ga dukkan alamu ma batasan wa ke kanta ba saboda allurar baccin da aka mata Khadija na gefe tayi tagumi Umar ma haka kowa da abinda yake sakawa a cikin ransa

_Na gaji da typing amma idan harnaga ruwan comments zan kara yi muku wani typing din anjima_ 🙏 NI DA YAYA SADEEQ ˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙ Chapter 17 _____Ringing din wayar Khadija ne ya katse shirun nasu bayan ta fiddo wayar Sunan Momy ya bayyana akan screen d'in wayar da hanzari ta d'auka ta kara a kunne tace "Aslm Momy". Daga can 'ban garen Momy ta amsawa Khadeeja da "W/slm Khadija naji ku shiru ne shine nace bari na kira naji ya ake ciki?". "wallahi Momy lafiya lau anyi mata dressing din bakin ta ne sai karin ruwa da aka sa mata". "sai yaushe kenan zaku dawo?". "dazaran ruwan da ake 'kara mata ya 'kare saboda nurse d'in tace zamu iya tafiya ba wani ciwo bane kawai buguwan da tayi ne, saboda ce mata nayi fad'uwa tayi abayi ta bige". "yayi kyau". Momy ta bawa Khadija amsa daga haka suka yi sallama

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Da bibbiyu Sadeeq yake tsallake steps soboda yana son yaje wurin cin abinci kafin a kira sallar azahar kici'bus yayi da Momy a dai dai lokacin da ya gama sauko wa daga steps din cikin sakin fuska Momy tace "ah Sadeeq ga fa abin karyawan ka can fuskar ka tayi zuru zuru nasan kuma yunwa ce kake ji".

"eh wallahi Momy yanzu haka saurin da ki ka ga inayi restaurant zani".

Kafin Momy ta ba Sadeeq amsa Siddeeqah ta sauko daga sama d'an kwalin ta rike a hannun ta tana susur kanta d'ayan hannun ta kuma rike take da bakin zanin ta daya kwance tayi wani iri da ita yayanayin ta ya nuna alamar tana cikin damuwa

Kallon ta Momy tayi na wasu 'yan da'kiku bayan ta gama nazarin ta tace "Mai gaskiya lafiyan ki ki kayi zuru zuru dake ko kema yunwar ce". "wallahi Momy nima haka kawai naji ni wani iri ina Ummi take?". "Ummi tana sama tun da kuka haura tabi bayan ku kin san ta da bacci idan babu makaran ta tana can tana sana'ar". D'an ta'ba baki nayi nace to ina Khadeeja?". "ta raka Jiddah asbiti ayi mata dressing d'in gurin da taji ciwo". "To Momy nima bari naje na huta". "ba dai ki huta ba kije ki shirya Sadeeq ya kaiki gurin gyaran kai saboda jibi ne tafiya makarantar ki in Allah ya kaimu". Jiki na ne yayi sanyi ni wallahi da zasuji ta tawa su 'kyale ni na cigaba da rayuwa ta a haka saboda banga aibin ta ba "Maza mana kije ki shirya Siddeeqah tunanin me kike yi haka?". Momy ta tambaye ni "babu komai". na fad'a ina haurawa sama Maida duban ta tayi ga Sadeeq da yayi kicin kicin da rai kamar wanda akece ga ranar mutuwar sa "ba sai kaje restaurant ba ga kayan da mukayi breakfast can na hana suwaiba ta kwashe kaje ka karya saboda ka kai Siddeeqah wajen gyaran gashi kanta yayi wani iri".

"Haba Momy asa idi driver ya kai ta mana ni inada uzurin da zanyi". ya 'karasa fad'a kamar zai rushe da kuka Saida Momy ta 'kare mai kallo sannan tace "lallai Sadeeq kana da aiki tana matsayin matar ka ace sai wani driver ya kai ta gurin gyaran gyashi to kai maye amfanin ka da bazaka kula da iyalin ka ba?". Yana sosa 'keye ya ce "uhm Momy baza ki gane bane amma wallahi ba wani son yarinyar nike ba kawai dai zan hakura ne saboda nayi muku biyayya". Tabe baki Momy tayi kana tace "ina tausayin ka Sadeeq amma kaje kayi duniya ce" Ba tare da yaji komai aran sa ba ya nufi dinning tebur Momy ma d'akinta ta wuce abin ta saboda Daddy yana gida

Zuciyar Sadeeq a cun kushe ya bud'e kular farfesun hanta ya zuba a filet kana yaja kujera ya zauna ya d'auki cokali ya fara cin farfesun amma sai yaji kamar yana cin magani saboda magan ganun da Momy tayi masa basu yi masa dadi ba, haka ya bar cin abincin ya ciro wayar sa yad'an shafa screen d'in wayar ya danna number Farooq saida Wayan ta fara ringing sanan ya kara a kunne ringing d'in farko Farooq d'in ya daga yace "officer officer". Muryan Sadeeq a murtuke yace "kayi maganar makarantar yarinyar nan kuwa?". "d'an iska wai saurin me kake yi haka yaushe garin ya waye". Sadeeq na jin amsar da Farooq ya bashi yayi saurin katse kiran yana Jan wani dogon tsaki "mtssss". Adai dai lokacin Siddeeqah ta sauko daga sama tayi fes da ita sanye take cikin shigar doguwar riga 'yar dubai mai ruwan hanta ta yafe kanta da mayafin rigar duk da ba kwalliya tayi ba amma tayi kyau abinka da farar mace mai siririyar fuskar da ke d'auke da dogon hanci gaskiya tayi kyau ko ma'kiyi dole yace masha Allah saboda kama take da larabawa.

Gaban sa ta tsaya tace "yaya na shirya". Wani mugun kallo ya watsa mata gami da cewa "dan uban ki ni sa'an ki ne zaki 'bace min dagani ko saina tashi na yi ball da ke". Kafin Siddeeqah tayi wani yun 'kuri Momy ta fito daga part din ta. Tana Murmushi ta 'karso gurin Siddeeqah ta kama hannun ta ta kalli fiskar ta tayi fayau da ita masha Allah "gaskiya irin wannan kyau haka kamar zaki gasar kyau". Rufe fuskar ta tayi da mayafinta ta ce "Allah Momy banyi kyau ba ko hoda da kwalli ban shafa ba". "ai gwara da kika bar fuskar ki ahaka sai ainihin kyanki ya dad'a fitowa masha Allah". Tana Murmushi tace "Momy da gaske ina da kyau?". "wata ta ta'ba kiran ki da mummuna ne?". Waigawa tayi inda yaya Sadeeq yake suka had'a ido ya balla mata harara Momy na lura dasu idan ta fahimci Siddeeqah Sadeeq ne ke ce mata mummuna. Kafadar Siddeeqah ta dafa tace "rabu dashi mai sunan manya kinfi shi kyau nesa ba kusa ba kishi yake dake amma ko makaho ya shafa yasan kin fita daban kama da larabawa kike yi wallahi da za a kwana ana fad'ama wani ke hausa fulani ce bazai yadda ba har sai kinyi magana yaji muryan ki". Murmushi ne kwance akan fiskar Siddeeqah tace "Allah yabar mana ke Momyn mu ta bata fek kiss a kumatu". Kallan sa Momy tayi tace "tashi mana Sadeeq ka kai ta ta shirya kai take jira". Kamar zaiyi kuka ya ce "yanzu sai a ganni da wannan abar rigi rigi zan kaita gurin gyaran gashi ai abin kunya ne". Momy na dariya tace "Sadeeq kenan wani lokaci idan kayi wani abu sai ka dawo kamar karamin yaro, Siddeeqah ce zaka ce wannar abar? Allah ya shirya ka amma aganina ganin ka tare da ita zai 'kara maka girma saboda iyalin ka ce".

NI DA YAYA SADEEQ                       ˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 18

______"haba Momy 'yar wannan abar ce zan fita da ita a matsayin iyali na?". "Eh Ita d'in fa wallahi Sadeeq ka kiyaye ni ka raina ni ko? Duk abinda nike fad'a maka abanza nike fad'i saboda baka d'auka". "Momy dan Allah kiyakuri na daina ki ce mata ta wuce mu tafi". "Au bakin ka ciwo yake da bazaka  fad'a mata ba kai? Ko kafi 'karfi ne? Sadeeq ina raba ka da kiwan kyalla kana shige wa kyallah ta haihu". Momy ta fad'i haka cikin dakiya da tsitstsire sa da ido Kame kame ya fara

Siddeeqah da taji haka tace "Momy sai mun dawo".

"to adawo lafiya 'yar albarka".

Harabar gidan ta fito  taja ta d'an tsaya kamin yayan nata ya fito su wuce,

adai dai lokacin mlm Habu ya wangele get motar su Jiddah ta silalo ciki idi driver ya samu guri yayi faking kana ya fito ya bude musu murfin motar Khadeeja ce ta fara fitowa sai Umar ya fito saida Khadeeja ta zura kan ta da hannayen ta a cikin motar ta kamo Jiddah da kyar Jiddahn ta iya fito wa tana ciccin magani, saboda yadda take jin zuciyar ta na mata daci da radadi akan dukan da Siddeeqah ta mata, ita kadai tasan kalan tanajin cin mutuncin da tayiwa Siddeeqah.

kallo daya Siddeeqah ta musu ta kawar da kan ta gefe tana dariya ciki ciki saboda yadda taga bakin Jiddah ya yi sun tumeme Sadeeq ne ya fito shima ganin Siddeeqah na dariya ita kad'ai abin ya bashi mamaki yana shirin daka mata tsawa sai ya hangi Khadija rike da hannunan Jiddah Umar na biye da su suna taho wa Kallo na yayi kamar zai yi magana sai kuma ya fasa. Ya yi gaba abin sa cikin sauri nima na mara masa baya ba tare da na lura ba naji na ci karo da mutum a tsorace na ja da baya ina yarfe hannu na, ganin Jiddah ce na bige "mttsssss" na ja wani dogon tsaki naga sanda Khadija ta yi mata magana da alamar dai mantuwa tayi a mota saboda naga cikin motar ta koma  Idan jidda yayi 'kwala 'kwala murayan ta na rawa tace "wallahi zaki san kin ta'ba ni yarinya zan nuna miki kalar nawa rashin mutuncin banziya d'iyar shegu ke idan....". "Tas tas". shine 'karan marin da Sadeeq ya wanke Jiddah da shi yana wuci yace "kada na kara jin kin ce mata shegiya duk lalacewar naka naka ne saboda hannun ka bai ru'bewa ka yanke ka wurgar ita d'in jinjin ki ce nasan kin San da haka. 'bace min dagani kafin na 'ba'b'ballaki".

Jiddah kusan suman tsaye tayi saboda yadda taji saukar marin batayi zata ba lura Sadeeq yayi da Jiddahn bata cikin hayyacin ta d'an ta'be baki yayi ala mun ko a jinkin sa, kana ya kallo ni nayi sauri nayi 'kasa da kai, zaki wuce mu tafi ko sai na had'a dake munafuka kidinga yin abu sumi sumi to ki kaddara aure na dake... ".

Bai 'karasa maganar ba kira ya shigo a wayar sa laluba aljihun sa yayi ya fiddo batare da ya kalli sunan mai kiran sa ba yayi picking call d'in gami da karawa a kunnen sa sannan yayafito ni da hannu ya yi gaba. Sai a lokacin Khadeeja ta iso kallo na take yi nima da kallon na bita yaya Sadeeq har ya shiga mota, nima bu'de gidan baya nayi na shiga na zauna, sai Sadeeq d'in ya waigo fuskar sa a murtuke yace "ke uban waye diraiban ki zaki dawo gaba ki zauna ko saina miki tsinannan duka". "uhm" na fad'a kana na dawo gaban motar. Habu mai gadi ya buɗe masa get ya fice daga gidan

Khadija na taba Jiddah tayi luuuuu zata zube a 'kasa cikin hanzari Khadeeja ta mai do ta kirjinta ta rungumeta mamaki kwance akan fuskar Umar yace "wai aunty Khadija mai yasameta ni ma yan zu na dawo kina tafiya nima naje gurin Habu mai gadi". Cikin kuka Khadija tace "Umar wannan wace kalar rayuwa ce daga wannan sai wannan gaskiya ni na gaji Zan roki Daddy ya barni na koma kaduna da zama wallahi bana son tashin hankali, nasan ita da Siddeeqah ne ko yaya tunda ina zuwa suka bar gurin". Ta 'karasa fad'a tana rushewa da wani irin kuka mai ban tausayi.

Tana kokarin kama Jiddah sai ga Daddy ya fito da alamar masallaci zai je soboda ankira sallar Azahar, hannun sa d'auke da gorar ruwa ta faro, hango 'ya'yan sa daya yi cikin wani hali yasa shi karasa wa gurin su da sauri

Allah sarki mahaifan mu  ko mai zamuyi musu bazamu taba biyan su ba saidai muyi musu adduar Allah ya yafe musu yayi musu sakaiya da gidan aljanna fiddausi 🙏

"Khadija mai yasameta nehaka? na gan ku cikin tashin hankali". Daddy ya tamabaye ta

Murayan Khadeeja na rawa cikin kuka tace "Daddy wallahi nima ban sani ba yanzu muka dawo daga asbiti shine na barta anan na koma mota dauko magun-gunan da aka bamu, nan dai Khadija ta kwashe labarin abin da ta sani ta fad'awa Daddy gorar ruwar  hanun sa ya bude murfin ta ya zuba rawa a tafin hannun sa ya watsa wa Jiddah a fuskar ta nan take taja dogon numfashi ta sauke 'kirjin ta na bugawa da sauri da sauri kara rungume 'yar  uwar ta tayi tana sauke ajiyar zuciya ganin ta farfado yasa Daddy cewa "ku shiga daga ciki Umar zo mu tafi masallaci". "To Daddy".

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Aban garen Sadeeq kuwa wani 'katon plaza ya kai ni mai kyau da tsari bakin Siddeeqah a sake take kallon gurin saboda ita tun da take bata ta'ba ganin kasuwa mai kyau irin wannan ba badan taga basuyi tafiya mai nisa ba da sai tace kasar ya bari da ita yana gaba tana bin sa a baya har suka isa daidai bakin wani 'katon shago mai dauke da kofar gilas tafke ke irin wacce na ciki yake ganin na waje amma shi na waje baya ganin na ciki

Wani abun Sadeeq ya danna a jikin bangon shagon can sai ga wata mata ta fito da ganin ta ba bahaushiya bace saboda a kwai 'karin gashi a kanta kuma babu mayafi a jikin ta rigar ta irin mara hannu ce sai wani d'an gajeren sikel da take sanya dashi, da turan ci Sadeeq yayi mata magana itama ta mayar masa bayan sun gama naga ya ciro kudade masu yawa ya mika mata ta amsa tana godiya yace "bita mana kika saki baki da hanci kina kollo na kamar yau kika taba gani na".

Bayan sun shiga daga ciki Siddeeqah ta ga Mata a zazzaune akan kujeru masu kyau da burgewa wasu kuma an saka musu kan su a cikin wani inji yana kara wuuuu haka dai Siddeeqah tai tabin gurin da kallo kamin ta zauna a kan wata kujera da babu kowa , tsoro ne fal a cikin ranta saboda yadda taga ana sa mutum cikin inji gaskiya ita baza ta yarda a sata ba aje a fille mata kai ana zaune 'kalau da ido matan gurin suke kallon ta ganin ta suke kamar balarabiya wata a cikin su ce tayi karambani tace "sannu baiwar Allah". Kallon ta Siddeeqah tayi sai taga babbar maca ce saboda a kalla zata kai shekara 30 a duniya Adan dakile tace "yauwa sannu Aunty". Saida gaba daya matan gurin suka kalli junan su saboda yadda suka ji muryan ta sanyi ga dadi haruffa suna fita dai dai kamar koyan hausar tayi masha Allah

Saida aka gama ma wasu mata sannan layi yazo kaina mai saloon din ta dube ni "kanwar oga taso ki zo layi yazo kanki". A tsorace Siddeeqah ta tashi tace "amma ni dan Allah kada ku sani a cikin wancen injin ku wanke mun kaina kawai haka".

"To bazamu saki ba tashi muje" mai saloon tace

Bayan wasu mintocin da basu haura talatin ba saiga shi Siddeeqah ta fito das da ita an gyara mata kanta har kyalli yake bayan kamshin da yake tashi asalin kyanta ya kara baiyayana masha Allah a gaban katon madubi ta tsaya tana kallon yadda aka gyara mata gashin  duk tsayin sa da cikar sa anmayar dashi guri daya anyi mata faking a tsikayar kai sai shafa kan take tana murmushi saboda ita kanta tasan tayi kyau. Mai kula da gurin ce tazo tace "kan war oga ya dawo yace kizo ku tafi". "to". Na ce na yafa mayafi na ta zuge min glass na futo

A jikin motar sa na hango sa hannayen sa dore akan kirjin sa ya zuba min idanu kamar wani maye😅 da ni ke kallon sa haka da yace "uban me nike kallo". ahankali na karaso inda yake bai ce min komai ba ya zagaya yashiga nima na shiga ahanya ya kunna mana karatun alkur'ani mai girma muna saurara naji na kara samun natsuwa sosai kuma hankali na ya kwanta gaskiya alkur'ani rahama ne a tare damu saboda yadda yake samara da bayin Allah nutsuwa da kwanciyar hankali.

Cikin wata unguwa ya shiga damu mai gidaje iri daya A bakin get din wani gida naga yayi faking sannan ya dauko wayar sa ya dade yana danne danne yana dariya harda yin kiss a wayar ni dai ban ga ya kira kowa ba sai na ga ya aje wayar

Can sai ga Zuby ta fito sanya da d'ikin atamfa riga da siket amma irin dinkin nan ne da ake cemai jahannama ga fasinja saboda komai na jikin ta ya bayyana mayafin ta a kafada ta doro shi bakin ta dauke da cingom tana taunawa yana kas

Tabe baki Siddeeqah tayi kana Ta cigaba da da kallon ikon Allah

Bangaren da nike tazo ta bud'e gani na da tayi a ciki yasa tayi turus harara ta wurgomin taja dogon tsaki ta maida murfin ta rufe, cikin masifa ta dawo bangaren da Sadeeq yake tana jijjiga kafa

Tace "wace ce wannan ka kwaso Sadeeq? kamar aljana ko gamo nayi ni Nike ganin ta kai baka ganin ta?".

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Ina mai baku hakuri akan rashin jina da kuke yi a

Ina godiya da yadda kuke nuna min kauna Allah yabar mu tare ya hada fuskokin mu a cikin aljanna fiddausi

Dan Allah duk wanda yake karanta min book yayi kokari ya dunga yimin comment da share nagode taku har kullum *Siddeeqatul khairy Yahya * (S beauty✍️)

NI DA YAYA SADEEQ

Story and Writer by Siddeeqatul khairy Yahya ( *S beauty*✍️)

˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Page 19

______dawo da kallan sa yayi izuwa gare ni ya wurga min harara kana ya kalli Zuby da take cika tana ba tsewa saida ya saki fuskar sa ya fad'ad'a ta da Murmushi yace "uwar gida sarautar mata duk kishin ne haka ko gaisawa kin ki bari muyi ki kwantar da hankalin ki akan wannan abar". Ya nuna mata ni da hannu kana ya cigaba da cewa "ina da ke mai zanyi da ita ko baki kare mata kallo bane? Ko matan duniya sun kare bazan so wannan abar ba danni kallon na miji nike mata". Muryan Zuby a dakushe tace "to maye halakar ka da ita? da zaka zo gurina sai kazo da ita, ni wallahi har kasa naji na tsane ta saboda ko macen kuda bana son tarabeka bare kuma macen da halakar aure zai iya shiga tsakanin ku, ina kishin ka ina yi maka son da bazan iya kwatan ta maka ba idanuwa basa iya ganin sa dan Allah Sadeeq kada ka ci amana ta, ka soni koda rabin son da nike maka ne ". Idan Zuby har ya cika da kwalla, Sadeeq kuwa jikin sa yayi sanyi a ransa yake shawara "shin ya fad'a wa Zuby matsayin Siddeeqah a wurin sa ko kuwa yayi mata karya". saboda ya hango tsantsar kishin sa da 'kiyayyar Siddeeqah acikin 'kwayar idanun ta gwauran numfashi ya sauke yace "Baby ki kwantar da hankalin ki 'diyar mai gadin mu ce fa". Kallon sa Siddeeqah tayi suka had'a ido ta tintsire da dariya tace "saboda ka wulakanta ni zakace diyar mai gadin gidan ku ce ni?, to badiyar mai gadi bace kadai fadi wani". A fusace ya daga hannu zai kwada min mari, Zuby tai saurin ce masa "abinda ta fad'a gaskiya ne shiyasa zaka dake ta na shiga uku Ni Zubadah Sadeeq mai kake nufi dani?". "ki saurare ni baby wannan yarinyar da kike gani munafuka ce idan kuma kin yarda da abinda ta fad'a shikenan amma ni iyakar gaskiya ta na fad'a miki". "haba Sadeeq da ganin wannan yarinyar ba d'iyar mai gadi bace jibe ta fa da larabawa take kama fatar jikin ta luwai luwai, wai ka ta'ba kare mata kollo kuwa dan Allah Sadeeq ka kalle ta yanzu". Wai gowa yayi ya kalleni na tsawan wasu yan sakonni kana ya cigaba da kallon Zuby, mi'ko masa wayar ta tayi tashiga camera tace "kaima kalli kan ka ka gani". Sadeeq bai fahimci inda Zuby ta dosa ba shidai kawai biye mata yake, bayan ya kalli kansa ya mi'ka mata wayar, tace "ina fatan ka fahimci inda na dosa yanzu?". Kai ya girgiza mata alamar bai fahimci komai ba tace "ina son ka fad'a min maye Alakar ka da 'yar mai gadi da har kake kama da ita? Wallahi ko alqur'ani aka bani zan dafa ita d'in jinin ka ce Sadeeq maiyasa kayimin kar...". Tsawa ya daka mata gami da cewa "ke ashe bakida hankali? ni zaki duba tsabar ido na kice min makaryaci tabbas zan nuna miki kuskuren ki". Sai yanzu Zuby taga rashin dacewar abinda tayi a fusace Sadeeq yayi ribas Zuby na kwala masa kira, amma ina ransa ya riga ya baci figar motar yayi sosai yake gudu akan titi saura kiris ya daki wata mota da ta fito daga wani layi zata hau titi sai Allah ya takaita abun yayi sauri ya ci burki idanuwan Siddeeqah sun yi kulu kulu tsoran ta kada yaje ya kashe ta tasan ya kashe banza wayar sa ce ta fara ringing amma ko ta kanta bai bi ba koda yazo bakin get din gidan su sosai yake danna horn mai gadi a tsoroce ya leko ganin yallabai ne yasa yayi sauri ya wangale masa get din acikin ran Habu yake cewa "ko waya tabo yallabai yau?". Bayan Sadeeq ya sulala motar sa cikin gidan, yanemi waje yai faking da sauri Siddeeqah ta kai hannun ta da niyar ta bude motar ta fita sai taji ta a kulle gam, alokacin Sadeeq ya hada kansa da sitiyarin mota tsoro ne fal acikin zuciyar ta, tana jin yadda zuciyar Sadeeq ke harbawa da sauri da sauri ahalin yanzu tasan ko sunan sa ta kira shake mata wuya zaiyi komawa tai ta zauna itama tayi tagumi hawaye na saukar mata da batasan dalilin zuwan su ba

*Dan Allah duk wanda ya karanta yayi min comment da shera ngd*

NI DA YAYA SADEEQ                   

˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 20

______Sun d'auki kusan mintuna goma shabiyar a haka batare da d'ayan su ya yi 'kwa'k'kwaran motsi ba sai sautin bugun zuciyar Sadeeq dake sauka fat fat, Siddeeqah kuwa duk da akwai na'urar sanyin dake saka cikin motar saida tajike da gumi sharkaf, idanuwan ta suka dad'a fitowa waje. dago raunannun idanun sa yayi da suka koma launin gwauta saboda tsabar bacin rai ya sauke su akan na Siddeeqah, da sauri ta maida kanta kasa tana wasa da y'atsun hannun ta zuciyar sa ce take ingiza sa da ya shake mata wuya wata zuciyar kuma ta ce masa "Kul Sadeeq ka kashe gawar da ba taka ba, ka bud'e mata mota ta fita" haka kuwa akai yabi shawarar zuciyar da ta gar gad'e sa soboda haka ya bude mata murfin motar Siddeeqah naji ya bud'e tayi sauri ta bude murfin ta fito har tana neman dungurawa a kasa soboda yanayin Sadeeq d'in yayi mugun bata tsoro da sauri da sauri take tafiya jefa kafar ta kawai take batare da tasan inda take jefewa ta ba, ji tai ta ci karo da mutum a tsorace ta ja da baya ganin Sadeeq ne yabiyo ta d'ayar hanyar da ake iya haduwa da Wanda yabi ta gaban gida, yanda taga yanayin sa har yafi d'azun firgitar wa idanuwan sa sun kara yin jaa kamar Jan gauta, nufo ta ya fara yana d'an Murmushi yana shafa sajen sa, 'kafa mai naci ban baki ba gudu ta fara shima ya mara mata baya cikin ikon Allah saiga Momy a harabar gidan da alamar wani abu take nema saboda idanuwan ta a kasa suke, da gudu Siddeeqah taje bayan ta ta 'boye tana nishi "ke lafiyan ki kuwa daga ina haka kamar an koro ki?". Momy ta fad'a tana duban Siddeeqah Bata lura da Sadeeq ba, da hannu Siddeeqah ke nuna mata inda Sadeeq yake sai alokacin Momy ta dube sa, washe baki yai ya wayance yace ma Siddeeqah "ba dai kin ki bari na kama ki ba nima zan rama yarinya, waifa Momy ce mata nayi ta jirani mu taho tare shine ina gama faking ta rigani fitowa shine nabi bayan ta da ta hango ni sai tafara gudu nima shine na biye mata". Siddeeqah kamar sakarya haka ta saki baki da hanci tana kallon shi lallai ya iya tsara labari,

cikin gamsuwa da abinda ya fad'a Momy tace "ai da baka biye mata ba yarinya ce, amma gaskiya kun dade ko ka kaita wani gurin ne? Daddyn ku na ta kiran ka a waya baka dauka munyi tunanin ko ba lafiya ba hankali ya fara tashi". "Wallahi lafiya lau Momy layi muka tarar a gurin saloon d'in, amma me ya fito dake naga kamar wani abu kike nema?".

"to babu damuwa, eh wallahi d'an kunnen Jiddah ne  guda daya ya fad'i sanda suka dawo daga asbiti".

Tace "anan ya fad'i shine nace bari na duba ko zan gani".

"haba Momy ke da kanki ina sauran yaran gidan?".

"Suna ciki Khadija ta ce ta gaji zata shiga ta huta dan ko abincin rana bata ci ba, Umar kuma yana tare da Jiddah, Ummi kuma tun safe ban kuma ganin ta ba".

"Kibar neman haka Momy muje ciki ba rabon ta bane kawai sai asai mata wani".

"dama a cikin irin tsarabar da Bilkeesu ta kawo musu ne alokacin da ta dawo daga India daham ne yanada tsada sosai yanzu ita kadai ce ba ta da".

"Momy ita ta jawa kanta".

Siddeeqah kamar ruwa ya cinye ta Momy ce ta kama hannun ta tace "muje ciki yau na girka abinda ki ka fi so a bincin gargajiya".

"dan Allah fa Momy?".

"zan miki 'karyane?".

"a a Momy".

Ta fad'a tana rufe fuskan ta da tafin hannun ta ahaka suka karasa cikin gidan Siddeeqah na mamakin Sadeeq,

Yayin da shi kuma ya ji haushin ganin  Momy a harabar gidan batare da ya ma Siddeeqah matsiyacin duka ba dan so yayi ya mata dukan ban kwana saboda ba lallai ya kuma haduwa da ita ba har sai ta dawo hutun makaranta, yanda bazata manta dashi ba

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾

Kamar wacce tayi karya takai ta komo tarasa ina zata sa kanta dafa kafad'ar ta akai da han zari ta dago kanta ganin Lubancy ce Kawar ta yasa Zuby sauke ajiyar zuciya tace "kawata kin zo a dai dai dan dama yanzu nike shirin zuwa gidan ku wallahi ina cikin tashin hankali nasan babu Wanda zai fitar dani saike".

"haba ke kuwa kinada ni kike cewa kina cikin tashin hankali kin manta wace ni kin manta kirari na? Bari na na tuna miki".

"a a barshi ban manta ba kai na ne ya kulle na rasa mai yake min dadi, sai yanzu dana ganki na ji sauki a raina nasan ke a wurin ki ba komai bane soboda na shiga matsalar da tafi wannan kuma kin mini maganin ta".

"yauwa yar gari  ashe baki manta da wace ce kike tare da ita ba".

Zuby tace "kawa ta mu zauna na baki labarin abinda ya sa na shiga cikin tashin hankali nan".

Saida Lubancy ta je ta  bude karamin fridge din dake dakin ta dauko goran lemu sannan ta dawo ta zauna a bakin gado tace "ina jinki".

"ina wannan gayen da nike baki labari Wanda na had'u dashi a Instagram kwanaki kin tuna shi?".

"Eh anyi haka na tuna to mai ya faru dashi ko shima an fad'a masa halin ki ne". Lubancy ta fad'a haka tana duban kawar ta

"ko daya kawata nan take Zuby ta kwashe duk abinda ya faru ta fad'a ma Lubancy,

tsaki Lubancy taja kana tace "wallahi Zuby kina bani mamaki d'an karamin abu duk ki bi ki tada hankalin ki ba kin ce   yana soki ba?".

"Eh yana sona na gani a cikin 'kwayar idanun sa".

"kuma kince yarinyar suna kama".

"wallahi suna masifar kama abinda ya bani haushi" da yace" min 'yar mai gadin su ce baki ga yarinyar ba kama da larabawa take yi".

Lubancy tace "dadi na dake gajen hakuri, da kin bisa a yadda  yace idan ma da wata a 'kasa zamuji daka baya, kince kina son sa kuma auren sa zakiyi kin tafka kuskure da kika ce masa karya yake saboda shine gaba dake, amma ko nan gaba ki kiyaye kisan kalar maganar da zaki dunga gaya  masa, Zan san yadda zamu bullo wa lamarin, saboda nima yanzu tawa ce ta kawo ni tun jiya da muke chart kika fad'a min kin gama period naji kamar nayi tsun tsuwa nazo saboda nayi missing d'in ki ".

"Kawata kenan wallahi bakida hakuri". Zuby ta fad'a tana zuge zif d'in rigar ta,

ita ko Lubancy dama doguwar riga ce ta zumbulo sai undies da ta saka nan take ita ma ta cire doguwar rigar tayi cilli da ita ta kamo Zuby suka 'karasa cire ma juna kaya,

sosai Lubancy ta rikice saboda Zuby Allah ya yi mata baiwar komai bata da makusa a halittar  jikin ta shine ke rud'an maza da kuma matan da suke neman junan su

sakonni suka fara aika wa junan su sosai suke romance suna ihu. Babu inda basa tabawa a jikin junan su

Wa'iya zu billah lallai halin Zuby sai ita baza taso Sadeeq ya sani ba dan shi kamilar mace yake so ya aura, ja musu 'kofar nayi ina takaicin rayuwar Zuby

♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾♾ Ina cin danbun ina side yatsun hannu na Ummi na hango tana saukowa daga sama. Dinning din tazo ta zauna da alamar daga bacci ta tashi saboda yadda idanuwan ta sukayi, kallo na tayi tace "maiyar dambu sai kace kin samu wani abun dadin, ko naman kaza baki masa irin wannan santin, ni kuma wallahi na tsane sa dole nike ci nasan Daddy ne yasa Momy tayi dan shima yana son dambu".

Nace "yarinya da kinsan kalan dadin da nike ji alokacin da nike cin dambu da ko magana aka ce ki min bazaki ba saboda idan zan baki amsa a cikin santi zan baki, yanzu dai bari na gama sai ki sake maimaita abinda kika fad'a".

Ummi tace "tab sai na tsaya har sai kin gama kamar yarinyar ki bani da wannan lokacin bari naje ko Indomie na dafa dan yau ba zanci danbun ba".

"ke dai kika sani idan za a shekara ana jera yin dambu babu abinda zai dame ni".

"uhm". Ummi ta fad'a ta nufi hanyar kitchen

Umar ne tafe rike da hannun Jiddah ahankali suka karaso gurin, Umar yai sauri ya ja mata kujera tai saurin dakatar da shi da fad'in "Umar mai kake shirin yi haka to wallahi na daina had'a gurin zama da wannan 'yar kauyen muje falo idan ta gama sai nazo muci".

Kallon ta nayi na kwashe da dariya nace "da alamar har yanzu bakin ki bai mutu ba".

Umar na kalla nace "wai ka nuna mata madubi kuwa? na tabbatar da  taga yadda nayi mata da ko suna na taji an ambata gaban ta ne zai fad'i dan Allah idan bata ga ni ba maza je ka d'auko saboda ina son ta san ruwa ba sa'an kwando bane".

"Aunty Siddeeqah dan Allah ku daina wallahi banajin dadin hakan ko kadan". Umar ya fad'a kamar zai rushe da kuka

ganin haka yasa nace "to shikenan kanina ya wuce amma kaja mata kunne kasan ni duk Wanda yai min kan kara na itace nake masa".

Umar yace "Aunty Jiddah muje".

A masifan ce Jiddah ta kwace hannun ta fuuu ta wuce falo ta zauna tana kananun magan-ganun da ita kadai tasan mai take cewa

🤙 _Hy guys please don't forget to comment vote and follow me on Wattpad join my group on Telegram please please please_ 🥰

NI DA YAYA SADEEQ

˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 21

So sai Siddeeqah take dariya harda rike ciki, tana ayyana yadda zata gyara ma Jiddah zama dan wallahi ta daina daukar rainin hankali

Take Umar ya mara ma Jiddah baya yana mamakin kiyayyar da suka ma juna kamar ba 'yan uwan juna ba

A zaune ya sami Jiddahn a kan kujera sai cika take tana batsewa tana ganin sa ta daure fuska tace "mai kazo yi wuce ka bani guri munafuki ni zaka raina ma hankali a gaba na za ka dunga yiwa waccan yar kyauyen magana? Har da ce mata aunty saboda munafurci na cin ka". Ta karasa maganar tana nuno masa inda nike

shi dai Umar bai ce mata komai ba sai mamaki ma da ta kara bashi

Jin kamar ana hayaniya Momy ta fito da Alamar daga bacci ta tashi, a dai dai lokacin Ummi ta fito daga kitchen hannun ta dauke da plate din abin ci, kallon mu Momy ta shiga yi daya bayan daya, daga karshe ta sauke su akan Jiddah tayi mata kallo irin na gar gadi, ba tare da tace mana komai ba ta koma ciki abin ta

Ummi kuwa zama tai a dinning din tana fadin "wash Allah na".

Kallon ta nayi nace "kefa raguwa ce daga dafa Indomie sai kizo kina wash kamar wacce tayi abin a zo a gani?".

"Bazaki gane bane". Ummi ta fada tana kai lomar Indomie

Shi kuwa Sadeeq tun sanda suka shigo ya haura sama soboda yana bukatar ya huta, dan Zuby ba karamin bata mishi rai tayi ba sosai yake mamakin ta dan shi baya son rashin kunya musamman ma idan yasan ya girmi mutum, to yana so a girma ma shi, a gogan hannun sa ya cire tare da lalubar aljihun sa ya ciro wayar sa ya aje a kan madubi kana ya shiga cire kayan jikin sa, wannan ita ce dabi'ar Sadeeq a duk sanda zai shiga wanka sai ya fara cire kayan sa a bedroom sannan ya ke shiga bayi, to bayan ya shiga ya dauki kusan mintuna 43 a cikin bayin yana cuda jikin sa ya zuba wancan ya zuba wannan sai da yaji kam shin ya mishi yadda yake so, sannan ya fito daga cikin kwamin wankan ya zo gurin da tawul yake a rataye ya daura a kugun sa kana ya dauki karami ya shiga goge kansa daga haka ya fito.

* * * * * * * A ban garan su Zuby kuwa bayan sun gama fasikan cin su suka shiga wanka nan ma sai da suka bata mintoci suna kissing din juna kamar wasu mata da miji Zuby ta manta da wani Hallita mai suna Sadeeq saboda Lubancy ba baya ba wajen romance ta iya solon makirci da Jan hankali kala-kala.

Bayan sun fito daga wankan ne suka shafa mayuka masu kam shi tare da fesa body sprea riga da wando Zuby ta dauko a cikin durowar ta kana ta duby Lubancy tace "sweety wani kalar kaya zan fiddo miki?".

"My love duk wanda kika dauko min zan sa". Lubancy ta fada cikin salo mai Jan hankali

To bayan sun gama shiryawa suka shiga fesa turaruka masu sanyin kamshi gami da daukar hankalin wanda duk a ka gibta ta kusa dashi.

Hijabi suka zum bula har kasa tare da saka safa a kafar su ke idan ki ka gansu zaki rantse mutanen arziki ne.

Falo suka fito inda suka tarar da Mama zaune tana kallon BBC World news, ta maida gabadaya hankalin ta da nutsuwar ta akai

Kamshin turaran tilon diyar ne ya dawo da ita ga barin kallon TV,

kallon su tayi cikin sakin fuska tace "kar dai har zaki tafi?". Mama ta fada tana duban Lubancy wacce ke tsaye tana dan Murmushin tace "Eh Mama zan tafi dama sako na kawo mata".

Kallon Zuby Mama tayi ta ce "iya rigima ina zuwa kuma? ko rakiya zaki mata".

"Eh mama". Zuby ta bata amsa a takaice

To babu damuwa ki dawo Lafiya amma gaskiya yau kar ki dade kin San Abban ki yana gari, motsi kadan yace "kina ina?". Sai dai nayi masa karyan kan ki na miki ciwo kina bacci kin kuma ce kar a tashe ki har sai kin tashi, fek kiss Zuby ta mannawa Mama a goshi tana fadin "Allah ya bar min ke Mama na I love you". "Love you too". Mama ta fada tana dariya irin ta-su ta manya da yike ita ma irin gogag-gun iyayan nan ne, kuma ta san da duk wani abu da diyar ta-ta take aika wa asali ma ita ce ta sata akan hanyar

* * * * * * * * To a bangaren Sadeeq kwance yake a kan makekyan gadon sa idon shi a rufe kamar mai bacci amma kuma ba bacci yake ba a duniyar tunani yake.

Wayar sa ce ta shiga ringing amma be da niyar dauka har kiran ya katse saida a ka sake kira a koro na biyu ya bude raunan-nun idanun shi ya lalabi wayar ganin sunan Farooq na yawo akan screen d'in wayar ya danna picking kana ya kara a kunne

daga can ban-garen Farooq yace "kai bana son iya shege tun dazun nike kiran ka baka dauka ba, ba yan kasan haka kawai ba zan dunga kiran ka ba".

"Ina jin ka to". Sadeeq ya fad'a yana cin magani

Farooq ya kwashe da dariya yace "dan iska wannan ji da kan naka ba shi zai sa a dunga maka abinda ka ke so ba, ni dai kasan ba tsoran ka zan ji ba ko?".

Cikin jin haushin kalaman Farooq Sadeeq yace "malam ya i she ka haka ka fadi abinda ya kawo ka ina jin ka".

Farooq yace "akan maganar makarantar matar ka ne na gama magana da wannan abokin nawa da yake koyar wa a makarantar ya sama mata admission yace maganar aji sai idan an kaita sun mata interview zasu gane ajin daya dace da ita, saboda haka daga yau zuwa kowace rana zaku iya kaita dan har register yai mata ".

Shiru Farooq yayi ko Sadeeq din zai ce wani abu amma sai yaji a kasin haka,

Bayan wasu yan daki ku Sadeeq yace "ka gama?".

Cikin takai cin abokin nasa Farooq yace "dan iska insha Allah wannan yarinyar da ka ke rainawa sai ta zame maka ciwan ido, yana gama fad'ar haka ya kashe wayar sa

Aje wayar sadeeq yayi gami da daga kafada alamar ko in kula ya tabe baki a can cikin zuciyar sa yana jin dadin zai rabu da ala ka kai

NI DA YAYA SADEEQ

˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 22

To bayan fitar su Zuby gidan su Lubancy suka zarce dake wata unguwa amma unguwar ba ta masu kudi can bace, kuma ita Lubancy iyayan ta sun rasu tun tana yar karama, a gurin kawun ta take, kasancewar sa namiji ba ko da yaushe yake gida ba shiya yasa Lubancy ta zama abar da ta zama yanzu duk da matar kawun na kokari amma sam Lubancy ta raina ta bata jin maganar ta, ganin Allah bai bata haihuwa ba kar ta cika matsawa ace dan bata son zafin yara bane shiyasa ma yanzu ta zuba mata idanu, in dai duniya ce wanda bai zo ba ma jiran shi take.

Duk da sun sami matar kawun a tsakar gida, haka su ka wuce ta ba tare da sunyi mata sallama ba, da shigar su dakin Lubancyn suka wuce suna wani  shan kamshi.

A cikin zuciyar ta take musu adduar shiriya dan baza tayi musu mugun fata ba kuma Allah na gani tayi iya bakin kokarin ta dan ta san abin da suke aikata wa ba abin arziki bane, ta bar ma Allah saboda duk zagin da mutanen unguwa suke mata yana dawowa kunne ta a cewar su "dan ba yarinyar ta bace shiyasa ta barta tana yin abin da ta ga dama". Amma ita ta san d'a a wannan zamanin ko kai ka haife shi sai kayi hakuri da shi.

* * * * * * * * * To bayan sallar isha'i ne Daddy ya ce wa Momy "ta je ta kira masa yaran gidan zai yi magana dasu". Ba tare da tayi musu ba ta ce mai "to".

Falo ta fito in da ta kwalama Suwaiba mai aiki kira, nan take suwaiba ta zo tace "na'am". Momy tace "haura sama ki kira min yaran nan, ki tabbatar kin fada ma ko waccen su".

"To Hajiya". Suwaiba ta fada kana ta haura sama

Dakin Khadija ta fara zuwa in da ta shiga buka kofa  bata wani bata lokaci ba Khadijan ta zo ta bude kofar ganin Suwaiba tsaye tace "Suwaiba lafiya?".

Suwaiba tace "lafiya lau Hajiya ce tace "tana son ganin ku".

To kice "gamu nan".

Da "to". Suwaiba ta amsa

sai da tabi duka d'akunan yan matan ta sanar musu, sannan ta sauko kasa inda ta tarar da Momyn inda ta bar ta take ta shaida mata gasu nan zuwa kana ta koma bakin aikin ta.

Ku san a tare Siddeeqah da Khadeeja suka sauko dan sun ruga kowa fito wa a lokacin falon babu kowa sai TV da yake a kunne yana karatun Al'qur'ani mai girma

Kusan tare suka zauna kan kujera kowa da abinda yake sakawa cikin ran sa, can dai Khadija tace "sister yau ba magana ne?".

Ita Siddeeqah ba rufi ne da ita ba saboda haka ta mayar wa da Khadija amsar ta da cewa "yo gani nayi kina wani share ni nayi tunanin kina shigar ma Jiddah ne shiyasa ki ka ga ban kula ki ba, saboda na yarda na bata da kowa a gidan nan in dai akan kwatar yanci na ne".

Bata karasa maganar ba Jidda ta fito ganin Siddeeqah a zaune yasa ta ja dogon tsaki ta ce "sis Khadee me yisa ki ka zauna tare da wannan yar kauyen".

Khadija tace "wa fa?".

Nuna ni tayi da yatsa ba tare da ta jiwo ta kalle ni ba,

ganin haka yasa na mike cikin masifa na kama hannun nasa abaki na ganna mata cizo kana na koma gurin zama na kamar ba ni nayi ba.

ai kuwa ta shiga yin kuru-ruwa wanda yai sanadin fitowar su Daddy, Ummi ma da take sama ta ji ihun cikin sauri ta sauko har ta kusan tayi tun tube saboda ko gaban ta bata kalla ba.

Kafin su Daddy su ce wani abu yah Sadeeq ya shigo bakin sa dauke da sallama amma saboda ihun da Jiddah take yi babu wanda yaji sallamar.

Da mamaki dauke a fuskar Sadeeq ya kara so cikin falon ya ma rasa wa zai tambaya abin da ya faru saboda haka ya jingina da bango ya harde hannayen sa waje guda

* * * * * * * * * Bayan shigar su Zuby dakin Lubancy ta maida kofar dakin ta rufe da mukulli, kusan zan iya cewa Lubancy bata gajiya da da romance saboda haka ta shiga shafa jikin Zuby take ita ma tsigar jikin ta ya fara tashi nan take suka shiga cire ma juna kaya bayan sun gama suka fada kan katifar Lubancy suna nishi sama sama take suka fara tsotse-tsotsan juna suna fada ma juna kalamai masu dad'i.

Wa iya zu billah Allah ka shirya mu kashir ya zuri'ar musulmai baki daya

* * * * * * * * * * Sam sadeeq bai son hayaniya ganin Jiddah bata da niyar yin shiru ya daka mata tsawa, nan take tayi tsit kamar ruwa ya ci ta sai shash-sheka da take yi a kai a kai, sai a lokacin Daddy ya nemu guri ya zauna kana Momy ta zauna ita ma.

Da hannu Daddy ya nuna ma Sadeeq din Kujera alamar ya zauna babu musu ya zauna, an dauki kusan mintuna hudu babu wanda yai magana can dai Daddy yai gyaran murya yace ma Jiddah "ke! Tashi ki zauna". Saboda a lokacin Jiddah a duke take kan ta a kasa tana shash-shekarar kuka.

Ita ma babu musu ta nemi kan Kujera ta zauna kusa da Ummi sai murza idanuwa take yi.

Bayan ta zauna Daddy yace kafin na fara cewa komai "ku tashi muje muyi dinner".

Gunin sha'awa zaune suke reras a kan dinning din ba ka jin sautin kowa sai karan cokula saboda Momy ce tayi girkin abincin ba karamin Daddy yayi ba jalof din taliya ce da kuma farfesun kaza ga farfesun kifi ga kuskus haka ban garen drink ta hada jus kala-kala dan Momy ba baya ba wajen iya abin ci.

Ina cikin ci Inna ta fado min a rai saboda haka na ijiye cokalin nayi tagumi kwalla na zubo min, Daddy ne ya lura da halin da nike ciki yace "A a mai gaskiya mai kuma aka miki?".

Cikin kuka nace "Daddy Inna na tuna tun nazo banyi magana da ita ba".

Yace "ai ba kuka zaki ba ko Sadeeq ki ka ce ma kina son magana da ita zai kira miki it maza daina kuka bari mu kammala cin abinci sai a kira miki ita ko".

Ya karasa maganar cikin sigar lallashi nace "to Daddy

 

* * * * * My Fan's Please ku cigaba da bani hadin kai saboda shine karfin gwuiwa ta

Dan Allah Wanda beyi following dina ba dan Allah kuyi yanzu sannan ku cigaba da danna min vote kuna aje min comment please show me love 💞❤️

NI DA YAYA SADEEQ

˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 23

 

   Cigaba da cin abincin nayi ina jin dadi har cikin raina yau zanyi waya da inna, saboda zumudi ban wani koshi ba na mike daga kan dinning din

Momy tace min "ina zuwa?".

Naba ta amsa da "na koshi ne".

Bayan na wanko hannu na falo nazo na zauna ina sake sake a raina

can shima yaya Sadeeq ya zo ya zauna, na kalle shi muka hada ido ya banka min harara nima na rama.

Yace "ke da ni ki ke?".

Nace "nima dani kake?".

Ganin ya taso nasan bugu na zaiyi na mike da gudu na nufi dinning ina kiran sunan Momy, ban kai ga karasa wa ba nayi kicibus da ita, da alamar ta tsorata da yadda nike kwala mata kira tace "ke lafiyan ki?". Da hannu nike nuna mata Sadeeq da saura kiris ya damko ni Allah ya kawo ta.

Sai a lokacin ta lura a tsaye yake sai mazurai yake na rashin gaskiya.

Momy tace "Sadeeq Sadeeq wai sai yaushe zaka girma? To idan ka dake ta me zaka ji?".

Yace "Allah Momy rashin...".

Cikin sauri Momy ta katse sa da fadin "ban tambayeka ba Sadeeq ba tun yau ba nasan halin ka idan aka bibiya kai ne ka fara".

Daddy ne ya zo gurin da muke yace "kai dai Sadeeq anyi katon banza abin kunya ka tsaya kana biye ma karamar yarinya sai kayi ai tunda kaima irin ta ne baka da hankali, ku wuce mu koma falo".

Ya fad'a yana nuna mana hanya Momy ce ta fara yin gaba Daddy yabi bayan ta, ganin da gani sai yaya na kalle sa karaf muka hada ido ya galla min harara madadin na rama sai na kwashe da dariya ina yi mai gwalo nace "anji kunya giwa tana fada da shawo inba ga tsoro ba...".

Ban karasa maganar ba ya damko ni ya toshe min baki ya tsats-tsare ni da idanu yace "ke dan uban ki yaushe zaki hankali dan kinga su Daddy na shigar miki shine zaki min rashin kunya dama na dade ina neman wannan damar gashi yanzu na samu zan ragar gaji bakin yarinya".

Tuni ido na ya raina fata gashi ya toshe min baki bare na basa hakuri

Ana haka sai ga Daddy ya zo wuce wa ganin Sadeeq matse da baki na yasa shi mamaki dan takai ci bai ce masa komai ba illa  da yace "bani guri na wuce".

Kunya ce ta kama Sadeeq yana sosa keya ya sake ni kana ya matsa a hanya Daddy ya wuce ni kuwa ina ganin Daddy ya wuce na falla da gudu ina haki kamar wacce tayi gudun fan falaki

Momy tace "keda wa kuma? A ina ki ka tsaya bayan mun taho?".

Sai da na zauna akan kujerar da ke kallon ta nace "kedai Momy ki bari kawai kuna wuto wa ya damko ni ya shake min yuwa tare da toshe min baki, yanzu haka bacin Allah ya kawo Daddy da kashi na ya bushe".

Momy tace "Sadeeq din?".

Nace "kwarai kuwa".

Zatayi magana kenan ya shigo yana dan sosa keya tace "ka kyauta ka nuna bamu isa da kai ba".

Zai yi magana tace "za kai shuru ko sai na saba maka".

Bai kuma magana ba ya nai mi guri ya zauna,

bai jima da zama ba sai ga Khadija da Ummi nan bayan wasu yan daki ku Daddy ya dawo hannun sa rike da na Umar can sai ga jidda nan ita ma fuskar nan tata a kwabe kollo daya nayi mata na kawar da kaina saboda dariya na so ta kama ni zokai zokai tazo ta zauna a kan kujera.

*  * * * * * * * * *

Aban garen zuby kuwa bayan sun gama sheke ayar su, wanka suka kuma yi a gurguje kana suka fito kasan cewar a kwai taron da suke zuwa duk karshen mako, toro ne da manyan mata yan madugo suke sheke ayarsu,

sun shirya tsaf cikin wata doguwar riga yar kanti daga kasan ta a yanke yake haka saman ta shara shara yake kuma hannun bes ne da ita yanayin rigar iri daya ce suka sa, sai dai kowa da kalar tasa,

Wani katon hijabi suka maka akan yar iskar shigan nan tasu dan ko undies basu saka ba kuma dama idan zasu taron ba a saka undies kashe wayoyin su suka yi kana suka daura nikab suka fito lubancy ta rufe kofar ta, alokacin tsakar gidan ba kowa

Sadaf Sadaf suka fice daga gidan dama kafin nan sunyi waya da drivern da yake kaisu duk karshen mako

Sun kuma ci sa'a suna fitowa yana karasowa ba su wani tsaya bata lokaci ba suka hau yaja su,

Bayan doguwar tafiyar da sukayi yayi fakin a dai dai get din wani gida mai girman gaske suka fito yaja motar sa yayi gaba saboda ya saba yana kawo su kuma duk karshen wata suna biyan sa kudin sa dan haka suka tsara dashi,

duk da bai san me suke aikata wa ba amma yana kyauta ta zaton ba alkairi bane,

Saboda tsaro ko mai gadi ma mace ce tsohuwar soja saboda basa son harka da maza sam

Bayan sun kwan kwasa an buda musu suka shiga, gida ne mai girman gaske an kawata sa da ado irin na zamani sai da suka wuce gat biyu sannan suka samu inda ake toron mata ne a zazzaune sun kai su tala tin ko wacce ka gani ba shigar ar zi a tare da ita,

Basu karasa inda matan suke ba sai da suka cire nikab da hijabin, suka tura cikin jaga dama ta kalmi mai tsini zuby ta saka take ta shiga tafiya tana gir giza ba bu abinda bai motsawa a jikin ta, gaba daya hankulan matan ya dawo kanta a ka shiga tafa mata ana kiran sunan ta ana wasa ta kana ta sami kujera ta zauna lubancy tabiyo bayan ta

Sai da aka fara gabar da abinci suka ci suka sha tare da kayan marmari iri iri da madara, bayan sun gama babbar cikin su mai suna Hajiya Turai ta tashi tana kwar kwasa shigar jikin ta bata da maraba da tsira ra

* * * * * * * * *

Please and please follow Comment Vote

NI DA YAYA SADEEQ

˙·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 24

Sai faman yauki take kamar kal kashi bata da tsayi kuma tana da dan jiki taci uban bilicin kan wani dakali ta hau tace "madugo!!". suka ce "mu ne". "madudo". "Mu ne!!!".

Ta cigaba da cewa "ba tare da bata lokaci ba kamar yadda muka saba ako wani mako, yau ma hakan take a matsayi na na shugabar wannan kungiya ina mai kara farin cikin sanar daku yau ma akwai shagali dan munyi manyan kamu".

Raf Raf Raf suka dunga tafa mata ana ihu

Haka dai masu mukami a cikin kungiyar su kai ta futowa cikin shigar da bata da maraba da tsirara suna bayani kana su koma su zau na

A karshe dai kowa ya tashi suka yi layi kana wata Hajiya Tubulas tace "bari naje na kira manyan matan su zo su zabe ku dare na yi

ta wata hanya ta bi bata jima ba sai gata da wasu mata datti jawa da ganin su matan manya ne dan fatar su luwai luwai sai sheki take yi suma ba wata suturar arziki suka sa ba, bayan sun iso, Hajiya turai ta ce "to kun dai gansu nan gogaggu ne a harkar ba abin da basu iya ba ku koma gefe zan dunga kiran su daya bayan daya duk wacce taga wacce tayi mata sai tayi magana amma ko waccen ku baza ta zaba su wuce biyar ba".

Take gurin ya kaure da ihu aka hau tafi Raf Raf Raf

* * * * * * * * * *

Daddy yai gyaran murya yace "Alhamdu lillah ina mai kara jad-dada godiya ta ga Allah ma daukakin sarki daya a ramin lokaci domin na kara tuna tar daku dan gane da wasu abububuwa da na lura suna faruwa a gidan nan,

Ya kalli Momy yace "ko kina da abin fada?".

Tace "bani da shi".

Yace "to madallah

yace to kai Sadeeq "Momyn ku tazo min da batun wai ka sama ma Matar ka makarantar kwana haka a kayi?".

Ya karasa maganar yana kallon Sadeeq

Kamar da gaske Sadeeq yace "wallahi Daddy saboda na temaka mata ne, nayi tunani naga idan anan ne ba lallai ta maida hankali tayi karatun kirki ba amma acan idan bata ganin idan wanda ta sani sai ta fi maida hankali".

Cikin gamsuwa da maganar Sadeeq Daddy yace "idan hakane kayi abu mai kyau, yaushe ne, zaka kai ta?".

Yace "gobe ne daddy dan na gama shirya mata komai".

"Ka kyauta Allah yayi albarka haka ake so".

"Ameen ameen Daddy". Sadeeq ya ce

In banda faduwa ba abin da gabana yake yi sai na rasa me ke min dadi yanzu gobe wannan mugun zai raba ni da farin ciki na sosai nike jin kuna a raina nayi narai narai da ido ban san sanda kwalla ta fara zubo min ba

Momy ta kalle ni tace "kiyakuri ki daina kuka ki kaddara tun kafin Allah ya halicce ki ya tsara miki yadda rayuwar ki zata kasan ce, ba kuka zaki ba godewa Allah zaki da ki ka samu masu tsaya miki akan karatun ki dan wallahi wasu irin wannan damar suke so amma basu samu ba insha Allah zaki ga amfani karatun nan gaba".

Naji dadin nasihar da Momy tai min saboda a rayuwa ta ina son nasiha kuma ina dauka sosai hawaye na na share nace "to Momy insha Allah zan jure".

Daddy ya cigaba da cewa "na dawo kan ku, ke Jiddah". Ta dago kai ta kalle sa yace "da ke kuma Siddeeqah, bana son tone tone ba tun yau ba ina lura daku a cikin gidan nan bakwa ga maciji, idan nayi magana wa Momyn ku sai tace min ba haka ba, amma wa'innan abu buwan da suka dunga faruwa a yan kwana kin nan yasa naji babu dadi, kuna yan kana nun ku daku kun iya fada har haka, a gaban mu kenan fa muna da rai, to idan kasa ta lullube fuskokin mu ya kenan? Ku saurara da kyau ku jini bana son na kara ganin irin haka a gidan nan ko naji labari zanyi mummunan saba muku kun ji ni?".

Ya karasa maganar cikin kausasa harshe.

Nace "to Daddy insha Allah haka bazai sake faruwa ba"

Ita ma Jiddah tace haka

yace "ku tashi ku yafi junan ku kuyi ma junan ku sallama saboda Allah ya la'anci mai tada fitina".

Yi mukai kamar ba muji abin da yace mana ba

yaya Sadeeq da mun gama kai shi ban go ya taso da zafin sa zai dake mu Daddy yai saurin hana shi

Yace "ka bisu a hankali yara ne nasiha zaka musu yanzu sai suga muna takura musu ne".

Ba dan ran Sadeeq yaso ba ya koma ya zauna

Nasiha daddy ya fara yi mana mai ratsa zuciya yana kara tunatar damu duniyar nan ba komai bace kuma duk mai yanke zumunta ba zai shiga Aljanna ba haka dai yai ta tuna tar damu! jiki na yayi sanyi matuka na gamsu da duk abunda ya fad'a saboda haka na mika ma Jiddah hannu babu yabo ba fallasa ta miko min mukayi musabaha

So sai Daddy yaji dadi dan ya nuna farin cikin sa yai ta samana Albarka

Khadija na zun buro baki tace "wai ni da Umar me mukayi? Daddy baka sa mana Albarka ba".

Murmushi Daddy yai irin nasu na manya kana yace "ai ban ware ba Khadeeja Allah yai muku albarka gabaki dayan ku".

Khadija na Dariya tace "amin Daddy".

Fira muka shiga ta ba wa ina basu labarin kauye ana kwasar dariya can dana tuna banyi waya da inna ba nace "yaya".

Bai dago ya kalle ni ba dan hankalin sa akan waya yake

Momy tace "baka ji ana magana ba?".

Sai alokacin yadago kai yace "lah wallahi Momy banji ba me tace".

Tace "yo kace bakaji ba taya kasan ita tayi magana? Allah ya shirya ka Sadeeq".

Siddeeqah tace "dama Momy so nike ya kira min Inna".

Yace "Inna tayi bacci yanzu ki bari sai gobe idan Allah ya kaimu kan ki tafi zan kira miki ita ki mata sallama".

Murya ta a dakile nace "to".

Yace "Momy na manta ban fada muku ba nima gobe zan koma kaduna ana nema na a office din mu".

* * * * * * * * * Dan Allah kuya kuri da jina da kukai shiru kwana biyu

Ku cigaba da yimin comment da vote please

Kuyi following dina 💞

NI DA YAYA SADEEQ

·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 25

      Momy ta ce "amma sai ka kai Siddeeqah makaranta ko?".

Ya ce "bani ne zan kaita ba Farooq ne zai kaita ni da safe ma  zan wuce".

Sai alokacin Daddy yai magana ya ce "yau na kara tabbatar da rashin hankalin ka, matar taka ta sunna zaka bari wani kato ya dauke ta a mota, yayi tafiya mai nisa da ita? Tun wuri ka canza tunani wannan sakarci ne".

Daddy na gama fadar haka ya mike ya nufi bedroom.

Momy ma ta ce "Sadeeq ma kare maganar da safe zan bi bayan Daddyn ku".

Ba dan ran Sadeeq yaso ba ya ce "Allah ya tashe mu lafiya". saboda yaso su gama magana tun yanzu, dan shi har cikin zuciyar sa ba zai kai ta ba

* ** * * * * * * * *

A ban garen Zuby kuwa suna ta sheke ayarsu inda wa'innan manyan matan suka zabi wa'inda sukai musu kana suka shiga wani daki mai girman gaske yana dauke da manyan katifu masu laushi an lailaye su da zannuwan gado masu kyau da tsari

Ko wace mace mata biyar ne a kanta biyu suna wasa da dukiyar fulanin ta yayin da biyu suke kasan ta suna wasa da HQ din ta daya tana sunmbatar ilahirin jikin ta

Baka jin karar komai sai sautin kukan dadi da suke yi

*** * * * * * * * * *

Jiddah ta ce "Sis Khadee ni na tafi na kwanta sai da safe".

Ta ce mata "Allah ya tashe mu lafiya".

Daga nan da zata wuce ta murje min yatsa Allah yaso Umar da yaya Sadeeq sun lura da ita

Aikuwa na taso na ingije ta ji ka ke kum alamar ta bugu da wani abun, koda na jiyo ina huci sai naga da teburi ne ta buge goshi

Kafin ta kwallara kara yaya yai sauri ya toshe mata baki, kana ya ce "wai ku wa'inna irin yara ne? Kwata kwata ba kwa son zaman lafiya yadda kasan kuna ganin hanjin juna, da ina dauka waccan ce mara gaskiya". Ya fadi haka ne yayin da ya nuno ni da yatsa, ya cigaba da cewa "ashe kema da naki laifin, kin dai san halin waccen yarinyar bata barin sai ta kwana ki kula yar daba ce ko a kauye tsoran ta ake".

Kallo ni yai muka hada ido da shi  na galla masa harara na ce " aikin banza idan kura na maganin zawo ta fara yi ma kanta".

A ransa yake mamakin irin karfin hali na, wani lokacin ina burgesa yadda nike nuna bana tsoran sa bare nayi shakkar sa bai kuma tanka min ba

Har yanzu toshe yake da bakin Jiddah sai numfar fashi take kamar wata marar lafiyar da take jin jiki

Ummi ce tace "ni dai bacci nake ji sai da safen ku".

Da dayan hannun sa ya daga ta cak ya kai ta dakin ta, saboda baya son su Momy su san abinda yake faruwa

Khadeeja da bata ga komai ba Umar ta tambaya ya shiga labar ta mata abinda ya faru

Dogon tsaki taja kana ta haura sama tana jin babu dadi ita wallahi ta gaji da wannan abin da suke yi sam bata son hayaniya

Kan kujera Siddeeqah ta koma ta  kwanta tana fadin "wash wallahi Umar na gaji".

Kusa da ita ya matso yace "wai Aunty Siddeeqah na tambaye ki mana".

"Ina jin ka Umar".

"wai wani abun ki ka ci ki ka zama mai karfi? Ko kina training ne?".

Sai da na kal kyale da dariya nace "meye kuma training? Ban san sa ba bare nayi, kuma ba wani abu da nike ci, kawai ni bana son rainin wayau nasan inada tsokana amma Jiddah ita take tsokana ta, ba ni ce ke tsokanar ta ba".

Ya ce "hakane Aunty Siddeeqah amma dan Allah ki dunga hakuri".

To kawai nace masa saboda naga zai raina min hankali wai na dunga hakuri caf sai dai idan bata taba ni ba amma maganar hakuri bata taso ba

Nace dan zo ka danna min kafa ta "

To yace yayin da yazo ya fara danna min ahaka har bacci ya kwashe ni ban san lokacin da Umar ya tafi ba

*** * * * * * * * * *

Sai gurin karfe dayan dare komai ya lafa a wurin su Zuby wanka sukai ta shiga sai ka samu mata gurin  hudu a cikin bayi saboda bayin da dan girman sa babu laifi, har da Zuby a cikin wa'inda su kai wankan saboda haka ta fara kin tsawa cikin sauri ta maida kayan ta

gaba daya hankalin ta ya koma gida saboda tasan yanzu haka hankalin Abban ta ba akwan ce yake ba gashi ta kashe wayar ta bare ta kira Mama a waya ta tambaye ta halin da ake ciki

Tsaki taja a fili ta ce "shiyasa wallahi bana son zaman da Abba yake a gida saboda kwata kwata bana sakewa".

Kafad'ar ta taji an dafa cikin sauri ta dago da yan kananun idanuwan ta ta sauke su kan  wata yarinya da  ganin ta bazata wuce 18 years old a duniya ba

"Hy".

"Hello".

Suna na Sumayya amma ana kira na da Sumy Zuby ta ce "nice name".

Sumy ta ce "ko zaki bani number ki".

Sai a lokacin Zuby ta kare ma Sumy kallo yarinya ce karama kirjin ta a cike yake kuma itama babu laifi akwai mazaunai, Kamar wata mayya Zuby ta lashi la'b'ban ta tace "amma dai baki dade da shigowa cikin wannan kungiyar ba ko? Saboda naga babu ke  a cikin group d'in kungiya ta karasa maganar cikin salon yanga

Sumy ta ce "eh yau ne na fara Zuwa hajiya Tubalas ce ta kawo ni".

"Yauwa Koda naji saboda a wannan kungiyar tamu kowa ya San kowa". Zuby ta fada tana kara gyara bra din ta.

* ** * * * * * * * Acan daki Sadeeq ne kwance sai juyi yake ya kasa bacci saboda ciwan marar daya taso shi gaba, da kyar ya iya furta "Allahumma Lah sahla Illah ma ja'altuhu sah'lah wa'anta ta'ja'aulul huznah iza shi'itah sah lah''. 

Sosai cikin ya cigaba da murda mai ganin juyi a daki shi kadai ba shine mafita ba yasa ya mike cikin karfin hali ya fara bin ban go idan cikin ya murda mai sai ya tsugunna idan ya lafa ya cigaba a haka ya sauko step din bai lura da Siddeeqah da take bacci a falo ba gabad'aya siket din jikin ta ya tattare guri daya sai fararen siraran cinyoyin ta da suka baiyana gunin ban sha'awa

Bayan ya shiga kitchen din durowoyi yay ta budewa har Allah ya bashi sa'a yaci karo da abin da yake nema, take ya dauki kofi yajika kanwar bai tsaya wata wata ba ya kafa baki yana gama shanyewa ya jefar da kofin, take cikin sa ya fara hautsinawa, amai ya fara taso mai anan kitchen din ya tsugunna yai ta kyalayawa kamar hanjin cikin sa zai fita

bayan ya gama yaji cikin nasa ya lafa masa cikin juriya ya mike hannun sa akan marar sa ya fito

Sai alokacin ya lura da Yar matar sa kwance duk ta takure guri daya

Abu buwa da dama zuciyar sa ta fara raya masa akan ta

Saboda haka ya matso kusa da ita ya zauna kan kujerar

Cinyoyin ta ya kura ma ido sai ya kai hannu ya taba sai ya janye.

Ramadan kareem✨ 🌙                  Ramadan kareem ✨🌙         Ramadan kareem ✨🌙

Ina fatan kowa yana cikin koshin lfy ya Azumi Allah ya karbu ibadun mu 🙏

NI DA YAYA SADEEQ

·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 26

       ___Ya dauki tsayin lokaci a haka yana kallon tsala tsala cinyo yin nata, daka bisani ya mike yana mai jin haushin kansa ko me yagani a jikin wannan kwailar yarinyar? Haka ya tambayi kanshi ganin bashida amsa yaja dogon tsaki "mtssww" duk abinda Sadeeq yake yi Siddeeqah bata san inda kanta yake ba.

Izuwa lokacin cikin nasa yai masa sauki sosai sai dan abinda ba a rasa ba

Dukan kafar ta ya shiga yi kamar a mafarki taji ana bugun ta a tsorace ta bude ido ganin Sadeeq ne yasa ta dan ji sanyi a ranta

Dube dube ta fara sai alokacin ta tuna ashe a falo ta kwanta, dirowa tayi daga kan kujerar ta wangale baki tayi hamma Sadeeq harda toshe hanci yayi saboda da tayi hammar bata kare bakin ta ba wai kada yaji wari,  tayi mamakin ganin sa amma sai bata nuna nasa ba ta bige da cewa "wash".

A yatsine Sadeeq ya dube ta wallahi shi har cikin zuciyar sa ya tsane ta mtwssss ya kuma Jan tsaki a karo na biyu, afili yace "wallahi Daddy bai kyauta min ba daya aura min yarinyar nan"

Duban sa itama tayi tace "aikin banza wai harara a duhu, kaje ka fada masa man".

Bata karasa fada a gaban sa ba ta ruga da gudu saboda tasan duka ne zai biyo baya, ta ko yi sa'a dakin Ummin abude yake tana fadawa ta maida kofar ta rufe kana ta fara maida numfashi daka bisani tabi lafiyar gado.

Da takaicin ta Sadeeq ya mike Ko kadan babu laka a jikin sa  ahankali ya ke tafiya har ya haura sama ya shiga makwancin sa

*** * * * * * * * *

Bayan ta gama gyara bra dinta ta dubi Sumy tace "dan zuge min zif din". Da "to". Sumy ta amsa kana ta zuge mata kamar yadda ta bukata.

Basu jima ba sai ga Lubancy ta zo, tana ganin Zuby tare da Sumy tayi kicin-kicin da rai, sarai Zuby ta gane nufin Lubancy amma sai ta basar tace "yauwa dama tun dazu ke nike jira muje ko".

Ba tare da Lubancy ta tanka mata ba tayi gaba asakarce Zuby ta bi bayan Lubancy da kallo kana ta maida kallon ta ga Sumy tace "am mata mu mun tafi sai idan mun hadu wani satin".

Sumy ta ce "to".

Koda suka fito bakin get din sun tarar da Zuly na jiransu amoto saboda haka basu wani tsaya bata lokaci ba suka shiga Zuly tajasu suka dau hanya

Tafiya suke babu mai kula dan uwan sa Zuby aka fara saukewa saboda unguwar tasu tafi kusa, kana tayi musu sallama ko da tazo bakin get din ta rasa ya zatayi saboda tasan mai gadi yanzu bacci yake yi, can ta sauke ajiyar zuciya da sauri ta fiddo wayar ta daga cikin jakar ta number Mama ta shiga laluba Mama dake safa da marwa a dakin ta taji ringing din wayar ta da sauri taje ta dauko kana ta duba screen d'in saboda taga wace me neman nata.

Ganin sunan shalelen nayawo akai yasa Mama tai saurin dagawa gami da karawa a kunne, daga can bangaren Zuby tace "Mama a bude min kofa". Daga haka ta kashe wayar bata dade ba sai ga Maman tazo ta bude mata, tana shiga Mama ta maida get  din ta tura ahankali Zuby zatai magana Mama tai sauri ta tashe mata baki tun kan su karasa falon Zuby ta cire nikabin fuskar ta cikin sanda suka wuce falon basu zarce  ko ina ba sai dakin Zuby kana Mama ta maida kofa ta rufe, Masifa Mama ta shiga zazzagawa inda sabo Zuby ta saba saboda indai Abba nanan to fa haka Mama ke yi sai da ta gama kana Zuby ta dubi Mama tace "haba Mama wai meyisa ki ke min irin wannan ne? Ni gaskiya bana so ki sani a gaba ki tai min masifa sai kace yarinya karama".

Dafa kafad'ar Zuby tai tace "kin dai san halin Abban ki duk da nace kin ce kar atashe ki nan yai ta zuwa yana buga kofar ki yana ambatar sunan ki yanzu haka nasan idon sa biyu dan sanda na baro sa yana bayi dan ya dauro alwala maza canza kayan ki ki kwanta zanje na ce masa kin tashi".

Mama na gama fadar haka ta fice daga dakin, a gag-gauce Zuby ta canza kayan kana ta kwanta ta rufu da bargo kamar mara lafiya

Ko da Abba ya shigo tambayar ta yashiga yi me ke damun ta kin sha magani? Haka dai yai ta mata tambayoyi yace "ko na kira miki Dr khamis ne?". Tace "a a Abba". Yace "to ya jikin naki". Kamar mara lafiyar gaske yadda ta marairai ce fuska tace "Abba da sauki sosai fa". "Allah ya kara sauki amma baki fada min meke damun ki ba". Tace "wallahi Abba ciwan kai ne mai tsanani ga jiri da nike gani shiyasa dana sha magani na kwanta nace kar a tada ni". Kan nata ya taba babu wani zafi yana Murmushi yace "Alhamdu lillah kan da sauki tunda gashi jikin naki babu zafi". Tace "Eh Abba". Mama ce ta shigo hannun ta dauke da karamin kofi akan wani dan karamin tebur ta ijiye kana ta zo ta dan yaye bargon Zuby tace "daure ki tashi ki kurba shayi ne nayi miki irin wanda kike so". Abba yace "ai kuwa kin kyauta Mariya miko min na bata". Da jin  haka Zuby ta dan yunkura ta mike tana dan ciza leben ta na kasa tace "Abba zan sha da kaina  a miko min". Abba bai baro dakin ba sai da ya tabbatar da lafiyar diyar sa.

* ** * * * * * * * * *

Washe gari da misalin 9:00am na safe gaba-daya mutanen gidan a farke suke Momy ce da kanta a kitchen sai khadija da Ummi da suke taya ta aikace-aikace yayin da Suwaiba keta share-share da goge-goge Jiddah kuwa da Alama bata tashi ba, Siddeeqah kuwa hango ta nayi cikin shigar material ja da ratsin bulu dinkin doguwar riga, kasan cewar bata da kiba bai kama mata jiki ba kuma ko hoda bata shafa a fuskar ta ba, bata iya daura dan kwalin zamani ba saboda haka tayafo sa  a kanta, gyaran gashin jiya duk ya tuje ya zame daga dunot din da akai mata, saboda gyashin ta irin mai santsi din nan ne ahankali take saukowa daga step din,

Yayin da Sadeeq yake tawowa cikin sauri-sauri dan shi Sam bai lura da mutum ba, amma ita ta ganshi tana ta kokarin kaucewa amma ina, saida ya ture ta tayi taga-taga zata fadi bakin ta na rawa takasa yin ihu kamar yadda ta saba saboda firgita, sai alokacin Sadeeq din ya lura cikin zafin nama ya kamo ta ya janyo ta kirjinsa kokarin hada hannayen sa yake ya rungume ta tayi sauri ta ture shi cikin tsiwa tace "malam na fara gajiya da wannan iskancin naka ko ka dauka kowa dan iska ne irin ka? to ka kiyaye ni wallahi dan ko hannu na ka kuma tabawa ka taba Allah ya isa, ina fatan ka gane". Tana gama fadar haka tai saukowar ta dama shi haurawa zai yi

Bai ce mata komai ba kuma baiyi kokarin bin ta ba, saboda atunanin sa idan sun rabu yau ba lailai ya sake haduwa da ita ba saboda haka zai daga mata kafa duk rashin kunyar da zatai mai bazai tanka mata ba

"Momy ina kwana". Siddeeqah ta fada lokacin data karasa kicin inda Momy ke wanke fatatus

Cikin sakin fuska Momy ta juyo ta kalleni kana tace "lafiya lau yan makaranta har kin shirya?".

"eh Momy".

"yau ba saikin tayani ba kije falo ki zauna ga Umar can sai kuyi fira kamin mu gama, saboda kada kayan ki su baci kije makaranta a dunga yi miki dariya".

"to nace" na fito falo inda na tarar da Umar shi kadai a zaune, kusa da shi na zauna kana nace "Umar". Da sauri ya dago kai ya kalle ni, na cigaba da cewa "da gaske dai makarantar kwana yaya zai kai ni, shikenan bazan kuma sake ganin ku ba sai na dauki tsawan lokaci, wallahi ni an cuce ni an raboni da Inna gashi yanzu kudun da nike gani nike jin dadi za'a rabani da ku". Tuni kwalla ta fara zubomin ban damu na share ba saboda kukan shine ya kamaceni a wannan lokacin, sosai Umar ke lallashi na amma Sam naki sauraren sa kuka na nike wuy-wuy, acikin wannan halin Daddy yazo ya isko mu Tambayar Umar ya shiga yi abinda yasani kuka Umar bai boye masa komai ba ya fad'a masa, Daddy ya ce "haba mai gaskiya indai akan makarantar da zaki tafi ne kike kuka to an fasa babu inda zaki ai na dauka da yardar ki zai kaiki ashe gaban kansa yayi".

Karaf maganar da Daddy yayi sai a kunnen Sadeeq saboda saukowar sa daga sama kenan kan yakara so falon kasa ya tsinkayi kalaman Daddy

Cije leban sa yayi da karfi bai saki ba saida yaji zafi afili yace "wannan wace irin yarinya ce mai naci da taurin kai, yanzu mai take nufi ya riga yagama tsara yadda komai zai tafi, amma yanzu Daddy yana neman ya kofsa masa".

Bayan ya kara so falon har kasa ya tsugunna ya gaida Daddy ba yabo ba fallasa ya amsa mai

Kana Sadeeq din ya nemi kujera ya zauna yana kitsa abubuwa da dama a cikin ransa

Haka itama Siddeeqah babu abin da zuciyar ta bata raya mata game da Sadeeq ba, sai yanzu take kara tabbatar wa da zuciyar ta cewa tabbas fa yaya ba son ta yake ba, idan ba haka ba mai yisa bai kai daya daga cikin kannan sa ba? Bata da wannan amsar amma tabbas ita ko za'a kashe ta bazata wannan makarantar ba ta gwaumace ta mutu a jahilar ta

* ** * * * * * * * *

Kwance take kan gado tayi dai-dai abinta da ganin ta hankalin ta kwance yake sai sharar baccin ta take.

Ringing din wayar ta da ake kira shiya ta data daga nannauyen baccin daya dauketa tun jiya dan ko Sallar asuba batayi ba.

A firgice ta farka ta lalubo wayar ta daga karkashin filo bata tsaya duba wanda yake kiran nata ba ta d'auka ta kara a kunne, daga muryar sa ta gane Abba ne, ban san me yace mata ba naji tace "to Abba gani nan ".

Bata tashi a lokacin ba sai da takara kusan 13 minutes sannan ta tashi tsaye tana mika da hamma da Alamar baccin bai isheta ban daki ta fada tayo wanka a gurguje bayan ta fito ta shafa nayukan ta kana tasaka atamfa riga da zani rafa ta dan fesa turare mai sanyin kamshi ta daura dan kwalin ta ta fito cas da ita, saida ta kalli kanta a madubi irin wanda yake nuna mutum daka sama har kasa kana tayi Murmushi ta fito dakin ba tare da tayi sallar asuba ba, wannan dama dabi'ar ta ce hada sallah ko ba abinda take yi bazata taba yin sallah akan lokaci ba sai lokacin ta ya fita an shiga na wata

A falo ta sami Mama da Abba suna karya wa akan dinning zama ita ma tayi kusa da Abbah aka shiga karya wa da ita suna dan taba fira akai-akai.

Bayan sun gama mai aikin su Ramatu ta zo ta kwashe kwanukan, kana Abba ya koma kan kujera ya zauna "shalele tashi ki dauko min rimot". Abba ya fad'a yana duban Zuby da mikewar ta kenan a kan dinning da "to". Ta bashi amsa bayan ta miko mai zama tayi kusa dashi akasa tana ja mai yatsun kafa, saboda tasan Abbah nasan haka

* * * ** *** * * Kowa na karya wa amma ban da Siddeeqah da tayi tagumi ta tsurawa filet din gaban ta ido Wanda yake a cike da soyayyan dan kalin turawa da kyau

"Momy tace Wai ke kuwa lafiyan ki lau gaba daya yau ban gane miki ba ko akwai abinda ke damun ki ne?". Ga dukkan alamu hankalin ta baya tare da ita saboda tayi zurfi cikin tunani, lura da haka yasa Khadeeja dafa kafad'ar ta tace "sisi wai maye haka irin wannan tunanin kina yar karamar ki".

Fir gigit Nadawo daga duniyar tunanin da na Lula ba tare da na gano nazarin da nayi ba.

Kallo na Momy tayi kana ta kawar da kai Daddy yace "ci abincin kinji ki daina irin wannan tunanin babu kyau nasha fada miki".

Kai na gyada kana na fara cin abincin haka nai ta turawa kamar ina cin magani haka nike jin dan danon abin cin .

Bayan mun gama kan mu tashi daga dinning din Daddy ya kalli Sadeeq yace "kai Sadeeq na soke tafiyar Siddiqah zuwa makarantar kwana ba dani ba za'ai wannan zalincin kaji na fada maka wannan ai zalinci ne, na dauka da yardan ta kayi komai ashe san zuciyar ka ka aikata, na baka daga nan zuwa lokacin da zan yi tafiya ka lallashe ta idan ta yar da to idan kuwa bata yarda ba sai dai ka kaita wacce yan uwan ta suke zuwa, kada kuma ka man ta zuwa anjima zan tafi bayan azahar ".

Daddy na gama fadar haka ya bar gurin

Saboda kaduwa har da zufa ke karyo wa Sadeeq Sam baiyi tsammanin abin zai kai haka ba, kallo na yayi muka hada ido na banka mai harara, cije Leban sa na kasa yayi nima nayi yadda naga yayi, Momy na lura damu bata ce komai ba ta Mike zata bar dinning din yaya Sadeeq yai sauri yace "Momy dan Allah kiyi wani abu akai kice wani abu please nasan Daddy na jin maganar ki".

Tace "kaga Kaga ka fita ido na tun wuri kayi abinda Daddyn ku yace maka dan yanzu kayan sa zan je na shirya babu ruwa na ni".

Ta na gama fada ita ma ta bar wurin

Ya mutsa fuska ta nayi nima kana na Mike tsaye nayi mika harda dan ihu na hada kana na bar gurin ina dariya kasa kasa, nasan Sadeeq ya tsani haka da ace Daddy bai ce sai na yarda ba da tuni ya kai min duka

Shikuwa Sadeeq mamaki yake yadda karamar yarinya kama ta ta iya makirci

Tashi yayi ya haura sama dakin sa ya shiga kana ya dauki wayar sa daya barta akan gado kan kujera ya koma ya zauna kana ya shiga danna nambobin Farook ya ko ci sa'a ringing 3 Farooq ya dauka kiran, daga can ban garen Farooq yai sallama inda Sadeeq bai amsa masa sallamar ba, kusan ita ce dabi'ar sa ba kowa yakewa sallama ba, kuma ba kowa yake amsa wa ba, sai cewa da yai "Malam kana ina ne?".  Ya bashi amsa da "gani na kusan shugowa Abuja dan wallahi anyi min transfer zuwa Yobe shiyasa nazo na dauke ta na kaita da wuri nima na samu na shirya".

"kamar dole a kasa sa yai magana a dakile yace yobe fa kace to Allah ya tsare".

Ran Farooq bace yace "dan iska saboda ba kai bane aka mawa dole kayi min isgili, insha Allah kai ma sai anyi maka in dai transfer ce ruwan dare ce, dan wannan sabon matemakin kwamishinan bashida kir ki".

Ko a jikin Sadeeq yace "to sai me ai dama aiki nace zanyi kuma idan anyi min transfer din akan aiki ne kaga kuwa mai zai dame ni?".

Cikin jin haushin kalaman sa Farooq yace "babu, dama yanzu baza kasan inda matsalar take ba sai nan gaba".

"Am kaga dama akan yarinyar can na kira ka".

"Wace yarinyar?". Farooq ya tambaya duk da ya gane akan Siddeeqah Sadeeq yake magana amma sai yai masa bariki

Cikin kosawa da maganar Sadeeq yace "wai meyisa ka fiye surutu ne kafi son aita maimaita magana daya, bayan kasan yanzu bani da wata matsala da ta wuce waccan yar kyauyen".

Cikin zolaya yace "kai malam ni bana son gulma ka fito kayi min bayani sai kace matar ka amma sai wani boye-boye ka ke".

"amma kai ba karamin dan iska bane ni zaka raina wa hankali sai anjima na ma fasa fada maka abinda zan fada".

Farooq na dariya yace "matsalar ka ce wannan, nan da 15 minutes zan kara so insha Allah kace mata ta shirya".  Yana gama fada bai jira amsar Sadeeq ba ya kashe wayar

* * * * * * * * * * "Shalele".

"Na'am". Abbah

Wai kuwa kin tuna aboki na Dr Usman da yake da zama a dubai?".

" Eh Abbah ".

"yauwa kin San ai yana da d'a, da yake karatu a kasar misra?".

"eh Abba kan ya tafi ma ai yana zuwa nan ko ba Maheer ba?".

"shi fa ashe baki manta dashi ba na dauka kin manta dashi to kinsan shi kadai Dr ya mallaka kamar yadda nima ke daya na mallaka".

"eh hakane Abba".

"Masha Allah na zauna ni da Dr din munyi magana har mun gama yanke hukunci zamu hada ku aure kar shen watan nan zai dawo dan ya kammala karatun sa a harkar kasuwan ci, kuma da ya dawo sai biki babu bata lokaci".

"amma Abbah".

"abba me? Shalale a wannan karon ko sau daya ki daure kiyi min abunda nike so, duk da nasan kina da Wanda kike so amma ni wannan ne zabi na".

Yana gama fadar haka ya mike gabad'aya Zuby jin ta take kamar ba ita ba saboda tasan Maheer mutum ne mai shegen sa ido da taka tsan tsan akwai shi da tsoran Allah kuma yana son mace mai addini dan yasha fada mata, shin ma cewa yayi yana son ta Ko kuwa dai iyayen su ne suke son su hada auren? Tashi tai daga zaunan da take ta shiga yin safa da marwa tana zagaye dakin, a haka Mama ta shigo ta cin mata

* * *

Please Comment Follow me Vote I love you all Allah ya bar zuminci da kauna

NI DA YAYA SADEEQ

·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

CHAPTER 27

"lafiya naga duk kin rasa nutsuwar ki lokaci guda ko wata maganar Abban ya fad'a miki?". Mama ta tambayi Zuby dake faman safa da marwa a falo dayan hannun ta dafe da goshin ta saboda jirin da take gani.

Cikin sauri Zuby ta juyo ta kalli Mama tace "ina lafiya Mama wallahi ni mutuwa zanyi bana son Maheer Mama ki taimaka min idan Abba yace sai na aure sa mutuwa zan yi".

A dai dai lakacin Abba ya fito daga bedroom din sa da jaka trolley yana ja yar karama, da alamar tafiya zai yi, yaji duka abinda Zubaidan ta fada ransa na suya yace "aikuwa sai dai ki mutu amma ko gawar ki ce sai an kaita gidan Maheer zan can banza zan can hofi, duk laifin ki ne Mariya" ya fad'a yana maida duban sa gare ta "ke kika bata yarinyar nan amma gabaki dayan ku zanyi maganin ku bari na dawo tafiya, kuma kufara shirye shiryen biki daga yanzu zuwa kowani lokaci za'a daura aure". Yana gama fadar haka ya fice abun sa, Maganar da yayi da Kamal jiya ta kara dawo mai sabuwa fil yaji kamar yanzu ake fada masa ita, take zuciyar sa ta fara kuna da radadi tabbas ka haifi d'a ne amma baka haifi halin sa ba, idan kuwa hakane Mariya ta dade tana raina masa hankali amma ya godewa Allah da jiya Kamal ya ganar dashi, shi dama ya dade yana zargin da akwai abinda suke boye masa ya bari ne saboda yasan dole wataran asirin su zai tonu, ya kuduri aniyar sa ido sosai akan ta saboda yagano abinda take aikata wa, aran sa yace  "ya tabbata Mariya ce ta Lalata yarinyar saboda duk wani abu  da take yi da sanin ta take aikatawa, tabbas idan ya gono ba abun arziki bane kashin Mariya ya bushe dan san da zai bata Zubaidan tayi alkawarin bata tarbiya kamar diyar da ta haifa ta cikin ta da haka ya kawar da tunanin ya shiga cikin mota ya bata wuta.

hhhmmmm idan Abba yasan munanan abun da take aikata wa ya zaiji acikin ransa kuma wani mataki zai dauka akan Mama Mariya ? Kudai cigaba da bina sannu ahankali ganin yanda labarin zai kaya

* * * * * *

Da misalin 9:45 Farooq ne a bakin get din su Sadeeq inda yake dannawa mai gadi hon, da sauri mai gadi ya taso daga kan kujerar sa ya zo ya dan leka ta kofa ganin Farooq ya leko yana daga hannu yasa mai gadi yai sauri yazo ya wangle gate din, yana fadin "yallabai yau kai ne a gidan namu sannun da zuwa gaskiya ka sha hanya kayi sa'a yallabai kuwa yana gida bai fita ba". Shi dai Farooq bai tanka masa ba ya sulala da motar sa kana ya nemi guri yai fakin, mai gadi ya maida get din ya rufe yana kara jinjinawa Farooq hannu.

Jim kadan ya kashe motar ya fito,

A dai dai lokacin ni kuma na fito zan je na kaiwa mai gadi wasu kaya da Daddy yace na bashi, ina ganin sa na karasa gurin sa baki na dauke da Murmushi nace "laa! Yaya Farooq yau kaine agarin namu, aradun Allah naji dadin ganin ka dama na gaji da zaman garin nan yanda kasan ina kur-kuku haka nike jina, kafa ta kafar ka sai na bika mun tafi Dan de".

Yana dariya yace "to yar Inna keda zaki tafi makaranta ina ke ina komawa kyauye ko bakya so ki zama yar birni ki dunga turanci ki waye ki zama babbar yarinya?".

Shiru nayi na yan sakwannin da baza su wuce biyu zuwa uku ba kana na ce "yaya Farooq kenan duka wa'innan abubuwan da ka lissafa ina so na zama ko dan na bawa yaya mamaki , amma saboda mugunta irin tasa    makarantar kwana ya sama min  kuma yace kai ne zaka kaini, ko kazo tafiya dani din ne?". na karasa maganar ina gyatsine da jijjiga kugu.

Dariya nabawa Farooq yanda yaga lokaci daya na canza yanayin magana ta zai yi magana  nace" ban tari numfashin ka ba yaya amma ni babu inda zan bika mu tafi wata makarantar kwana, jeka ka dawo zanyi na kuma gayawa Daddy kuma ya yi na'am da batu na.

Dan yace " ma yaya Sadeeq in dai yana so ya kaini makarantar kwana to ya fara neman amincewa ta idan kuwa naki aminta sai dai fa ya kaini makarantar su Khadija".

Sajan sa Farooq ya shafa yace" ho ho ni Farooq yanzu ina shi Sadeeq din?". Tace" ban sani ba  amma dai yana gida bai fita ba ".

" To maza je ki kai wannan sakon da aka aike ki kizo mu shiga gidan".  

Nace "ban gane nazo mu shiga ba yah Farooq ni fa na fada maka in dai dan nice kazo gidan nan gwara ka koma dan bazan je ba, ba sai ka tsaya bata lokacin ka ba nasan bazaka rasa abin yi ba"

Ina gama fadar haka na wuce aiken da akai min, a zaune na gan sa hannun sa rike da radio kamar kullum ya kure volume kuma ya kara a kunnen sa, bai san nazo ba sai da yaji an kwace radio, a hasale ya jiyo ganin nice yai Murmushi yace " yar gidan Inna ya akai?" kayan hannu na na mika masa gami da fadin "wai me kake ji a radio ne? kullum da ita nike ganin ka kuma ka kure volume ko ciwan kunne baka ji". Yace "banda abin ki yar Inna mai zan ji da ya wuce labaran dunya ai labaran duniya niki ji saboda yanzu lamarin kasar nan tamu abubuwa duk sun rukice sai addu'a".

Nace "hakane Allah ya kawo mana sauyi mafi alkairi ".

"amin" Yace gami da fadin "wannan kayan fa guga zan kai ko me?".

Nace "Daddy yace na kawo maka".

Ai kuwa yaji dadi sosoi dan kayan sabbi ne kala hudu haka dai na baro sa yana ta zabga godiya kamar wanda akace an gafar ta masa gabadaya zuniban sa.

A inda na bar sa anan na same sa tsaye da waya annu yana dannawa nace "baka tafi ba yah Farooq?".

"ina zani? ni da nike jiran ki mu shiga".

Nace "to shikenan tunda ka nace halan akwai abunda kake son yi muje".

Ina gaba yana baya har muka karasa cikin katafaron falon gidan in da naci karo da Sadeeq har saida ya ture ni, saboda shi zai fita ni kuma na kutsa kai abinka da mara nutsuwa, shi kuma ya dunfaro kofar ne cikin zafin nama, ihu na fara ina kiran sunan Daddy saboda kaina ya dan bugu da bango, shi kuwa yaya Sadeeq yayi tsaki sun fi biyar yana kara jin tsana ta a zuciyar sa yarinya sai tsinannan sharri to shi yanzu mai ya mata da take so ta tara mai jama'a?".

Daga kan da zaiyi sai yaga Farooq a tsaye jingine da jikin ban go ya harde yannayen sa a kirji sai Murmushin mugunta yake yi.

A hasale Sadeeq yace" malam maye?".

"Nishadi mana ko kar nayi?". Farooq ya fad'a still kuma yana dariyar sa

"kallon kanka ka rainawa hankali Sadeeq ya bi Farooq da shi kana yace bani wuri ni na wuce kana bata min lokaci".

A dai dai lokacin Momy ta fito tana fadin "yaya lafiya ke dawa".

Sam bata lura da Farooq ba sadeeq ta hanga a gurin aikuwa ta fara yi masa fada tana cewa "a haf ai nasan sai kai sarkin cin zali in dai kaji kukan yarinyar nan a gidan nan to ba kowa bane face  kai".

Kallo na tayi tace ke tashi rabu dashi kiyi masa Allah ya isa tunda bazai daina ba Allah zai saka miki ".

Ina gunjin kuka na mike ina fiki fiki da idanu na ina kara matso kwalla a haka na haura sama na wuce daki na na kwanta a kan gado ina kallon sama ina jin zuciya ta babu dadi.

Farooq na shaafa keya yace" Momy ina kwana?".

Sai a lokacin Momy ta waigo inda yake fuskar ta a sake Tace" lafiya lau  Farooq yaushe kazo ne?".

Yace" shigowa ta kenan "

Tace" madallah ya Hajiyar taku?".

" Suna lafiya suna gaida ku".

"Masha Allah muna amsawa, kar dai tafiya da gimbiyar kazoyi ?". Ta tambaye sa

Yace "eh Momy".

Tace "bai fada maka ta fasa zuwa ba?".

"Eh bai fada min ba amma yanzu dana shigo kan na kara so cikin gidan na hadu da ita abakin get shine take sanar min cewa ta fasa zuwa".

Tace "yauwa sai kusan yadda za'ai dan Daddyn ku ya kusan gama shiryawa kuma yana so yaji matsaya ne kan ya tafi". Tana gama fadar haka ta bar falon.

A hankali Farooq ya kara so inda Sadeeq yake ya dafa kafadar sa yace "aboki na akwai matsala fa amma kana nuna kamar abin bai dame ka ba bayan kai ne mutum na farko daza ka fi kowa shiga damuwa idan har yarinyar nan tace baza ta ba. Ni wallahi mamaki kake bani yar wannan yarinyar ta gagare ka sarrafawa sai kace ba namijin duniya ba ko girman kan ne zai hana ka shaho kan ta? To idan shine zai fi kyau ka aje sa a gefe saboda.... ".

"dallah malam dakata ya kake magana kamar kana bani umarni nifa kaga wannan karatun da za tai kanta za tai mawa ba ni ba, saboda haka idan ma karatun ne tace bazatai ba kwata kwata ni ba damuwa ta bane, bayan ita zan iya auran gudu uku wa'inda suka fita komai, so kada ka tsaya bata yawun bakin ka ".

Farooq yace" nifa ba nufi na ka bata hakuri ba, ba kace yarinya ce bata da wayau ba kuma bata san komai ba, to ai shaho kanta ba zaiyi wahala ba shine nike so kayi mata yan dabaru ko ka fasa kara auren ne?". Y

Yace" ban fasa ba amma kada ta gano ni fa kasan bana son raini".

"haba babu abinda zata gano kawai shiga ciki zan turo maka ita".

Yace "to shikenan kai anan zaka zauna?".

"eh".

Farooq ya fad'a yana mai samun kan kujera ya zauna yace "kasa a kawo min ruwa da dan abin tabawa".

"To" yace ya haura sama.

Khadija ce ta sauko bayan sun gaisa ta nufi  kitchen ta hada masa kayan ciye ciye da ruwa  kana ta dora akan katon tirai tazo ta aje masa akan tebur zata tashi yace "ina zuwa ki zauna muyi fira bana son zama shiru ni".

Komawa tai ta zauna ai kuwa nan Khadija tai ta basa labari yana kwasar dariya

* * * * * * *

Nan Abba ya bar Mama da Zuby cikin jimamin magan ganun sa, tabe baki Mama tayi ta kamo hannun Zuby suka zauna akan kujera tace" wai meke faruwa ne dan ni wallahi ban fahimci inda kalaman Abban ki ya dosa ba".

Sai da Zuby ta sauke gwauran numfashi kana tace "kina nufin Abba bai fada miki suna son su hada aure na da Maheer ba?". Tai maganar ne cikin sigar tambaya

Mama tace "bai fada min ba amma in dan wannan ne ki kwantar da hankalin ki ban ga aibun Maheer ba ni".

"Haba Mama ya kike so nayi da Soyayyar Sadeeq da take dawainiya dani? wallahi yanzu haka daurewa nike yi rabo na dashi tun jiya ko awaya bai kirani ba".

"shiyasa nace ki kwantar da hankalin ki yanzu ki fara shawo kan Sadeeq din daga baya sai musan yadda zamuyi da Abban naki".

"Mama kin San bamu da wannan lokacin kuma tabbas Abba da gaske yake, dan naga bacin ransa, wanda ban taba gani ba, wallahi ni ba wai Maheer din ne bana so ba tsoro nike kada asiri na ya tonu a silar auren sa da zanyi".

"Da wannan dan wannan" Mama ta fada tana sa hannu ta goge gumin daya keto mata a goshin ta , wani kallo Zuby ta bita dashi wanda ita kadai tasan ma'anar sa, kamin ta tashi ba tare da tace komai ba tanufi dakin ta, wayarta ta d'auka number Sadeeq ta shiga nema har sau uku tana kiran sa amma bai dauka ba

Shi kuwa Sadeeq zaune yake a dakin sa yana kallon kiran ta amma sai yaki dauka saboda ba karamin mamaki ta bashi jiyannan ba, gashi bata kirasa ba tun jiya bare ta basa hakuri shine yanzu zata kira sa tai masa dadin baki dan ta mayar dashi dan iska, Sam bazai dauka ba har sai tayi nadama yanda ko nan gaba baza ta maimaita makamancin sa ba.

Turo kafar dakin a kayi ko sallama batai ba ta shiga, a dai dai lokacin kiran Zubyn ya kara katsewa

Saida na turo dan karamin baki na nace "yaya gani yaya Farooq ne yace kana kira na".

Ganin yadda nike cika nike batsewa naba wa yaya dariya sai da yai Murmushin sa mai isar sa wanda yake kara baiyana ainihin kyawun sa yace "zo kiji magana zamuyi kika zo daure da dan kwali a kugu sai kace wacce tazo filin daga".

Sai alokacin na tuna  da dan kwalin da naci damara dashi ni kaina dariya abun yabani saboda na dade ban yi hakan ba kwancewa na shiga yi yaya yace "a a ki bar abin ki ya miki kyau". 

Dan nesa dashi ta zauna yace "ikon Allah wai ni kike gudu to bari ni nazo na same ki na fada miki ba dukan ki zanyi ba magana ce zamuyi ". Ya karasa maganar a lokacin da ya zauna kusa da ita hannayen ta ya kama gami da tallafo habar ta , hada ido sukai cikin sauri tayi kasa da nata, ba wai dan tasan kunya ba amma sai taga ya kara mata kwarjini bazata iya cigaba da kallon kwayar idon sa ba, shiko Sadeeq tausayin Siddeeqan  ne ya kama shi a karo na farko a cikin rayuwar sa tun bayan ta fara tasowa, wallahi bai taba tunanin akwai ranar da zata zo yaji tausayin ta ba sai gashi rana kwatsam wai tana bashi tausayi, bai san sanda ya rungume ta a kirjin sa ba yana jin bai kyauta mata ba, Siddeeqah dai ta zama kamar mutum mutumi cikin ta har ya duru ruwa tsoro ya kamata tasan yauma aljanin yayan nata sun kuma tashi, tana so ta dago tana tsoro, saida ya gaji dan kansa ya sake ta yana shafa bayan ta yace "dan Allah Siddeeqah kiyi min wannan alfarmar ki daure ki tafi wannan makarantar wallahi saboda ina son ki ne nayi miki wannan gatan".

Da sauri Siddeeqah ta dakatar da shi ta hanyar fadin "ya isa haka yaya duk maganar da zamuyi a tsakanin mu kada ka ambaci so domin babu shi a tsakanin mu har abada, ka fada min ba zaka taba sona ba kamar yadda nima ban taba jin sonka dai-dai da rana daya a cikin zuciya ta ba, na yarda zan tafi idan har kayi alkawarin za kabi duk wani sharadi da zan fada maka".

Bakin Sadeeq na rawa Yace "naji fada min zan bi duk abinda kika ce".

Ta cigaba da cewa "na yarda zan je idan har ka yi alkawarin zaka sake ni idan nagama karatu, lokacin na girma na kara wayau ta yadda zan samu irin mijin da nike so na aura, amma ni wallahi Sam ban dace da kai ba yaya". Ta fada tana dago kai, suka hada ido tayi sauri tai kasa da nata saboda kwarjinin sa.

Yana mamakin Siddeeqah lokuta da dama idan tayi wata maganar ko babbar mace albarka koda yake ba abin mamaki bane zamani ne dan ga yaran da basu kaita nan ba suna abin da ba kowace babbar macen ba, itama dan ta taso a kauye ne shiyasa take da wayan kauye.

yace "in dai wannan ne mai sauki ne zan sake ki tunda ke ce kika bukaci haka, amma mai zaki cewa su Daddy da Momy idan suka bukaci sanin dalili?".

Sai da ta tashi daga inda take tayi tsallan murna tace "bani ce zan basu amsa ba kaine ya dace da ka basu amsa, ko dai ka fada musu gaskiyar bama son junan mu ne ko kuma kayi musu karyar da har abada bazasu gane ka ba, kaga sai ka je ka auri wacce kake so, nima na auri wanda nike so".

"to". Kawai Sadeeq yace dan tafara gundurar sa da wannan maganganun nata da yake daukar su kamar tatsuniya

Bai san ita kuwa siddeeqah har cikin ranta take fada masa wannan maganar ba

Tace "ko kaifa yaya  hannu ta mika masa tace mu kulla abota yaya nayi maka alkawari daga yau zan dunga jin maganar ka zanyi kokari na zama mai nutsuwa kamar yadda kake so zan dunga yin duk abunda kace nayi ina son wannan abotar tamu ta fara daga yanzu zuwa lokacin da zaka sake ni".

A tunanin Sadeeq Siddeeqah ce bata da wayau dan shi gani yake ya gama da ita shiyasa komai tace yake yarda, yanzu ma ya yarda su kulla abota, har zuwa ranar da zata kare secondary school ya bata takardar ta.

Hannun sa ta kama tace "yaya tashi muje falo ka fadawa su Daddy na yarda".

Mikewa yayi kamar yadda tace ta shiga jan hannun sa suka soma tafiya tana gaba yana biye d a ita a baya, a haka suka fara taka step suna saukowa, tuni suka fara daukar hankalin wasu daga cikin mutanen falon da suka lura dasu kama daga Daddy Umar Jiddah da Ummee banda Farooq da Khadija da suka zauna akan kujerar da tabawa step din,  Momy kuwa bata gurin tana bedroom taje daukowa Daddy wayoyin sa daya manta, gaskiya sun burge sun bada sha'awa kuma sun dace da junan su.

Ahaka suka karaso fuskokin su dauke da nishadi Ba karamin mamaki Momy tayi ba alokacin da ta gan su, haka ma Daddy da sauran yaran gidan  

Koda suka karaso falon kan kujera Siddeeqah tai wa Sadeeq masauki inda itama ta zauna kusa da shi hannun ta na sarke da nasa sai Murmushi take tana kara shige wa jikin sa, shi kuwa Sadeeq daure wa kawai yake dan bai saba da wannan sabon al'amarin ba yana so yai mata tsawa yana tsoran ta birkece masa

Momy da Daddy kuwa addua suke acikin ran su Allah yasa lokacin haduwar kan yayan sune yazo Allah yasa su d'aure ahaka

Comment Share Vote

NI DA YAYA SADEEQ

·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

Chapter 28

______Shi kuwa Farooq tsabar mamaki sai mutsuka ido yake yana budewa gani yake kamar a film yake kallon su.

can Daddy ya numfasa yace "dama kai niki jira yanzu nike cewa Umar yaje ya kira min ku  dan lokacin tafiya ta yayi".

"Siddeeqah". Daddy ya kira suna na cikin wata murya mai nuna ana jin tausayin wanda akai wa ita".

"na'am" nima nace bayan na zare hannu na daga jikin yaya na daga kai muka hada ido da shi.

Ya cigaba da cewa "shin kin amince zaki tafi makarantar kwana?".

Ina wasa da yatsaun hannu na nace "eh na amince Daddy".

Sai alokacin Momy dake tsaye ta zauna tana fadin "Alhamdu lillah Allah yasa hakan ne yafi alkairi".

Take yaya Sadeeq ya sauke ajiyar zuciyar da ko wannen mu sai da ya dago kai ya kalle shi, ni kuwa takaici ne ya kamani ganin yadda yake murna zai rabu dani sai kace zai rabu da musifa, lallai ma yaya tabbas zan nuna maka nima macace kuma zan iya yin duk wani abu da mata suke yi wajen burge mazajen su, sosai nayi nisa cikin tsara yadda abubuwa zasu kasan ce idan na girma, firgigit nai a dan tsorace na dawo hayyaci na  sakamakon tabani da kafa da yaya yai.

Daddy yace "Siddeeqah lafiya tunanin me kike yi haka? bayan na hana ki yin dogon tunani irin wannan, kina yar karamar ki  Ko so kike hawan jini ya kama ki? Ki mutu tun kamin lokacin ki yayi?".

Baki na narawa nace "A a Daddy insha Allah na daina daga yanzu".

Yace "Masha Allah, Allah yai muku Albarka ni zan tafi ki kula da kanki banda kula kwayen banza karatu ne ya kaiki shi zakiyi "

Nace "to Daddy nagode insha Allah bazan baku kunya ba".

Sai da ya sallami duka yaran gidan, dama Momy ya ruga ya sallame ta, kana yabi ko waccen mu da kudi masu kauri, Gaba dayan mu muka dunguma zuwa harabar gidan saboda muyiwa Daddy rakiya, saida muka ga tafiyar shi sannan muka dawo gida, Momy ta daura daga inda Daddy ya tsaya nasiha take min mai ratsa zuciya, jiki na duk yai sanyi, son Momy da kaunar ta yana dad'a ratsa ilahirn jiki da bargo na, saboda yadda take kula dani, da nuna min so da kauna.

Bayan ta gama min nasihar tace "naje na kara shiryawa".

Kallon Ummi da Khadija nai muka hada ido naga jikin su yai sanyi Umar kuwa harda kwalla, jiki na a sanyaye na mike  na haura sama ba wani wankan na sake ba kaya kawai na sauya  i zuwa riga da sikel na atamfa dinkin bai min yawa ba kuma bai kamani ba, sannan na dauko hijabi na nasaka, ko da na sauko a tsaye na samu Yah Sadeeq da Farooq da wani katon akwati a gaban shi, yana Murmushi yace "yauwa muje ko, ke muke jira".

tuni kwalla ta fara wanke min fuska ta nace "amma yaya baka kira min Inna ba".

Shafa keyar sa yai  yace "ai na manta gwara da kika tuna min".

Hannu yasa a aljihu ya ciro wayar sa, amma sai ya rasa wa zai kira sanin Inna babu waya a hannun ta dama da ta Farooq suke gaisawa "saida ya dan bata rai yace "kina da rigima Siddeeqah sanin kanki ne Inna bata da waya"

Goshi na dan dafe, tuna cewar batada wayar.

Yace "amma dai ki bari zan san abin yi tunda ni yau zan koma zan baki number ta idan kinje makarantar sai ki bama wata senior ta kirani sai na hada ku kuyi magana".

"to" kawai nace

har bakin get su Momy suka rako ni, in rungume wannan in saki wannan haka dai nan ta kuka Khadija da Ummi da Umar suna tayani, yayin da Momy ke bamu hakuri kamar kar mu rabu da juna saboda sabon da mukayi,  sabanin Jiddah da ko Allah ya kiyaye hanya bata ce ba sai kallon banza da take bi na dashi, tana cika tana batsewa, yi  nai kamar ban gan ta ba saboda yanzu ba lokacin fada bane a gurina.

Da kyar yaya ya lallashe ni na shiga mota inajin raina babu dadi, tuni daman yah Farooq ya shiga sannan shima sadeeq din ya shiga mai gadi ya wangale get muka fice, su Momy nayi mana Allah ya sauke ku lafiya.

Yaya Farooq ne ke tukin yayin da Sadeeq ke kujerar me zaman banza ni kuma ina gidan baya ji nike gabad'aya rayuwar ta dagule min tafiya ta fara yin nisa dan barci har ya fara dauka ta

* * * * * * *

Zaune take kan dan madaidaicin gadon ta hannun ta rike da wayar ta sai cije lebe take tana tsaki wai ita Sadeeq zaiki dagawa waya to wallahi bai isa ba tun da yace yana son ta sai ya aureta, ta fada afili yayin da tayi  kwafa.

Number Lubansy ta danna kira har tafara ringing sai kuma ta kashe saboda tasan itama fushi take da ita baza ta d'auka ba, idan tana son su shirya sai dai fa ta shirya taje gidan su, gashi ita kuma yanzu bata jin zata iya fita saboda zuciyar ta babu dadi, safa da marwa ta cigaba da yi gabad'aya ta rasa me zatai, can ta tuna da group din su na madugo association aran ta tace "bari na dan hau online ko na samu na rage damuwa" gefan gadon ta zauna kana ta dauko wayar ta shiga cikin whatsapp din nan ta tarar da sakonni masu yawa amma duk bata tsaya bi ta kansu ba, abinda ya kaita kawai shi take so tayi, bayan ta shiga cikin group din a hankali tafara karanta sakonnin da akayi bata nan bata jima tana duba chart d'in ba ta fahimci fada a keyi, sakamakon wata da tayi left cikin sauri da sauri ta cigaba da duba sakonnin har zuwa inda aka tsaya da firar take ta fahimci Sumy ce tai left kuma ana kyautata zaton yar leken asiri ce gabad'aya hankulun officials da members din kungiyar a tashe yake saboda idan asiri ya tonu ba karamin yaki za ai ba, tuni Zuby ta shiga cikin firan inda har take bada labarin tayi magana ma da yarinyar har take ce mata "hajiya Tubalas ce ta kawo ta"

Hajiya Tubulas da jin an ambace ta, ta shiga auna ashar tana cewa "kada ayi mata sharri ita yanzu ko wuqa a ka sa mata a wuya a kace ta siffan ta kammannin Sumy to sai dai a yanka ta dan bata san ta ba".

Shugabar kungiyar madugo tace "ya kamata a hada meeting na gaggawa saboda a kawar da wannan gagarumar matsalar".

Tubulas tace "gaskiya bazai yuyu ba saboda a cikin dokokin kungiya ba a meeting sai ranar litinin din da tazo a cikin karshen wata, kuma kunga yau talata 28 ga wata, nasan kunsan cewa  karya doka daya ta wannan kungiyar dai dai yake da tonuwar asirin mu gabaki daya".

Sai alokacin Turai ta tuna da wannan dokar kuma gaskiyar Tubulas ne karya daya daga cikin dokokin kungiya babban laifi ne dan har gwara su dauwama a cikin wannan tashin hankalin da suke ciki, amma abin dubawa anan shine wata uku da suka wuce duka watan bai kare da litinin ba, kuma da alamar wannan ma ba da litinin zai kare ba, tunda yau talata.

Duk kannin su sunyi na'am da batun Tubulas saboda haka suka ce a nemo wata mafitar amma haka sukai ta fama duk inda suka bi sai suga babu hanya

Zuby dai gajiya tai ta sauka daga online din tana mamakin yadda Sumy ta ci amanar su, tasan tabbas kungiya bazata bar ta a haka ba sai ta dauki mummunan mataki akan ta.

Kofar dakin ta taji ana bugawa da sauri taje ta bude ba tare da ta tambayi wanda yake buka kofar ba, koda ta bude Lubancy ce ta shigo tana wani shan kamshi bakin ta dauke yake da chingom tana taunawa yana kara kas-kas, haka dai tai ta yamutsa baki tana yauki, bayan Zuby ta maida kofar ta rufe tazo ta rungume ta tana cewa "aminiya nayi missing din ki". Lubancy taso sharewa amma saita kasa saboda a matse take tuni itama ta rungumo ta tana sauke ajiyar zuciya, basu tsaya wata wata ba suka shiga cire ma juna kaya suka fada kan gado suna nishi tuni suka fara shafe-shafen juna suna sauke ajiyar zuciya.

idan kida ya sauya rawa ma canza ta ake yi, ganin abin yafi karfi na yasa na fito daga dakin naja musu kofa, ina yi musu adduar Allah ya shirya su dan wannan dabiar bata mutanen kwarai bace, wace irin musifa ce wannan da mace take neman yar uwar ta mace yayin da shima namiji yake neman dan uwan sa namiji, shiyasa annoba bazata rabu damu ba saboda aduk lokacin da akasumu saukar annoba to sabon Allah ne yai yawa akasa, kuma duk masu wannan dabiar a wuta zasu dauwama, indai basu tuba sun daina ba. wa'iya zu billah.

* * * * * * * *

Yunwar da ta fara kwakular ciki nane ta tashe ni daga nannauyen baccin daya dauke ni, na manta a mota nike saboda haka nai mika gami da yin juyi, ai kuwa cikin rashin sa'a na fada sakon mota inda ake saka kafafu, ihu na fara ina kiran sunan yaya da duk ya bi ya gaji sai mita yake wai Farooq baya gudu ". Shi kuma Farooq na cewa" in ba sama kake so na tashi ba ai wannan gudun ya isa ".

Ihu na ne ya katse musu firar su da sauri yaya ya juyo da kansa cikin motar yana fadin "subhanallah garin yaya haka ta faru maza tashi". Ya karasa maganar yana zuro da hannayen sa da kyar na iya temaka masa ya daga ni, bayan na gyara zama na akan kujera nace "yaya wai har yanzu bamu kai ba ni na gaji yunwa nike ji". Na karasa maganar cikin sigar shagwaba, nuna min Farooq yai yace "duk laifin shi ne kwata kwata baya sauri tafiya yake kamar wanda yake tsoran taka kwalta".

Nace "to ni yaya yunwa nike ji"

Yace "to bari mu karasa can gurin ina kyauta ta zaton karamar kasuwa ce sai muje baza'a rasa abin tabawa ba". Ya fad'a yana nuna min wani guri da nike hangen mutane

"To" Nace yayin da na hada kaina da gwuiwa ta

Ba mufi minti 7 ba muka karasa bakin gurin, kasuwa ce yar karama mata da maza sai zurga zurga sukeyi, yara da manya Farooq yace "banda abinka Sadeeq me zamu samu anan da zamu ci?".

Yace "mu fita ahaka ba zamu gane ba kuma can ma kamar masallaci ne mayi sallar azahar.

Yah Sadeeq yace" ki zauna a mota bari mu fita mugani ko zamu samu abinci".

Ban bashi amsa ba suka fita harda rufe motar

Basu wani jima ba sai ga Yah Farooq ya dawo da kwano a hannun shi da kwarya, bayan ya bude motar ya miko min na amsa, shi kuma ya juya 

Koda na bude kwanon danbu ne na gani yaji gyada da zogale yayin da ita kuma kwaryar fura ce acikin ta me rai da lafiya

Ba tare da nayi bismillah ba na shiga cin danbun, duk da yawan danbun saida na kusan yin rabin shi saboda ina mutukar son danbu a rayuwa ta, bayan na koshi kuma na dauki kwaryar fura itama na fara sha saida naji na cika cikina dam, sannan na hakura ba don bakina ya koshi ba sai don cikina da ya koshi

Gyatsa nike so nayi kozan dan ji dadin ciki na amma taki zuwa.

Can saiga su yaya nan sun dawo hannun Yah Sadeeq dauke da gorar ruwa bayan sun zauna yace "kin rage dan bun?".

Nace "eh".

"yauwa miko wa Farooq danni bazan ci ba furar zan sha ai itama kin rage?"

"eh nace yayin da na miko mai kwanon danbun dana furar

A mota suka ci bayan sun gama  suka je suka mayar da kwanon da kwaryar

Daka bisani muka kuma daukar hanya

" Nace yaya amma dai mun kusa zuwa ko?"

" eh mun kusa bai fi sauran mu 30 minutes ba mu karasa, ya nuna min wata katan ga da muke ta shigewa yace "nan kinga duk makarantar ce, zaro ido nai nace" kai yaya gari guda haka ".

Yace" eh har tafi haka girma bari muje ki gani".

Haka dai nai ta yiwa Sadeeq surutu yana biye min duk da fuskar sa babu wal-wala amma duk tambayar da nai masa yana bani amsa, a raina nike cewa "nasan yana tsoron nace na fasa ne shiyasa yake amsa min".

* * * * * * * * * * *

Aban garen Zuby kuwa bayan sun gama sheke ayar su tashi sukai suka shiga wanka kamar kullum nan ma saida suka bata lokaci suna tsotse-tsotse kana suka fito fiskokin su dauke da nishadi suka shirya cikin wata doguwar riga me ruwan kwai tana da laushi matuka Lubancy tace "ina zamu yau?"

Zuby tace "gurin shakatawa man, yauwa naga baki hau online ba meyisa".

Lubancy tace "banida data ne, wani abun ya faru ne ?"

Zuby tace "kwarai ma kuwa ina wannan yarinyar da kika sameni ni da ita jiya?".

Tace "eh na tuna ta".

Zuby tace "ashe yar lekan asiri ce yanzu haka tayi left a kungiya kuma ni fa cemin tai Tubulas ce ta kawo ta ashe karya tai min".

Lubancy tace "nifa shiyasa tun na kalli yarinyar naji batai min ba kwata-kwata kuma yanzu wani matakin aka dauka?".

"Har yanzu dai ba'a samu mafita ba kasancewar wa'innan tsinannun dokokin kungiyar na aiki, ke nifa abun ya fara isa ta gashi yanzu wlh ina cikin damuwa" Zuby ta fada tana sauke ajiyar zuciya

Kusa da ita Lubancy ta matso ta ce "kawa ta me ke damun ki fada mun naji ko zan iya miki magani".

Nan Zuby ta kwashe labarin komai yadda sukai da Abba ta fada mata hankalin Lubancy a mutukar tashe tace "da matsala gaskiya ya zama dole a fada wa yan kungiya saboda su taimaka mana da shawara kinsan a ka'ida ko aure kai baka daina wannan harkar da zaran ka bari kungiya zata tona maka asiri kuma kinga Maheer ba kalan mazan da zasu dauki haka bane".

Gwauran numfashi Zuby ta sauke tace "wallahi kawa ta shiyasa duk na bi na damu amma dai mu dan jinkir ta kafin mukai maganar kungiya idan Abba ya dawo zan roke shi".

Lubancy tace "to Allah yasa a dace".

"Ameen" ta fada yayin da ta mike ta dauki katon hijabin ta gami da fiddo nikabin ta a jaka tace "kawa tashi ki shirya mu tafi".

"To" Lubancy ta fada yayin da itama tai shiga kamar yadda Zubyn tai kana suka fito

Mama Mama Zuby tai ta kwala mata kira daga can ciki Mama ta amsa

Zuby tace "kina ina ne Mama?"

tace "ina kitchen"

Shiga kitchen din sukai inda suka tarar da ita tana nuna ma mai aiki wani abun gasa kaza da aka siyo shi sabon yayi.

Fuskar Mama dauke da fara'a tace "sai ina kuma?"

Lubancy tace "wallahi Mama mun gaji da zaman gidan ne shine zamu fita ba jimawa zamuyi ba".

Tace "to adawo lafiya"

"Allah yasa".

* * * * * * * * * * *

Wangala-wangalan get yaya Farooq ya wuce guda biyu, kana yai tafiya marar tsayi a bakin wani guri yai farkin danaga an rubuta staff room, kasan cewar na iya karatu amma ban san ma'anar shi ba,

Shiru yadan ratsa mu kana yaya Sadeeq yace "mu sauka man".

Yah Farooq ya fara fitowa sannan sai yaya Sadeeq, bayan ya fito yazo ya bude min kofa yace "fito mun kawo, bayan mun fito office-office mukai ta shigewa har muka isa wani office dan madai-daici, shiga mukai da sallama dauke abakin su yaya, inda muka sami wani malami a zaune da takardu a gaban shi yana ta dubawa, da alamar shine abokin yah Farooq ganin su yaya Sadeeq ya aje abinda yake, yah Sadeeq ya mika masa hannu, yana Murmushi ya amsa, hakama yah Farooq bayan sun gama gaisawa yai musu nuni da su zauna akan wasu kujeru da aka tanade su saboda baki,

Babu abinda nike sai zaz-zare ido ina kara shigewa yaya.take naji bazan iya zama a wannan dokar Dajin ba gaskiya to wai ma in banda  abun mutane taya za azo dokar daji ayi gini ace wai makaranta, ni dai gaskiya bazan zauna ba.

Da turan ci malamin yai min magana, ban san me yake nufi ba yaya Sadeeq yace " ya sunan ki yace?"

Nace "Siddeeqah Suleiman".

Yace "suna mai dadi, ku tashi na raka ku ofishin shugabar makarantar".

"to suka ce yayin da suka mike a tare, muka fito ina ta ganin dalibai na wucewa dai-dai haka, wani office din muka kuma shiga ba laifi ofishin babba ne kuma an dan kawata shi wata mata ce muka gani zaune akan kujera fuskar ta sanye da sirrin gilashi, matar ta manyan ta fara ce sosai kamar ka taba jini ya fito, dagani hutu ya zauna a jikin ta, tana da kyau dan irin doguwar fuskar nan gare ta tana da manyan idanu da dogan hanci ga dan karamin bakin ta, sanye take cikin kayan alfarma tana dan juya kan kujerar da take zaune, da Sallama muka shiga, fuskar ta dauke da fara'a ta amsa kana ta nuna mana kujeru tace mu zauna,  tunda na kalli matar naji ina son ta ban taba haduwa da wanda naji ya kwanta mi  arai lokaci daya kamar ta ba,

To abangaran Hajiya Amina ma haka lamarin yake dan kuwa tana kallon Sadeeq da Siddeeqah taji gaban ta ya fadi, ga kuma kwarjinin da sukai mata har taji  son su da kaunar su ya shiga ranta.

Tana dariya tace "Malam Naseer suwaye wa'innan?".

Yace "ai ranki shi dade sune wa'inda na miki maganar su wannan itace kanwar tasu da akai ma register".

Tace "masha Allah" yan mata ya sunan ki?" Hajiya Aisha tai maganar tana kollon Siddeeqah

"Siddeeqerh" na bata amsa yayin da muka hada ido ta sakar min Murmushi tace "sunan ki babban suna ne kuma nima sunan yarinya ta babba ce".

Nace "Ammi da gaske kema kina da yarinya me suna na?".

Bani da na fadi sunan ba ita kanta Hajiya Aminan yanayin ta ya nuna taji dadin yadda na kira ta, shi kuwa yah Sadeeq mamaki ne ya kama shi.

Tace "da gaske nike yata amma a halin yanzu bama tare".

Nace "to Ammi tana ina?".

Idon Hajiya Amina ne ya kawo kwalla ganin haka yasa yah Sadeeq yace "ke Siddeeqah ya isa haka kin cika tambaya".

Jikina a mutukar sanyi nace "Ammi ki yakuri na daina".

Handkerchief ta d'auka ta dan yi sama da glass din ta ta share kwallar data cika mata ido tace "babu komai yata".

Ya Sadeeq ta kalla tace kai ya sunan ka?". Nai sauri nace "Sunan shi Sadeeq yaya na ne kuma dashi Daddy ya daura min aure yace Wai alkawarin kanwar shi ne data...".

"Ke!!!" Yah Sadeeq ya daka min tsawar da saida naji hantar cikina ta kada a tsorace na dago kai na kalle shi inda na hangi tsan tsar bacin ran sa, ture ni yai daka kusa dashi ya tashi ya fita  fuu kamar zai tashi sama.

Farooq yace "ranki ya dade ki yaquri haka yake zuciya gare sa".

Hajiya Amina da ke saka abubuwa barkatai a ranta tace "ba komai, amma abinda ta fada gaskiya ne dan ta tuna min da wani dana shima haka yake kamar wannan?".

Farooq yace "eh gaskiya ne".

Daga haka babu wanda ya kuma furta wata kalmar

Malam Naseer ta duba tace "Malam jeka dasu office dinka kaina ya fara min ciwo ka bata ajin da ya dace da ita"

"To" yace muka fito, yah Sadeeq na hanga acan jikin mota, harara ya wurga min nima na rama harda murguda baki, a zuciya ta nike cewa ba zai taba canzawa ba".

Bayan mun zauna a office din

Malam Naseer yace "

"A jin ki nawa a makarantar da kika baro?"

Nace "Js 1"

"Shekarun ki fa?"

"sha hudu 14" na bashi amsa a takaice

Wata farar takadda ya dauko ya danyi rubuce-rubuce kana ya shiga yin magana da turanci yah Farooq na bashi amsa bayan sun gama ya miko min wata yar takadda yace "zan sa students su zo su tafi dake yanzu hostel din ku, dan yanzu dalibai suna aji ana karatu amma ke bazaki samu damar yin karatu yau ba saboda an kusa tashi ".

" to" nace bayan na amsa takaddar

Bayan mun fito da gudu na isa gurin yah Sadeeq na kan kame shi ina kuka nace "yaya yanzu tafiya zakai ka barni? saboda ba ka kaunata, kalli fa kaga ni dai na fasa bazan iya rayuwa anan ba".

Rage tsayin sa yai ya tsugunna yace "kowa da haka ya saba kema zaki saba karatu ne kuma ba'a samin sa a sauki saboda haka ki jure sannan banda rashin kunya dan akwai ban banci tsakanin makarantar kwana da ta jeka ka dawo, idan senior tace kiyi kiyi banda kin ji dan idan kika ce zaki rashin kunya wuya zaki ci".

Hawaye ne masu zafi suka cigaba da wanke min fuska na kara rungume shi, yah Farooq yazo yace "sake shi Siddeeqah, ki hakuri ba wani jimawa zaki ba zaku tafi hutu".

Ban sake shi ba na cigaba da kuka na "da kyar ya Sadeeq ya dago ni yana cewa" nace ya isa haka ki daina kuka muje na baki number na kuma insha Allah idan na samu lokaci zan zo na duba ki, kuma idan lokacin ziyara yai su Momy zasu zo".

Nace "to yaushe ne ziyarar?".

"an kusa". Ya bani amsa yana Jan hannu na muka nufi gurin mota

Bayan motar  ya bude ya fiddo wannan katon akwatin kana ya maida ya rufe

Yace "yauwa wannan shine akwatin ki duk abinda kike so akwai a ciki".

Kanshi ya dan dafa yace "Farooq munyi mantuwa fa"

"ta me?". Farooq ya tambaya

"Uniform din ta mana".

  yace "a haba na dauka ka dinka mata ne bari naje in karbo".

Cikin office din da muka baro ya koma bai wani jima ba sai gashi ya dawo da leda a hannun sa

Wasu students ne guda uku suka zo inda muke da turanci suka gaida su yaya suka ce Sir Nazeer ne yace muzo mu kaita hostel din ta, yah Farooq yace "to gata nan dan Allah amana ku kula mana da ita".

"insha Allah suka ce".

Kana ya Sadeeq ya ciro kudi ya bani nace "bana so yaya wanda Daddy ma ya bani suna gida na baro su".

Yace "ki amsa ki nada bukatar su".

Duk yadda yaso na amsa ki nai ba yadda ya iya wasu kudin ya ciro yabawa yan matan yace "wannan naku ne ku raba wannan kuma nata ne idan tanada bukatar wani abun sai ku bata".

"To" suka ce yayin da suka shiga Jan akwati na

yah Sadeeq yace ce "to Siddeeq zo ki amsa number kada na manta mota ya shiga ya dauki memo da biro ya rubuta number ya miko min na amsa

yace" sai na dawo duba ki Allah ya bada sa'a".

Ameen yah Farooq yace inda shima ya shiga mota hannu nai ta daga musu har saida naga sun Kule min sannan na daina na kalli wa'innan yan matan guda uku nace "ina zamu yanzu?"

Ba wanda ya tanka min suka cigaba da Jan akwatin da kamar na daina bin su sai dai nace bari naga gudun ruwan su

* * * * * * * *

Follow

Comment

Vote

NI DA YAYA SADEEQ

·٠•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·

Not edited

              Chapter 29

_____Iska ce mai dadi take ta kadawa tako ina saboda yawan bishiyoyin gurin, dalibai sai zirga zirga sukeyi, can na hangi wasu dalibai su biyu durkushe akan gwuiwoyin su, wata budurwa ce mai Jan dan kwali ke ta zabgar su kamar ta samu bayi da alamar yaran da ake duka magiya suke a kyale su saboda naga sai daga hannu sukeyi alamun ban hakuri. Sai da muka matso dab da wa'innan matan naga wata zabgegiyar bulala ce ta darbejiya a hannun mai dukan, take naji na tsane ta raina ya shiga kuna zuciyata nayin radadi, yaran da ake duka duk sunyi laushi idan su ya furfuto waje, adai-dai inda mai dugan takep wa'innan yan matan da aka hadani dasu suka tsaya, ba shiri nima naci burki.

Wannan firifet din tana ganin mu tayo kan mu tana dariya tace "sista Zamra daga ina haka". bata lura dani ba, dan kuwa na dan boye a bayan daya daga cikin wa'inda aka hadani dasu

Wacce aka kira da Zamra tace "wallahi daga staff muke"

Daya daga cikin matan da muke tare tace "ke dai Jamlah kullum kina cikin duty ko gajiya bakyayi wallahi da akwai kanwar ki a makarantar nan sunan ta sorry dan ta gama kadewa".

Wacce aka cewa Jamlah tace "hhhmmmm Saudat kenan ai shiyasa naki bari a kawo Sajida yanzu haka kano aka wullata".

Wacce nike bayan ta ce ta goce sai alokacin Jamlah ta lura dani dago kai nayi muka hada ido take naji gaba na yai mummunan faduwa har saida na sa hannu na dafe kirji na saboda yadda yake buga min.

Ita ma a bangaren Jamlah kusan haka taji faduwar gaban, sai dai bai kai nawa bugawa ba kallon kallo mukayi har saida Wasilah tace "yaya dai Jamlah kin San ta ne?".

Da sauri Jamlah ta dauke idon ta daga gareni tace "a a ban san ta ba naga dai tana kama da Wanda nasani ne".

Zamra tace "koda naji dan new commer ce yanzu haka hostel zamu kai ta".

Murmushi Jamlah tai daya kara fito da kyawun ta tace "yakamata ku han zarta kaita dan kuwa dole muyi mata welcome to......". Bata gama karasawa ba Wasilah tace "wai ke Jamlah wace irin muguwa ce? na lura Sam bakya jin dadi idan baki ci zalin yayan mutane ba to wallahi wannan bazaki dake ta ba idan ko kika dake ta duk abun da ya faru dake ke kika ja ma kan ki"

Tana gama fada tajanyo hannu na muka fara tafiya ganin haka yasa senior Zamra da Saudat suka biyo bayan mu Jamlah taji zafin kalaman da Wasilah ta fada mata don haka ta kuduri aniyar ramawa tako wani hali ne dan ba'a yi yar da zata gaya mata magana ba, kuma saita daki bushashshiyar yarinyar taga uban waye ya tsaya mata da har suke takama, tasan indai kudi ne ba za'a fi uban ta ba, ranta bace ta wuce batare da ta kumu kallon wa'innan yaran da take duka ba.

Munyi tafiya mai nisa sannan muka zo bangaren hostel din wani dogon daki ne muka shiga ba laifi dakin yana da girma bashida wani fadi can amma akwai tsayi, gadaje ne ajajjeri ko wanne gado sama da kasa mun samu tsira run dalibai a ciki, mun danyi tafiya a cikin hostel din saida muka kusan zuwa karshen shi sannan muka tsaya a saitin wani gado hannu senior Zamrah ta dora a saman gadon ta taba tace "Alhamdu lillah wai me sunan ki ne?" nace "Siddeeqah". Sadaut na dariya tace "masha Allah sunan kanwata ne wacce take bina insha Allah zan kula dake kamar yadda zan kula da kanwa ta" sannan ta nuna min saman gadon tace "kin ga wannan gadon shine gadon ki" ta kuma nuna min kasan tace "wanna kuma na Fadila ne ita ce makociyar ki, wani dan soko ta nuna min dayake tsakanin gado da gado a gyare na ganshi tsaf kamar dakin amarya yaji ado da kyale kyale harda sif tace" nan kuma corner ce anan zaki aje akwatin ki naga baki zo da bokiti ba a kudin ki da yayan ki ya baki zan sa a siyo miki ".

To nace yayin da nafara taka matakalar da zan hau saman gadon ina dariya na dare abu na sai naji kamar mafarki nike saboda wannan sabuwar rayuwar.

Akwatin suka ajiye a cikin corner din sannan sukai min sallama suka wuce

Wata yarinya naga tazo ta zauna akan kasan gadon mu, hakan yasa naji ajiki na ita ce Fadila Saukkowa nai na mika mata hannun mukai musabaha tana dariya tace "sannu Sista ni sunana Fadeela kefa?" ta kare tambaya ta tana kama hannu na ta zaunar dani a bakin gadon ta

Bayan na zauna nace "nikam sunana ba na yayi bane ke nifa da ana canza suna da tuni na canza dan wallahi ji nike idan an kira ni kamar tsohuwa aka mai dani"

Fadeela na dariya tace "ba wani nan halan ma sunan ki yafi nawa fada min dai naji sai na yanke hukunci"

Nace "wai Siddeeqah fah".

Rungumoni tai tace "sister sunan ki mai dadi wallahi sunan ya min sosai ina kuma son mai sunan, ke in takaice miki in Allah yasa nai aure na haihu sunan zan sama diya ta kin San ko saboda me?"

Girgiza mata kai nai alamar "a a"

Tace "saboda in faranta ma Ammi sunan babbar yarinyar ta ne data bata har yau mun kasa gano ta, ko dayike gaskiya ba wani bincike mukai ba, saboda ko maganar Ammi ba taso da anyi mata maganar duk annurin da yake a fuskar ta za kiga ya dauke, amma idan ka nutsu da kyau ka lura da yanayin ta zaka fahimci tana cikin damuwa lokuta da dama idan na kalli kwayar idon ta ina hango soyayyar diyar ta a tare da ita duk da kamin Daddyn mu ya rasu ta haihu dashi yan biyu mace da namiji yanzu haka zasu kai shekara bakwai kuma kasancewa ta marainiya gaba da baya yasa Ammi ta cigaba da kula dani, saboda mahaifiyata ta a gurin haihuwa ta Allah yai mata rasuwa, kafin Daddy na ya auri Ammi yar aiki ya barwa ragamar kula dani saboda ita kanta mahaifiyata marainiya ce bata da kowa sai Allah, ba karamar wuya nasha a gurin Atine yar aiki ba saboda Daddyn mu ba mazauni bane idan yana gari kar kiga yadda Atine ke kulawa dani tun ban da wayau har na fara wayau bayan wasu shekaru na saba da wuyar da Atine ke bani duka da zagi wanka da ruwan sanyi horo da yunwa saka ni aikin da yafi karfi na, kwatsam sai wata rana na kwanta rashin lafiyar da banyi tunanin zan kuma bude ido na na ganni a duniya ba, da farko Atine tayi banza da lamari na ta cigaba da da tsangwama ta, bayan kwana biyu tazo ta sameni a bayi na kwance ko numfashi bana yi ruwa ta dibo ta shiga kwara min, amma ko alamar farfadowa banyi ba, kusan sau uku tana kwara min amma ko motsi banyi ba hakan yasa ta kwarma ihu game da fadin waiyo ni Atine na shiga uku, takai ta kawo ta rasa mafita can dabara ta fado mata akan ta gudu ta barni tasan idan aka kama ta baza ta tsira ba, haka kuwa akai tuni ta shiga dakin ta bata dauki kaya ba sai jakar ratayawar ta kamar mara gaskiya ta fito ta danyi waige waigen ta kana ta fara tafiya cikin sanda koda ta fito harabar cikin gidan sai tai tozali da abinda yasa zuciyar ta ta buga, wato Daddy ne ta gani tare da escorts din shi da alamar yanzu ya shigo gidan, tana sosa kai ta karasa inda yake kamar yadda ya saba yi mata aduk sanda suka hadu haba haba duk da kasancewar shi babban attajiri amma Sam baya kyamatar talakawa hasali ma kullum cikin kyautata musu yake tare da marayu, bayan Atine ta gaishe shi yace "ina zaki ne haka Atine naga kamar shirin fita ne a tare da ke? keda tunda kike a gidan nan baki taba fita ba saida izini na gashi yanzu ma ba dan mun hadu ba sai dai naga ba kyanan to ina kika bar min er leleta? mummunan mafarki nai a kanta shiyasa na dawo nigeria duba lafiyar ta saboda na samu nutsuwa"

Tuni gumi ya fara karyo wa Atine kan kace me saman kan hijabin ta ya jike jagab kasancewar a tsakiyar rana suke alhaji bai kawo komai ba ganin Atine bata da amsoshin shi yasa yace "wai lafiyar ki ko mutuwa akai miki naga ba kamar yadda na saba ganin ki ba".

Muryar Atine na rawa tace "eh ranka shidade Baba ta ce dama ta rasu to shine zan....."

Bata karasa ba ya daga mata hannu gami da fadin "haba Atine Ince ba yau nike da ke ba, ai bai kamata ki tafi haka ba da kin sanar dani ko a waya ne sai nasa a kai ki, amma yanzu muje na sallame ki tunda ina gari sai ki bar min shalele ta".

Gaban Atine na faduwa ta juyo cikin gidan tasan yanzu bata da halin fita tako ina masu tsaro ne gwara ta shigo in yaso ko bariki ne sai tai mishi da wannan shawarar ta samu nutsuwa, da karfin ta ta dawo gidan duk kuwa da karfin hali take kar ki tona kiji kasan zuciyar ta.

Akwai kofa ta musamman da Daddy yake bi saboda haka tanan yabi bai zarce ko ina ba sai ban garen sa inda ya gaji da kayatuwa dan zubin gidan sarauta akai mai kayan kawa kuwa da alatu ba'a magana saida yai wanka ya kintsa sannan ya fito dama ka'idar sa indai yana nan daukata yake mu tafi gurin cin abinci, aduk irin ranar sai najini sakayau kamar ina aljanna motsi kadan zanyi Daddy na zai ce me kike so saboda yana mutakar so na da kauna ta kuma tunda nike ban taba bude baki nace mashi ga abunda Atine take min na rashin kyautatawa ba

Koda fitowar sa sunana ya shiga kwala kira shalele shalele haka Daddy ke kirana, jin shiru yasa ya zauna akan daya daga cikin kujerun falo ya dauki rimot ya canza channel, sunan Atine ya shiga kira a karo na uku sai gata ta fito daga dakin ta da injin shara a hannun ta tana ja tace "Alhaji kira na kake dan na kunna inji kasan kara bazai bari inji ba"

"eh" Daddy yace mata "shalele zaki kira min dan ina ta kiran ta naji shiru nasan yanzu ba lokacin baccin ta bane"

Duk da Atine taji mugun faduwar gaba amma sai ta dake tace mai "to"

TA shiga bangare na ko bayin da nike bata kalla ba ta danyi shawaginta ta dawo harda durkusawa akasa tace "Alhaji ban ga Fadeela ba na duba ko ina kuma da zan fita anan falo na barta tana kallo kuma nace karta je ko ina"

Da sauri Daddy ya mike yana fadadin "what? bazai yuyu ba Sam wannan ba mai yuyuwa bane"

Wani madanni yaje ya danna a jikin bangon falon , kan kace me saiga escorts dinsa nan sun shigo ce musu yai "Fadeela ce ta bata ku nemo min ita tana cikin gidan nan nima zan tayaku dubata"

Atine ya kalla yace "ina da ina kika duba?"

Bakin ta na rawa tace "ranka shidade iya bangaren ta kawai na duba"

Gyada kai yai alamun gamsuwa kana ya dubi daya acikin escort din yace "kai da ita ku tsaya anan ku kuma ku shiga ko ina ku duba banda bangare na"

Haka sukai ta binceka lungu da sakon gidan in takaice miki har farfajiya suka fito amma basu same ni ba, daya daga cikin su ne yai bangaren siminful shiga ciki yai wai ko zai sameni amma shiru, cikin rashin nasara duk suka hallara a falon idon dadi ya kada yai jawur saboda tsananin tashin hankali, iya kaduwa Atine kam tayi, dan kallo daya zakai mata ka fahimci rashin gaskiya atattare da ita

Komawa kan kujera Daddy yai jikin sa babu laka tagumi yai ya rasa ina zai sa rayuwar sa kadde ace mafarkin da yai ne ya tabbata idan kuwa hakane ya ci amanar Maryama wato mahaifiyata kenan gaban sa ya cigaba da tsanan ta bugu, can yai zunbur ya mike yana fadin "kun duba toilets kuwa?"

Gabad'ayan su suka bashi amsa da "a a"

Kafin yace suje su duba tuni kowa ya fad'a ciki duk inda suka san da bayi sai da suka buda kwatsam Daddy ya buda toilet din da ke daki na mai zai gani gudan jinin sa ce kwance a bandaki ko numfashi ba tayi, cikin jarumta ya qarasa ciki, zufa na keto mai dago ni yai kaina yai baya luu, cire mun jikakkun kayan jiki na yai kana ya fito dani durowa ta ya bude ya fiddo min wata doguwar riga fara kyal ya sanya min a kan gado ya shin fidar dani tsabar rudewa ya rasa me zaiyi, can ya tuna da wayar sa daya bari a falo, futowa yai ya dauka bai tankawa kowa ba ya dawo daki na, number Dr Tameem ya shiga laluba ringin biyu ya dauka Daddy bai wani tsaya amsa gaisuwar da Dr Tameem ke masa ba ya shiga shaida masa dalilin kiran nasa da cewa lallai-lallai yana son ganin sa yanzu.

To bayan Daddy ya kashe wayar zirga-zirga yashiga yi, yana cikin wannan yanayin Dr Tameem ya shigo ya iske sa, bayan Dr ya kalli fuskar Daddy ya dauke kai saboda kallo daya zakai wa daddy ya baka tausayi, inda nike kwance Dr ya nufo dama da akwatin gwaje-gwajen sa yazo nan take ya shiga dubani da bani kulawa ta musamman, cikin kwarewar aiki irin na Dr Tameem, da farko yaji tsoro sakamakon jin numfashi na baya harbawa, cikin ikon Allah da ambaton Allah da yake ya kara daukar hannu na ya kai kusan 4 minutes kana ya saki hannun yana mai godiya ga Allah jin bugun zuciya ta ya dawo, da sauri da sauri ya cigaba da dubani yana kuma fahimtar inda matsalar take kan kace me tuni yasa na fardado daga dogon suman da nai amma ban bude idanu na ba Daddy ne ya matso kusa dani yace "shalele ki yakuri kada ki tafi ki barni bani da kowa sai ke".

Naji abunda Daddy ya fad'a amma bazan iya bashi amsa ba saboda baki na yayi nauyi

Dr Tameem ne yace "kar ka damu Daddy da ikon Allah zata warke harma tafi da lafiya yanzu baza ta iya magana ba saboda rashin kuzarin da yake tare da ita bari na gama duba ta saboda naga abunda yake damun ta".

Nan gefe na Daddy ya zauna yanzu ya dan samu nutsuwa sai dan abunda ba'a rasa ba.

Atine kuwa tunda taga shigowar Dr take ta zagawa ban daki dan ta zaga yafi a irga, ta ruga ta san kashin ta ya bushe.

Bayan wasu awoyi da basu haura biyu ba Dr Tameem ne zaune akan sif din gefan gado na yayin da Daddy ke zaune a bakin gadon Dr yace "nayi mamaki da na sumu Fadeela na dauke da cutar ulcer da limoniya gashi ulsar har tana nema tazama kuronik".

Shiru Daddy yai saboda ya rasa abunda zai ce ido ya kura min yana jin tausayi na har cikin ransa ledar ruwan da ake kara min ya kalla ko rabi bai yi ba ido na a limshe ina bacci saboda allurar baccin da akai min.

Kallon Dr Tameem yai yace "na dade ina zargin wannan nanny din bata ba Fadeela abunci, saboda aduk lokacin dana fita da ita restaurant karka ga yadda take cin abinci kamar wata mayunwaciya, amma saboda na kara tabbatar wa zanje na duba ctv camera na".

Dr yace "yafi ma dan wallahi idan muka ga itace silar wannan ciwan sai na Illata ta, saboda wannan tsantsar rashin imani ne da butulci kaduba irin wannan ni'ima da take ciki komai fa yi mata kake Daddy". Ya kare maganar cikin takaici

Numfasawa Daddy yai yace "Tameem kenan har yanzu kai yaro ne baka gama fahimtar macece duniya ba to acikin wannan duniyar da kake gani akwai mutane masu son zuciyar su, marasa godiya ga ubangijin su, acikin su akwai wanda da ubangiji zai bashi gabad'aya arzikin duniya, baza su taba gani bare su gode masa ba,  da za su samu haram ci za suyi saboda zalinci da son kan su, shiyasa a kullum nike kara godewa Allah dayasa inada ga cikin bayin sa masu godiya saboda kaga duk wanda baya godewa mutane to baya godewa ubangijin sa".

Dr Tameem yace "Hakane Daddy wallahi son zuciya yai wa mutane yawa ko a gurin aikin mu ina ganin masu mutukar son kansu"

Daddy yace "Allah ya ganar dasu damu baki daya"

"ameen" Dr ya fad'a

Kiraye kirayen sallar la'asar aka shiga yi saboda haka Daddy ya Kalli Dr yace "kaje kai sallah ni yau bazan samu damar zuwa masallaci ba, idan ka fita falo kace wa escorts din suma suje suyi sallar amma abar mutane uku su tsare Atine".

"to" ya fad'a yayin da ya mike ya fice, kamar yadda Daddy yace mai haka ya sanar musu kana ya bar gidan.

In takaice miki labari koda Daddy ya idar da sallah bayan Dr ya dawo ya bar masa ni shi kuma ya tafi bangaren sa, da shigar sa inda yake aje computer dinsa ya nufa bayan ya dauko ta ya nemi gefen makeken gadon sa ya zauna, dayike komai na gidan asete yake da kwamfutar sa, ba tare da bata lokaci ba ya shiga dubawa bayan wasu a wanni saiga idon daddy na zubar da kwalla, cikin sauri ya rufe computer saboda annune inda Aitene tasa kafa ta shuta ni na bugu da gini sai ga kaina ya fashe yana jini hakan bai ishe ta ba sai da ta kara min da duka, har yanzu Daddy mamaki yake bai taba zaton Atine ba yar halak bace kan sa ya dafe yace "oh ke duniya ina zaki damu ace duk wanda ka bawa amana sai yaci babu masu tsoran Allah, a gidan ka kana tsoran iyalan ka a waje kana tsoran mutanen da kake mu'amula da su, saboda rashin amana da yadda.

Mikewa yai jiri na diban sa ya fito bai daki na ya dawo inda ya samu Dr na ta faman danna waya, da ganin Daddy ya aje wayar saboda yanayin Daddy ya nuna yana cikin damuwa.

Dr ya dade yana tambayar Daddy, amma Daddy ya gaza cewa komai.

Saida ya zauna ya samu nutsuwa kana yace "ka kira min Dpo Babawo kasanar dashi yar aiki tayi yunkurin kashe yarinyar da take kulawa da ita".

Hannun Dr na rawa ya lalubi wayar shi, tuni shima idanuwansa sun kada sunyi jawur, number Dpo Babawo ya lalubo ya danna kira ta dade tana ringing sannan ya dauka, daga can bangaren yai magana da turanci, shima Dr cikin turancin ya mayar mishi.

To bayan ya kashe wayar ba'a wani bata lokaci ba sai ga motocin rundunar yan sanda tazo, da yike anguwar manya ce kullum cikin jin jiniya suke saboda haka mutanen unguwar basu kawo mai laifi aka zo kamawa ba.

Ita uwani tunda taji jiniya hanyar cikin ta ke kadawa sai muzurai take, bata gama sarewa ba sai da taga yan sanda sun shigo mata biyu maza uku, tana ganin su ta mike tana fadin "na tuba ku yafe min Alhaji Alhaji dan Allah kayi magana a kyale ni, a dai-dai lokacin Daddy ya fito daga daki na Dr na bayan sa kallon tsana Daddy yabi Atine dashi yace" tur da halin ki dama tsintacciyar mage bata mage, da izinin Allah sai kin girbi abinda kika shuka ku tafi da ita idan kun gama binciken ku ku mika ta koto dan sai na tabbatar da na kwatar ma yarinya ta yancin ta".

Tuni yan sanda suka tasa keyar Atine zata tsaya mu gaddama suka tara mata gajiya tare da saka mata ankwa a hannu suka ce mata "indai ta kara magana sai sun harbe ta". Da haka suka kashe bakin ta amma da sai ihu take tana ta fadin "ta tuba"

bayan yan sanda sun tafi da ita sunyi binkicen duk da yakamata kuma sun kama ta da laifi dumu duma, saboda haka suka mika ta koto inda aka yanke mata hukuncin shekara 25 agidan yari tare da horo mai tsanani kuma babu beli.

Tun daga nan Daddy shi ke kula dani duk wata dawainiya ta shine dan ya hakura da fita kasashen da yake shike kaini makaranta kuma ya dauko ni, bai yadda da kowa ba gani yake za'a kuma cutar dani.

Kafin kice me nayi kyau nayi bul-bul dani da kuwa kamar ki hure ni na fadin

Bayan wasu watanni Daddy ne a cikin masallaci bayan sun idar da sallah Ladan yace yana da magana, wasu aciki sun fita yayin da wasu kuma suka zauna, acikin wa'inda suka zauna harda Daddy na ladan ne ya fara jawabi kamar haka "sama da shekaru biyar da suka wuce na tsinci wata mara lafiya cikin ikon Allah nai ta nema mata magani saboda na lura sammu ne akai mata, to Alhamdu lillah yanzu ta samu sauki amma na tambaye ta ahlin ta tace bata da kowa to shine nike so naji ko akwai wanda zai iya cigaba da dawainiya da ita, saboda naga bata sakewa a gida na uwar daki na kullum cikin tsangwamar ta take, Duk da Daddy na tsoro bai hana shi cewa ba "ala gafarta malam babu damuwa zan dauki nauyin ta". Kasancewar Ladan yasan Daddy yasa yace "ah Alhaji Hamza mai zai hana ka aure ta tunda naga baka da mata ga marainiyar diya kana tare da ita, duk da na ga abinda ya faru kwanakin baya a labarai da mai aikin ka ta kusa kashe ta, yanzu sai ka sama mata uwa ai"

Gabad'aya yan masallacin sunyi na'am da batun sukai ta bawa Daddy kwarin gwuiwa, "to ba'a kin ta mutane" daddy ya fad'a ya kuma dora da cewa "amma ni yanzu tsoran matan nike gani nike kamar duk daya suke"

Nasiha Liman yai mishi daga bisani aka daura auran Daddy da Ammi abisa sadaki mafi karanci, bai kuma dawo gida ba sai da amaryar sa wato Ammi.

Sanda Daddy ya shigo na gansa da Ammi tambayar sa nai wace ce? Yace "Ammin ki ce". Da gudu naje na rungume ta ina jin son ta da kaunar ta har cikin raina, tunda ga ranar nima nai uwa farinciki na da wal-wala ta ya karu banda wata matsala saboda yadda Ammi ke bani kulawa ko mama ta na da rai iya abinda zatai min kenan, sosai nike jin dadin zama da ita kuma tana iya bakin kokarin ta akan tarbiya ta, har ta samu ciki, duk da itama wajen haihuwa taji jiki har nafara tunanin ko itama zan rasa ta ne, sai kuma Allah ya tashi kafadar ta, ta haifa min kyawawan kannai Wudat da Walid

Wannan shine takai-taccen tarihin Fadeela

Ci gaban labari

Kallo na fadeela tai tace "kin San wani abu kuwa?"

"a a". Na bata amsa

Tace "kina kama da Ammi har muryar ku iri daya wallahi"

Zanyi magana kenan saiga firifet sun shigo da bulala a hannun su, daya daga cikin su tace "eh lallai kune ferarrun yan iska ko da ba zaku wuce kitchen ku karbi abinci ba tun dazu aka buga ringing"

Yo ni dai ban san ya abin yake ba hakuri Fadeela ta shiga basu, yayin da ni kuma sai zare ido nike,duk magiyar da Fadeela tai musu bai sa sun kyale mu ba

Wata gutunwa a cikin su tace "wallahi baku isa ba Kuje ku karbi abinci kuzo kuyi mana wanki dan baku isa ba"

Kallon fuskar ta nai kamar kai amai, ban san sanda dariya ta kwace min ba, harda rike ciki, ina cikin yi naji saukar bulala tsui-tsui ban san sanda na kwarma ihu ba ina kiran sunan yah Sadeeq.

Cikin bacin rai tace "idan ma uban Sadeeq zaki kira kin dade baki kira ba da ganin ki baki da tarbiya agidan ku ba'a koya miki ladabi ba kin ja ma kanku wallahi bayan wanki da zakuyi sai an muku wankan jego".

Na bude baki na rama kenan Fadeela tai saurin toshe min, ta hanyar sa tafin hannun ta a baki ba

* * * * * * * *

Na gaji da typing zan dakata anan kasancewar bana publish kullum yasa nike yin typing da yawa amma don Allah ku aje min comment saboda ta hakan ne zan samu kwarin gwuiwar cigaba da rubuta littafin saboda kun san wannan shine farkon littafi na to yin comment don fadar ra'ayoyin ku shike bani karfin gwuiwa har naji labarin na shigar ku kuma kuna fahimta ta dari bisa dari

Please following Vote Share

NI DA YAYA SADEEQ

•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

No editing

Chapter 30

_____fita sukai suna huci, ni kam raina gabad'aya ya gama baci, kafad'ar Fadeelah nadafa ido na cike da kwalla nace "wai dan Allah a haka kuke rayuwa na fahimci da kiyi laifi da karkiyi duk daya, idan jinin ki bai hadu da su ba sai suyi ta jibgar mutum, ni gaskiya bazan iya dauka ba, haka kawai a gidan mu ba'a dake ni ba sai anan wasu katunan banza su rinka bugu na".

Fadeelah tace "uhm Siddeeqah kenan wannan ma kadan kika gani amma ahankali zaki cigaba da fahimta, kuma kamar yadda kika ce idan fa jinin ki bai hadu da su ba kin shiga uku, musamman ma suga kina da kyau to sai kin fi banuwa, tashi muje kar wasu su zo, su ganmu mu kara laifi".

Mikewa nai zuciya ta babu dadi yau daya ko yinin arziki banyi a makarantar ba duk ta gundure ni.

Muna cikin tafiya muka ji ana kiran Fadeelah da sauri Fadeelah ta waiga dan ganin wacce take kiran ta, aikuwa tai sa'a dan batai mugun gani ba school Momy dinta ta  gani, da sauri taja hannu na muka isa gurin ta rungume ta Fadeelah tai tace "Momy Halima wallahi tun jiya nike zuwa room din ku amma sai su senior Dijah su hana ni shiga". Ta karasa maganar cikin yanayi na damuwa

"ke kada ki damu dama naji ajikina kin zo kin barin ki sukai saboda na tambaye su suka dunga yimin hanya-hanya" a cewar Momy Halima

Kallo na tai muka hada ido tace "Fadeelah kenan, ai dama na fada miki dole wataran zaki nemi kawa, gashi ba'a dau wani lokaci ba har kin gaji da yawo ke kadai, amma dai diyar firinciful ce ko dan ga kama nan?" Momy Halima ta kare maganar cikin sigar tambaya

Fadeelah na Murmushi tace "wannan fa sabuwar zuwa ce yau aka kawo ta kuma ba diyar Firinsifal bace amma dai hostel din mu daya kuma sai naji ta kwanta min a rai, yanzu haka kitchen zamu amsar abinci dan su senior Habiba sun rutsa mu a hostel" nai dai ta labarta mata abinda ya faru, cizan dan yatsa Momy Halima tai ta ce " Allah ya saka mata amma ba wani wanki daza kuyi musu ku zo muje room din mu"

Binta mukai muna tafiya tana mana hira sai dariya muke

* * * * * * * * * *

Zaune suke cikin gurin shakatawar, Lubancy ce ta dubi Zuby ta ce "ni kam kawata kin yi waya da Sadeeq kuwa?"

Sai alokacin Zuby ta dago kanta daga danna wayar da take ta ce "a a wallahi nayi ta kiran sa bai dauka ba, banyi tunanin yana da bakar zuciya ba sai da wannan dan abin ya faru".

"kada ki damu nasan bai huce bane amma tunda yana son ki dole idan ya huce zai daga miki kawai dai ki cigaba da kiran sa" A cewar Lubancy

Kai Zuby ta daga alamun gamsuwa

Suna nan zaune wata matashiyar budurwa tazo wucewa, sanye take da dogon hijab amma bai kai kasa ba kuma fuskar ta sanye take da nikab, ga kuma bakin glass ta sanya, yanayin ta ya nuna kamar tana sauri, saida tazo gab da su Zuby wata leda dake hannun ta ta fad'i, ai kuwa takardun dake cikin ta suka watse, tsugunnawa tai ta fara kwashewa amma sai dai bata gama ba wayar ta ta fara ringing, daga wayar tai ta bar kwashe takar dun ta kuma yi tafiyar ta abun ta.

Gefan kafar Zuby Lubancy ta kalla tace "ke ga wata nan kusan kafar ki".

Zuby ta ce "me?"

Lubancy ta ce "kardun waccan da suka watse dauko mu gani"

Hannu Zuby tasa ta dauko, har zata mikawa Lubancy sai taga kamar rubutu ne aciki sha'awar karantawa taji, saboda haka ta shiga karanta abinda ke ciki kamar haka

"tabbas ranar nadamar ki ta kusan zuwa bama ke ba da duk wasu masu aikata mummunan dabi'a irin taki na rubata wannan sakon ne saboda nasan zai iso gareki".

Ras-ras gaban ta yai mummunan faduwa, mikewa tai cikin hanzari tana fadin ina take ina zan ganta, hanyar da taga wannan matashiyar tabi ta shiga bi, da ganin haka Lubancy itama ta mike ta biyo bayan Zuby tana tambayar ta lafiya? Menene? me yafaru? Haka ta jero mata tambayoyin ajere, Amma Sam Zuby ta kasa bawa Lubancy Amsa har bakin titi suka fito amma ko alamar ta babu,

Mai keke nafef ne yazo wucewa, Lubancy ce ta daga mai hannu yai faking, shiga sukai kana Lubancy ta fada mai unguwar da zai kai su.

* * * * * * * * *

Su Sadeeq ne a hanya sai sharara gudu yake duk da sun shigo garin kaduna amma bai daina gudu ba, saboda yaga Farooq bai gudu shiyasa tun acan, ya amshi tukin motar, kuma gashi sunyi sauri sosai daka kalli Sadeeq zaka san baya cikin damuwa

Farooq ne ya dube shi ya ce "kai mutumi na yanayin ka ya nuna kana cikin wal-wala fa, wai maye sirrin a bani? A sammini nima in tafi ina nishadi" ya fad'a yana duban abokin nasa

Saida ya kara gyara zama ya ce "Farooq kenan bai kamata ka tambayi sirrin farin ciki naba saboda nasan ka sani duk da nayi mata alkawarin ba zanyi aure ba har sai ta gama makarantar ta na saketa, amma wallahi kar ka tona zuciya ta kaji tayi fari kal kamar auduga, dan gani nike kamar yau ne zan rabu da kaya,

Sabalo Farooq yai yana kallon Sadeeq yama rasa mai ze cemai, wato sai yau ya kara tabbatar da Sadeeq gara ne number daya, tunda har karamar yarinya tafi shi wayau da hangen nesa,

Dariya Farooq ya shiga yi yana tafa hannayen sa

Ganin dariyar Farooq ta fara yawa yasa Sadeeq kuluwa, dan shi ya tsani rainin hankali, to inba rainin hankali ba maye na dan ya fadi abinda ke cikin ransa zai tsaya yin dariya.

Cikin kulawa ya ce "kai bansan iskanci, ka bude baki sai dariya kake kamar kaga wawan zama"

Saida Farooq yadai-daita kansa kana yace "wani hasashe nai shiyasa kaga ina wannan dariyar, amma ai har gwara naga wawan zama akan abinda na hango nan gaba kadan inda rayuwa".

Kwafa Sadeeq yai bai kara tanka mishi ba, saboda ya gama lura da Farooq dan rainin hankali ne.

A haka suka isa masaukin Farooq, bayan sun wuto gets, fakin Sadeeq ya nemi guri yai, a kusan tare suka fito daga motar kowa hannin sa a sama yana mika, saboda kowannensu ya gaji likis,  ban garan shi suka nufa direct, basu zarce ko ina ba sai bedroom ko takalmi Sadeeq bai tsaya cirewa ba, ya fad'a kan lallausan gadon Farooq yana kiran sunan Allah.

Shima Farooq dan wannan tafiyar data taso mai ne amma da lafiyar gadon zai bi, yanzu kam ba yadda ya iya, takalman sa ya cire ya fad'a bayi bai wani jima ba ya fito, bayan ya gama kintsawa yashiga shirya kayan sa duk wani abu da yasan yana da bukata ko zai bukata saida ya dauka, bayan ya gama shirya komai ya zauna a bakin gadon ya dubi Sadeeq da idanuwan sa suke alumshe kamar mai bacci, ya ce "nifa zan tafi don nagama shiryawa, nabar maka mukullin ne?" Sadeeq kaman bazai kula sa ba, saboda har yanzu bai gama hucewa ba, har Farooq ya fidda ran amsa sai yaga bakin Sadeeq na motsi

" a a ka jirani bari na watsa ruwa sai mu fita tare " wannan itace amsar da Sadeeq yabayar

Kan Sadeeq ya mike wayar Farooq ta fara ringing, ganin sunan abokin aikin su ne yasa ya dauka gami da karawa a kunne, adai dai lokacin shi kuma Sadeeq yashiga bayan gida

* * * * * * * * *

Ahanya muka ci karo da wannan gajerar firifet din, kasancewar bata magana da Momy Halima yasa ta bimu da kallon banza

Kallon Fadeelah nai nace "wai ya sunan waccan abar ne?". Na fada ina nuna inda take

Fadeelah tace "Rafi'a sunan ta, amma Rafsy ake ce mata"

Ina dariya nace "ta ko ci sunan Rafcy din"

A haka muka karasa Room din Momy halima, gado ne guda hudu na gani aciki saboda karamin daki ne, kuma a gyare yake tsaf, ko ina a tsaftace

Har bakin gadon ta muka zauna ta ce" bari na dafa mana Indomie dannima yunwar nike ji".

Wani dan karamin risho naga ta janyo daga karkashin gado, gami da dauko tukun ya, a wani bokiti naga ta dibi ruwa, inda ta bude loka ta dauko indomin, ba awani dauki lokaci ba indomin ta dawu, wani filet ta dauko ta juye mana gaba daya ta ce "Kuje ku wanko hannun ku kuzo muci" to muka ce muka dibi ruwa akofi muka fita, fitar mu keda wuya muka hangi, senior Jamlah inda muke take nufowa, cikin sauri na wanke hannun na dawo room, saboda yadda gabana ke faduwa.

Ko zama banyi ba sai ga Fadeelah tana dariya ta ce" kar dai har kin fahimci Senior Jamlah muguwa ce?". Tai maganar cikin sigar tambaya

Bayan na zauna ita ma ta zauna nace "ba dole ba kin San irin mutanen nan halin su baya boyuwa, koda kuwa sun so boyewa" nan dai na kwashi labarin komai da nagani na fada mata,

Batai wani mamaki ba tace "indai Senior Jamlah ce tayi abinda yafi haka ma, ke wallahi ko ni na tsane ta tsana mai mutakar yawan gaske, kuma kar kiyi tunanin ta taba duka na fa, a a ko daya haka kawai na tsane ta, kuma yanzu haka na hangi kiyayyar ki atare da ita, dan har tambaya ta tai wai maye alakata da ke? Nace mata ba komai, shine ta wuce tai kwafa".

Zanyi magana kenan Momy Halima tace "kubar firar haka ku bari sai munci abinci"

Sosai naci indomin dan dahuwar  tai min dadi

Karrawa naji ana bugawa Fadeelah na kallah nace "ta maye kuma?"

Tace "ta bacci ce maza tashi mu tafi hostel, kuma kada idan munje ki saki jiki kiyi ta sharban bacci, dan wallahi idan lokaci tashi yai baki tashi ba kin kade".

Nace "kai wannan wani irin bala'i ne haka makaranta sai kace wurin horan barayi da kangararru".

Momy Halima tace "kuyi zaman ku anan ke Fadeelah ai kin san ba mai shigowa cikin su koda kuwa karan hauka ne ya cije su ku bari sai la'asar mu fita,

* * * * * * * * * *

Direct Gidan su Zuby mai nafef ya sauke su, ko kudin sa bata tsaya basa ba, Lubancy ce ta biya sa

Koda ta shiga falon gidan babu kowa sai TV da aka bari a kunne yana ta wake wake, zama tai tasa hannu ta dafe kanta, saboda azabar ciwan da yake mata,

Lubancy ce ta shigo, bayan ta nemi guri ta zauna tace "wai don Allah kawa ta meya faru? Ni kin barni a duhu tun dazun sai tambayar ki nike kinyi banza dani, bazan iya jure kallon ki a cikin wannan halin ba, saboda haka zan tafi idan kin shirya fada min kya neme ni, ko ta waya ce "

Ganin Lubancyn da gaske take tafiyan zatai yasa Zuby tai saurin  cewa "dakata zan fada miki". Nan dai Zuby ta kwashe labarin abunda ta gani ta fada mata, cike da mamaki da fargaba Lubancy tace "amma fa wannan lamarin akwai daure kai mutuka, nama rasa ta ina zan fara "

Gwauran numfashi Zuby ta sauke tace "nima tuntuni abin ke yawo a kwakwalwa ta kenan, na rasa me hakan yake nufi?"

Yar aikin su ce tazo shigewa bayan ta gaishe su zata tafi, Zuby tace "kawo mana abin korawa" bayan ta kawo musu Zuby ta dubeta, tace "ina Mama ne? Kota fita ne?".

Rahamatu mai aiki tace " tana ciki ko wata kila bacci take yi" daga haka ta bar gurin

* * * * * * * *

Bayan Sadeeq ya fito daga wanka, durowar Farooq ya bude ya dauki kananun kaya riga da wando na jins, rigar me ruwan blu ce amma lite sai wandon jins baki, yai matukar yi masa kyau daya saka abun ka da mai kyau, bayan ya gama kintsawa ya taya Farooq diban kaya suka sa a bayan mota, suka kuma daukar hanya, bayan sun fito a bakin titi Farooq ya sauke Sadeeq sukai wa juna sallama, saboda ba hanya daya zasu bi ba, Motar haya Sadeeq ya hau inda yace "musu Kawo zasu kai shi" bayan ya sauka a kawo ya kuma tarar motar buruku daga nan kuma bayan an sauke shi ya hau mashin din da yake kaisu cikin kauyen su Inna saboda mota bata shiga, har kofar gida mai mashin ya sauke Sadeeq, inda ya  ciro kudin sa ya bashi, kana ya shiga gida bakin sa dauke da sallama, Inna dake tsakar gida na shan iska tana ganin sa tafara tafi tana cewa "maraba maraba lale-lale da yan birni" karasowa inda take yai, kana ya zauna akan wata kujera data gefan ta, yace "sannu Inna na same ki lafiya?"

Tace "ina lafiya lau mai gida ina yar rigama ta?"

Yace "Inna yar rigimar ki tana nan amma yau kwanan makaranta zatai".

Ido Inna ta zaro waje tace "makarantar kwana ka kaita ne?"

Kai ya gyada alamun "eh"

Inna tace "ina karami ya barka ka kai yarinyar nan inda za'a cutar da ita?".

Sadeeq yaso yace "dama ai baiyi dan taji dadi ba" sai kuma ya tuna mitar Inna,  dan kuwa ta  dungi yi har labari ya koma kunnen Daddy, labari kwa na komawa kunnen Daddy ai ya bani

Kara gyara zama yai, yaita yiwa Inna bayini akan makarantar kwana gwargwadon yadda yaso ya shigar da ita, kuma ta shiga tsaf dan sosai ya tsara ta, ya kuma shaida mata yanzu sun daina fada sun shirya da juna, sosai Inna taji dadin wannan lamarin dan haka tace "akwai wata fura dana dama bari na shiga na dauko maka nasan kana mutukar so" mikewa tai takwaf-takwaf taje ta dauko mai kwarya ta kawo mai, karba yai yayi godiya yace "Inna ni a gajiye nike, bari na je dakina na dan huta".

"to" Inna tace

Yayin da shi kuma yanufi  hanyar soro

* * * * * * * * *

Hudu saura Momy Halima ta tasheni daga nannauyen baccin daya daukeni dan na gaji, da kyar na iya bude ido na, kallon gefe na nai Fadeelah na gani zaune idanun ta sunyi mishi-mishi sai hamma take famanyi, mikewa nai zaune nace "Ash dadin gida kenan wallahi"

Momy Halima tace "maza ku tashi yanzu ba lokacin fira bane"

Haka muka fito daga room din muka tafi hostel din mu, kiran sallah naji anayi nace "lah dama akwai massalaci anan ne".

Fadeelah dake kokarin fiddo da sabon silifas a cikin akwatin ta tace "eh man ai nan da kike gani babu abin da babu don kinga har da islamiya ma, kuma har sauka ake yi"

Daga haka ban kuma cewa komai ba, Alwala muka je mukai muka tafi masallaci.

To da dare kuwa gaza bacci nai don kuwa banda juyi babu abunda nike, da yike bacci barawo ne ban san sanda ya kwasheni ba

Washe garin tun shida Fadeela ta tada ni, saboda nai wanka tace "idan banyi da wuri ba zan makara gurin zuwa class, to bayan nayo wanka nazo saka yunifom yace dauke ni inda kika barni, neman duniya ban ganshi ba, Fadeela na fadamawa tace" to ke a'ina kika barshi?" nace nan saman akwati na fa na dora shi"

Cikin takaici Fadeela tace "ai kuwa gwara ki daina wahalar nema dan an sace inada sabo bari na baki, amma kin San daya bazai isheki ba dole sai kinje office din shugabar majar kin karbo wani,

Cikin mamaki nace" ikon Allah mutum ba shi ya aje abu ba yazo ya dauka".

Fadeela tace "wannan ba abun mamaki bane bari na fiddo miki kisa kada mu makara.

Bayan ta fiddo min na saka, kallo na tai tace" Siddeeqah kinga yadda yunifom din nan suka miki kyau?"

Ido na zaro waje nace" ke dai kin cika zolaya wallahi"

Tace "daga fadan gaskiya".

Nace "ba wani gaskiya ke dai tashi mu tafi, tunda mun gama shiri,

" To" Fadeela tace min kana ta Mike  muka fito, kitchen muka nufa, bayan mun karbi breakfast din guri muka nema, bayan mun gama ci muka tafi class.

Wannan kenan

NI DA YAYA SADEEQ

•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

No editing

Chapter 31

____Kwanci tashi asarar me rai kuma babu wuya a gurin Allah.

a bangaran su Zuby abinda ya faru kuwa shine,

kwatsam wata rana suna cikin gidan da suke yin mitin, kamar kullum yadda aka saba, manyan mata suka zo suka zabe su suna tsaka da sheke ayar su, mai gadin su taji ana buga get koda ta bude matan yan sanda ta gani da bazata iya shaida a dadin su ba, ture ta sukai suka kutsa cikin gidan kai tsaye, har cikin katon falon suka shiga inda suka ganewa idan su zahiri take suka shiga jibgar su, ko wacce sai da taji saukar kulki a jikin ta tasan cewa an musu cune, haka yan sandan suka tarasu a guri guda, can na hangi Zuby da Lubancy sai raba ido suke, koda suka fito motocin yan Sanda ne sunkai goma Sha biyar da DSP Sadeeq ya ke jagoran ta, haka aka tarkata su aka kai su sell, koda labari yaje kunnen Abban Zuby ba karamin cikin tashin hankali ya shiga ba duk da alokacin baya Nigeria gashi bikin ta da Maheer a lokacin bai huce saura wata uku ba, ba shiri ya dawo nigeria, bai zarce ko ina ba sai gidan sa, da zuwa direct dakin Mama ya nufa koda ya buda kofa take kansa ya fara juya masa, saboda abinda ya gani, Mariya ce kwance bisa kan gado ga kartai har biyu suna kwanciya da ita, take ya fara ambatar innalillahi wa'inah ilaihi rajiun, haka yai ta ambatar sunan Allah, Mariya kuwa bata ji shigowar kowa ba sai alamar fita da taji, hakan yasa tace ma abokan shashan cin nata "su dakata, kamar taji alamar mutun" amma sukai burus da ita suka cigaba da aika aikan su, tuni Abba ya kira yan sanda kiran gaggawa, ba'a dauki wani lokaci mai tsayi ba sai gasu, nan ya nuna musu dakin da su mariya suke haka suma aka tarkato su sai police station, anan Abba ya sake ta kuma ya mata Allah ya isa, saboda ta cuce shi kuma ta cucu rayuwar yarsa, yace taje ta gani taci amanar aure, shiko Sadeeq koda yaga Zuby a cikin su baiyi mamaki ba Saboda abokin sa Maheer ya fad'a masa, kuma dama tun sanda sukai fadan-nan bai kuma koma mata ba, hakan yasa da Maheer yace mai ita zai aura bai ji komai ba, Maheer abokin Sadeek ne tare suka gama secondary school din su dake nan Abuja, abunda ya jawo to nan asirin su shine, Sumayya da ake cewa yar leken asirice, ashe kanwar Maheer ce kuma shi yaturo ta tun kamin ya dawo kasar Kamal makocin su Zuby ya fad'a mai abunda yake zargi akan Zubyn, hakan yasa yace kanwar sa tayi basaja taje, abunda basu sani ba har Video tai musu alokacin kuma ita ce wacce ta jefar da takadda a gurin wannan shakatawar, hakan yasa Maheer sanar wa Sadeeq shi kuma ya hada rundunar yan sanda, yayin da Sumayya ta musu jagoranci ta kai su har bakin get din, kunji ta yadda asirin jigagan yan luwadin ya tonu.

koda DSP Sadeeq yazo yana tambayar matan Dalilin dayasa suke yin wannan mummunar dabiar saboda yanaso ya gama hada bayanai ya mika su kotu,

Daga wacce zata ce kawar tace tai sila sai wacce zata ce mijin ta ne baya bata hakkin ta, haka dai ko wacce da abinda zata ce, abinda ya qara bama Sadeeq takaici harda matasan yan mata da bazasu wuce 18 to 19 ba, Zuby dai ba bakin magana saboda yadda take jin kunya ji take kamar ta ha'ka rami ta burne kanta, acikin su wanda yafi tsayawa Sadeeq a rai shine abinda daya daga cikin su tace wai ita da kishiyar ta ne suke yi a gida, har suka shiga cikin wani group na yan madugo zallah, daga nan aka kara buda musu ido, sosai Sadeeq yaji maganar ta dake shi tsoron matan yanzu ya kara kama shi, Allah abin tsoro mata abin tsoro, lalacewar har ta kai ga kishiya ta nemi kishiyar ta, saboda sun maida aure ba a bakin komai ba, sunyi Fatali da darajar sa sunci mutuncin sa, badon Annabi Muhammad ya roka kar a halakar damu ba, da tuni an dade da kifar damu, saboda duk wani abu da aka halakar da mutane akai muna aikatawa, an halakar da wata Al'umma akan tauye mudu da suke, ku fada min shin yanzu bama tauye mudu? An halakar da wata Al'ummar, akan luwadi, shin ku fada min yanzu bama aikatawa, an halakar da Al'umma da dama saboda yawan sabama ubangijin su, amma ku duba fa maye ba'a aikatawa a wannan zamanin, shan giya caca zina luwadi madugo, tauye hakkin wani zagin shuwagabanni cin amana, rashin yiwa iyaye biyayya, zagin malamai, cin dukiyar maraya, da dai sauran su, Allah ya bamu ikon gyarawa, idan muka gyara muma sai muji dadin rayuwar, haka dai yai ta jinjina lamarin yana yin rubuce rubecansa, a farar takarda, shi wallahi mamakin masu luwadi da madugo yake yi ko mai suke ji a jikin juna, ace wai mace da mace namiji da namiji, masifar tayi yawa dole annoba ta damemu shin ko kun sar masifar da yake haifarwa? Wallahi duk wanda ya mutu yanayi bai tuba ba wuta ce Makomar sa. Dan yanzu abin yayi yawa, iyaye ku saka ido akan yayan ku ku lura da tarbiyar su, ko kawa ce idan tazo wajan yarki kika ga ana shiga daki a rufo kofa wallahi ki bincika, zamani ne Allah ya kawo mu dole sai mun dage mun tashi tsaye akan tarbiyar yaran mu, saboda zaki tabawa yarinyar ki tarbiya rana daya wata shegiyar kawa tazo ta rushe.

To bayan kwana biyu kotu aka mika su, inda Alkali ya yanke musu hukuncin shekara goma sha takwas-takwas a gidan yari tare da horo mai tsanani, akace duk wacce hukuncin bai mata ba zata iya daukaka kara.

ita kuwa Mariya da abokanan fasikancin ta hukunci jifa aka yanke musu har sai sun mutu kasancewar su masu aure kuma sukai Zina, oh ni rayuwa ina zaki damu wai kina matar aure wace irin jaraba ce da bazaki kama kanki ki rike mutuncin ki ba, saboda ki samu Aljannar ki Allah dai ya ganar damu.

* * * * * * * * * * Bayan wasu shakaru haka Rayuwa ta cigaba da tafiya cikin hukunci Allah gashi har mun rubuta jarabawar mu ta JSCE,, aminci da shakuwa mai karfi ya cigaba a tsakani na da Fadeela, sosai muke kyautata wa junan mu, dan Ammi komai tare take siyo mana, haka nima komai tare yah Sadeeq ke kowo min idan zai zo min bizitin, haka idan nice naje gida idan zan dawo hutu komai biyu nike zuwa mana dashi, dan sau biyu su Momy da Inna suka zo min, na kyara girma na ban mamaki ni kaina mamakin yadda nai girman nike, idan ka ganni sai kace na kai irin shatakwas din nan, ga wayau na masifa da nai, sosai kama ta da Ammi take kara bayyana, dan dalibai da dama ce min suke diyar firinsifal.

na hadu da Sadiya kanwar yah Farooq a lokacin da yaya Sadeeq yazo min bizitin yasa aka kira ta, itama tun daga ranar muke zumunci amma ita ba hostel dinmu take ba, duk inda ka ganni zaka ga Fadeela da Sadiya haka ake cemana yan ukun Firinsifal, dan da angama karatu muke zuwa ofishin ta, sosai yanzu nike jin turanci dan ko magana da hausa ban fiye yi ba, dan jina nike babbar yarinya.

Senior Jamlah kuwa sun bar makarantar, sunyi candy, kuma koda tana nan ma, ban bari ta dake ni ba, dan kuwa karar ta nakai staff sai dai zagi da tsangwama idan mun hadu, sosai school Momy na Saudat take kula dani, shiyasa ban wani sha wuya ba gashi yanzu har zan barta.

Yau ne muke zana fefar mu ta karshe kuma cikin azumi ne home economy ne ya bada wuya gaskiya, duk wacce ta fito hol zakiga tana goge gumi, bayan na gama na fito na iske Sadiya zaune na jiran mu, nan muka shiga farar yadda fefa tai zafi, muna cikin firar sai ga Fadeela nan itama tace, "wash rabon da fefa ta bani wuya irin na yau wallahi na manta ku tashi muje mu shirya, dan da alamar wasu daliban ma sun fara tafiya".

hostel muka mufa inda a hanya muke ta haduwa da class mate din mu da akazo daukar su , dama duk munyi musayar numbers saboda dayawan wasu daga cikin mu ba nan zasu yi senior ba,

Ahaka muka karasa hostel muka shiga hada kayan mu bayan mun gama muka raka Sadiya itama ta hada nata.

Office din Ammi muka je, da sallama dauke a bakin mu muka shiga inda muka same ta a tsaye tana hada takardu, bayan mun gaishe ta, tana dariya ta kalle ni tace Yata duk kinfi kowa kosawa ko duk zumudin za'a Dande ne? tunda kince acan zakiyi Sallah"

Dariya nai kasa kasa nace, "Allah Ammi ba haka bane kawai kewar gida nike".

Tace "ai na gama ku tashi mu tafi gida daga can sai mu dauki hanyar Abuja"

Dama tuni nayi waya da Yah Sadeeq nace ba sai yazo daukar mu ba, Ammi zata kawo mu, dan tace "tana son zuwa ta gaida Inna saboda ina yawan bata kabarin ta"

A tsakar gidan su Fadeelah muka tarar da kannen ta yan biyu wato , Aysha suna kiran ta da little easha sai Aliyu suna ce mai Dady, haka yaran suka taho suka rungume mu dama mun saba dasu dan ina zuwa gidan idan anyi mana hutu yaya bai zo daukana da wuri ba, muna wasa da dariya muka karasa falon gidan, ciki Ammi ta shiga dan ta shirya haka ma Fadeelah, ya rage da gani sai Easha da Dady da Sadiya sai wasa muke, ahaka Ammi ta fito ta iske mu tace "ina Fadeelan?"

Sadiya ce tace "bata fito ba"

"Fadeelah Fadeelah" Ammi ta kwala mata kira, sai gata ta fito itama tayi fes da ita cikin shigar wata atamfa mai tsadar gaske, atamfar tana da kaloli da yawa a jikin ta mai digo digo, yayin da ta yafo mayafi brown, haka jakar ta da takalmin ta duk brown soboda akwai brown a jikin atamfar, duk da Fadeelah ba fara bace amma tayi mutukar kyau, yayin da Ammi ke sanye da doguwar riga yar dubai mai ruwan kasa ta yana mayafin ta fuskarta sanye da siririn gilashin ta na lura bata rabo dashi, dan ga little Easha nan duk sanda zan ganta itama dashi nike ganin ta,

Ammi ta kalli Fadeelah tace "dadi na dake nawa duk sanda aka shirya tafiya kece a baya".

Fadeelah tace "haba Ammi yanzu haka na dade?".

Ammi bata kula ta ba tace "ku tashi mu tafi rana na dad'a yi"

Dama su little Easha a shirye suke saboda haka muka dauki hanyar Abuja, a hanya muka tsaya a restaurant muka siya abinci mukaci, da misalin karfe biyar na yammacin ranar juma'a muka isa makekyan gidan su Khadija, yayin da Ammi tai hon mai gadi ya bude mata ta sulala ciki, gurin faking din motoci tai faking kana ta bude mana kofa, da gudu na fito ina ihu na nufi cikin gidan Momy da Ummi na tarar zaune suna cin kayan marmari a falo, fadawa cinyar Momy nai, itama kamani tai tana min oyoyo, ban tashi daga kan cinyar ta ba sai ga Ammi ta shigo bakin ta dauke da Sallama, koda Momy ta dago kai da Zimmar amsa sallama, sai tai maza ta tureni ta Mike tana fadin "Amina" ita ma Ammi idon ta zaro tace "Aisha" kollon kallo muka fara bin su dashi, ganin kowannen su idon sa na zubar da kalla, a dai dai lokacin Yah Sadeeq ya shigo gidan ganin Momy da Ammi na zubar da kwalla yasa yai turus yana jimami ya karaso falon.

Ganin basu san ma ya shigo ba yai gyaran murya yace "Ammi Momy ku zauna mana lafiya"

Momy ce tai karfin hali tace "dan Allah ku fada min mafarki nike ko kuwa ido na biyu ne Amina ce fa kanwar Daddyn ku goggwan ku Amina ce fa"

Ni kuwa da naji an ambaci Amina mikewa nai zunbur ina dad'a kare mata kallo, a cikin wannan yanayin Daddy da Umar suka iske mu, koda Yaga Ammi take yashiga murza ido yana fadin "Aisha Aisha kina ganin abinda idona yake gani ko kuwa gizo din take min kamar yadda ta saba?"

Momy tace "ba gizo take maka ba Aminan ka ce ita ce"

Take muka ga Daddy ya fadi yana mai sujja ga Allah, bayan ya dago yazo ya rungume Ammi, nan fa dakin ya kaure da koke koke baka jin karar komai sai shash-shekar kuka, harda su little Easha mukai ta kuka wuy-wuy shi kuwa Sadeeq ba hawayan amma idon sa yai jajur, mun dauki lokaci mai tsayi muna yi daga bisani yah Sadeeq ya shiga bamu hakuri, to bayan komai ya lafa Ammi ta samu guri ta zauna,

ni kuwa tashi nai na haura sama, dan na samu nai wanka na canza kaya, dakin Khadija naje dan na amsa mukulli na amma sai naji kofar ta a rufe, hakan ne yasa na nufi ban garan yah Sadeeq, nayi sa'a a bude na samu kofar, koda na shiga ban zarce ko ina ba sai bathroom din sa, ina shiga na hada ruwan wanka, koda na fito kamshin turaran sa dana ji ne ya tabbatar min da yah Sadeeq ya shigo, ina waigawa na gansa zaune a bakin gado, ya kura min ido, kunya ce ta kamin saboda tawul din dana daura dan karami ne ko cinya ta bai gama rufewa ba, na kasa dago kai na kalle shi, shi kuma ya kasa dauke kai daga gareni, hanyar fita bedroom din nayi amma sai naji kofar a kulle gam, jiyowa nai na kalle shi yana Murmushi yace "ina zaki bayan na rufe kofar ai tun na shigo na fahimci kina ciki da naji alamar ana wanka, nasan babu mai shigo min daki sai ke, shiyasa na rufe kofar dama a yunwace na dawo, ashe zan samu mai kore min kishin ruwa na"

Gaba na ne ya shiga buguwa dan yanzu sarai nasan maye aure kuma nasan abinda yake faruwa a tsakanin miji da mata, ji nai kamar an samin shokin na kasa gaba na kasa baya, haushin kaina ya kamani dana shigo bangaren sa, taku naji anayi da sauri na juye tsaye na gansa gaban madubi yana cire kayan jikin sa, gabana ya cigaba da faduwa, na shiga yi masa magiya, amma ko kala bai ce min ba, ya shige bayi abin sa, ya dauki lokaci mai tsayi can sai gashi ya fito da tawul daure a kugun sa, ba karamin kunyar sa bace ta kamani amma shi sai naga ko a jinkin sa, gefe na kawar da kaina saida ya gama shiryawa yazo gabana, kama hannu na yai yazo ya zaunar dani akan bakin gadon, shima ya zauna muna fuskantar juna yace "nasan yau rana ce ta farinciki a gareki, saboda Allah ya amsa adduar da muka dade munayi, ina tayaki murnar haduwa da mahaifiyar ki Siddeeqerh" ni dai ban ce mai kala ba, ya daura da "gashi kuma kin zana JSCE din ki shima ba karamin nasara bane". hannu na ya kama ya fara murza tafin hannu na, nai sauri na kwace ina fadin "maye haka yaya ka buda min kofa na fita kada aga na dade, nasan yanzu sun fara nema na ga yunwa inaji, yace " to ai banga magana ba amma ya jarabawar da dadi ko?"

Nace "eh Alhamdu lillah"

Kirjina naga ya kurawa ido nai sauri na sa hannu na ka kare nace "wai yaya maye haka kasan dai matar wani ce ni amma duk kabi sai kura min ido kake"

Banyi aune ba naji ya hada baki na da nasa yana tsotsa nayi ta kokarin kwacewa amma na kasa saboda yadda ya matseni a jikin sa. Saida ya gaji dan kansa ya sakeni yana maida wahalallan numfashi

Ni kuwa nayi tsuru-tsuru kamar wacce ruwa yaci ta.

Idanuwan sa sun kada sunyi jawur yace " wannan shine Punishment din da zan dunga miki aduk sanda kika kara ambata min wani" yana gama fada ya mike a kasalance ya bude kofar, ina ganin haka na zura a guje, yai saurin kamo ni yace "ke wai har yanzu baki yi hankali bane? Banason naga mace na gudu ki kama kanki baki san kin girma bane?"

"naji" na fada ina kunkunai nace "sakeni to"

Naci sa'a ban hadu da kowa ba direct dakin Ummi na zarce, ina shiga dirowar kayan ta na bude na dauko doguwar riga yar kanti mai ruwan madara, da sauri da sauri na kintsa na fito. Saboda na kosa na kara ganin Ammi a matsayin Mahaifiyata.

NI DA YAYA SADEEQ

•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•٠·˙

No editing

Chapter 32

______Koda na sauko zaune na samu su Easha da Dady karami da Umar afalo suna wasa, bayan na zauna, na shiga tambayar su Ina su Ammi Little Easha tace "suna dakin Momy".

"to" nace na mike na nufi part din Momy baki na dauke da sallama na kusa kai, a zaune na same su cikin dan karamin falon ta. Da alamar tattaunawa suke, nan kasa na zauna gurin Daddy nace "Daddy ina yini bamu gaisa ba "

Yace "lafiya lau Siddeeqah ya makarantar?"

"lafiya lau Daddy"

Yace "an kare ko yanzu sai cigaba?"

Nace "eh Daddy amma gaskiya ba makarantar kwana zan koma ba na gaji"

Yace "to shikenan nima nayi tunanin haka, kuma lokaci yayi da zaki tare a gidan mijin ki in yaso sai ki cigaba da karatun acan" kaina a kasa ni dai ban ce komai ba, na mike ina tambayar Momy Khadija, tace ta aiketa gidan kawar ta Hajiya Nafisa ," to" nace nan na bar su na fito, kitchen na shiga dan na taya Suwaiba aikace-aikacen kayan shan ruwa dan naga kamar aikin zai mata yawa ita kadai, munayi ina mata firar makaranta, a haka Ummi da Fadeela suka isko mu.

Muna nan kitchen din Sadiya tazo tai mana sallama direban su yazo daukar ta, nace mata "sai mun hadu a Dande"

"to" tace tana dariya ta tafi

da dare misalin karfe 10:00 pm dukkanin mu zaune muke harda yah Sadeeq, da yah Mubarak wato yayan Ummi, kuma shine zai auri khadija, tun wata biyu da suka wuce ya kare karatun sa a harkar computer, yanzu haka aiki yake a karka shin wani company, kowannen mu kagani fuskar sa dauke da annuri, Ammi ce tace "Yaya Ali wai yaushe zamu je Dande ne dan na kosa naga Inna na wallahi nayi kewar ta" yana Murmushi yace "ki kwantar da hankalin ki nan da Jibi ma sai mutafi in yaso dukkan ku sai kuyi sallah acan tunda sallar saura kwana biyar, dakanan ma ayi maganar tarewar yarinyar nan da kuma bikin Su Khadija"

Ammi tace "to shikenan Allah ya kaimu"

Da lokaci bacci yai nace "dole Ammi a dakina zata kwana"

itama dama tana son kebewa da diyar tata, yayin da Fadeela tace ita A dakin Ummi zata kwana saboda jinin su ya hadu , Jiddah kuwa tace ita da Little Easha zata kwana dan itama jinin su ya hadu, Dady karami kuwa cewa yai tare da Umar shi zai kwana, Khadija na dariya tace yanzu ni ba Wanda zai kwana dani ai shikenan, sai mun hadu da asuba "

Tana gama fadar haka ta haura sama, muma da daidai da daidai mukai ta watsewa.

Nida Ammi a daki fira muka dasa ta tsakanin 'ya da uwa ina kwance kan cinyar ta nike ce mata" Ammi wallahi Abba na bai da mutunci kamar bashine ya haife ni ba" Ammi tai saurin toshe min baki tace "ki daina fadin haka koma yaya ne dole ki bashi kima da daraja saboda shi din mahaifin ki ne" na ce amma fa Ammi tun nataso ban sanshi ba ban taba ganin shi ba, bai taba turo dai dai da naira goma yace a saimin sabukun wanki ba, Daddy ne ya tsaya min tsayin daka akan komai na rayuwa ta, sai Momy Allah yai mata Albarka wallahi tana kula dani, ko ita ta haife ni sai haka dan ba'a taba nuna min banbanci a gidan nan ba, haka fa lokacin Aure na da Daddy yaje kar kiga yanda Abba na yaci mai mutunci nan dai ta kwashe labarin komai ta fada mata, idon ta cike da kwalla take ce min "nayi hakuri ba yin kansa bane asiri ne amma Abba na yana mutukar so da kauna ta insha Allah nan bada jimawa ba komai zai zo karshe".

Bayan kwana biyu ya kama ranar zamu je Dande lokacin Sallah sauran kwana Uku da misalin karfe goma na safe dukkanin mu a farke muke kowa sai shiri yake bayan mun gama shirya wa, mota uku mukayi da Ammi da Momy da Daddy babba da Umar da karamin Daddy mota guda suka shiga, yayin da Khadija da Jiddah da little Easha suka shiga motar yah Mubarak, ni da Ummi kuwa motar yah Sadeeq muka shiga inda na zauna gidan gaba Ummi na gidan baya muka dauki hanyar Dande sosai yah Sadeeq ke tsulala gudu ahanya, na lura dashi yana son gudu a mota, mu dai Allah ne ya sauke mu lafiya, duk da idan nai hutu ina zuwa Dande amma ba laifi ta dan samu canji dan yanzu haka ana basu wutar nefa kuma asbitin bayan gari an dan gyara shi, a kofar gidan Inna mukai farking da futuwar mu yaran unguwa akai ta kallon mu ana ga yan Indian nan sun zo, sau tari dama ni haka suke ce min yar indiya, dayin fakin din mu, sai ga motar yah Mubarak nan shima ya danno kai, muna kokarin shiga saiga motar Daddy nan ita ma ta kunno kai haka muka dunguma gunin ban sha'awa da burgewa yaran layi kuwa sai kallon mu suke,

Bakin mu dauke da sallama muka shiga, babu kowa a tsakar gidan saboda haka muka dunguma cikin falon Hajiya Inna, a zaune take tana kallon talabijin "tsohuwa mai ran karfe" na fada yayin da na isa gare ta na fada kan cinyar ta.

Tana dariya ta baka min duka tace "dagani ja'ira kada ki karasa ni"

Turo dan karamin baki na nai nace "inna ki dai ji tsoron Allah yanzu ni ina naga nauyin da zan karya ki"

Kallon mu inna ta shiga yi daya bayan daya kana tace "Karami wa nike gani wannan kamar Amina na? Ko ido na ne kuma wa'innan yaran na waye?". Wato su little Easha da Fadeela take nunawa.

TA dora da cewa "ko tsufan nawa ne yake rudar dani Karami?". Ta ambaci sunan Daddy 1

Da gudu Ammi ta isa ga Inna ta rungume ta tana cewa "nice Inna nice Aminan ki ce"

Sai hawaye shar-shar yai ta zuba daga idanun inna jikin su Daddy yai mutakar sanyaye suka samu guri suka zauna

Inna sai sumbatu take tana cewa "ashe da rabon mu gana ashe da rabon zan sake ganin ki, bayan wa'innan shekarun, dama ni ban fidda rai ba kullum cikin addua nike ina rokon Allah idan kina raye Allah ya bayayyana mana da ke, Allah maji rokon bayin sa gashi ya amsa mana, jikin kowa yai sanyi nan mukai ta taya Inna kuka ba mai lallashin wani saida mukai mai isar mu, sannan mukai shiru,

Cikin kuka mai tsuma zukata, Ammi tace "Inna ku yafe min nasan na tafi na barku cikin matsanancin tashin hankali nima ba a san raina nayi ba, alokacin ban san inda hankali na yake ba, ni dai nasan kafin faruwar abun Habiba kiyasha ta tazo daki na, ina hada ido da ita naji gabana yai mummunan faduwa daga nan tace min "dauki shegiyar yarinyar ki ki kaima uwar ki banason na kara ganin ki arayuwa ta ki tafi nesa da wannan garin, sai na same ni da bin umarnin ta ban dauki komai ba sai mayafi na, na saba Siddeeqah a kafada na fito, a harabar gidan naga Alhaji Sulaiman, kallo daya na masa naji na tsane sa, haka na wuto shi yana so yai min magana kuma ya kasa, idon sa cike da kwalla na bude get na fito, ban zarce ko ina ba sai gidan ki Inna kina gani nana ki ka shiga tambaya ta lafiya? Me yasameni amma ban ce miki uffan ba na aje miki Siddiqah na fito, tafiya nai mai nisa da kafa ba tare da nasan inda na dosa ba, yamma ta fara yi saboda haka dare ya fara lillbe yini nagaji ga yunwa ga kishin ruwa, nan na zube a kasa gefan kwalta, wani mai mota ne yazo wucewa da ya ganni ya taimaka ya dauke ni, bayan ya sakani a mota asbiti ya kaini, bayan sun gama duk wani gwaje gwajen su basu ga komai a tare dani ba illah yar yunwar da ta galabaitar dani, kwana na biyu a asbiti aka sallame ni, wannan mutumin ya dauke ni kamin nan tun a asbiti yake tambaya ta, akan ya suna na kuma ina ahali na, amma babu uhm babu uhm uhm, sai dai nai ta bin sa da ido, hakan yasa ya fahimci ba kalau nike ba, da yike babban malami ne, shine fa ya dauke ni ya kaini gidan sa gurin matan sa anan garin katsuna, inda sukai ta nema min magani har Allah cikin ikon sa ya bani lafiya, bayan na dauki tsayin sheru bana ko magana, to bayan na warke na dawo hayyaci na ya tambaye ni ahali na ko suna ina, sai na tsinci kaina da ce mai bani da kowa sai Allah sai kuma kai, to bayan kwana biyu yazo min da maganar aure, nace masa ni da ba fita nike ba ina zan samu muji?" yace" indai wannan ne bashida matsala zai samo min mijin aure na kirki wanda zai rike ni amana "

Bayan sati guda ina zaune a daki na sai gashi yazo yake cemin" ya daura min aure, yanzu haka tare da mijin nawa yazo kuma dani zai tafi saboda haka na tashi na shirya "

Haka dai na baro gidan Mlm liman ba dan raina yaso ba nabi Alhaji Imran, wato baban yarannan

Ammi ta fada tana nuna su Fadeela

TA dora da cewa, nayi zama na amana da margayi, yana yawan tambaya na Ahalina amma sai nace" ni bani da kowa ".

Na rasa kuma dalilin da yasa nike cewa haka dan ko tunanin wani nawa ma banayi, cikin ikon Allah na haifi yarana yan biyu mace da namiji masu kama da Daddyn su, ya tambayeni shawara akan sunan da zamu sa musu nace" Asa min Aisha da Aliyu ".

Haka rayuwa ta cigaba bayan wasu shekaru ina zaune a office dina saiga Sadeeq da Siddeeqah nan sun shigo, tunda na kalle su na fara tuno da iyali na kuma naji ina kwadayin na sake haduwa dasu, tunda naga Sadeeq naji a jiki na dana ne haka itama Siddeeqah, sai naja ta ajiki na ta yadda take yawan bani labarin ku, hakan yasa na kara tabbatar da tabbas ita din jini na ce, amma sai ban taba nuna mata ba, nasha tambayar ta ina mahaifiyar ta? " sai tace min" mahaifiyata ta bata tun ina yar karama kuma har yanzu bamu san inda take ba " hakan yasa na kara jin kwarin gwuiwa shine fa da akai hutu nace ta bari zan kai ta".

Ta numfasa tace "wannan shine takaitaccan abun da ya faru bayan rabuwa ta daku".

Inna tace" wannan fa?"

Fadeela take nufi

Ammi tace" marainiya ce mahaifiyar ta ta rasu wajan haihuwar ta, kuma yayar su Easha ce da suke uba daya".

Daddy yace "naji kina cewa margayi yanzu shi Alhaji Imran din ya rasu?".

Wasu hawaye ne masu zafi suka zobo wa Ammi tace "eh ya rasu a sakamakon hadarin mota da yai".

"Allah ya jikan sa su Daddy suka ce"

Wannan kenan

Bayan ko mai ya lafa Ammi da Momy suka tambayi inna abinda za'a sha ruwa dashi?

Tace su bari Garba ya siyo tunda yanzu yamma tayi, ga gajiyar mota

Bayan kwana biyu ya kama jajibari, mayafi na na saba nace "Inna zan fita" tace "zuwa ina kuma keda ba kya iya zama a guri daya?"

"gidan Ladiyo man tun nazo ban leka ta ba fa".

"to a dawo lafiya" inna ta fada ni kuma na fice a buna

A soro naci karo da Yah Sadeeq, bayan ya kare mun kallo yace" ina zuwa?".

nace" gidan kawata Ladiyo zani ".

" kuma da izinin wa" ya jefo min tambayar

"inna mana" na fada a takaice

"to bazaki ba ki koma".

Kallon in ka isa na mai na fice a bi na

karasawa cikin gidan yai ransa a mutukar bace ya fara masifa saboda duk suna tsakar gidan, fadi yake "wai Inna akan me zaki bama yarinyar nan dama ta dunga gantali, da aure na a kanta".

Momy ce tai caraf tace "eh lalle ma Sadeeq, yanzu ne kasan da ita din matar ka ce yanzu ne kaje jin haushin yawon da take yi? To tun wuri ka fita ido na bazaka takura ma yarinya ba".

Ammi da ke wanke wakan da za'a kosai dashi tace "Haba Momyn yara ai da gaskiyar sa, tunda shi ba sakaran na miji bane taya zai bar iyalin sa sakaka a gari? Ina goyan bayan sa kuma bari ta dawo sai naci mutuncin ta, na kara ganin ta fita ba da izinin sa ba

Please Comment Share

NI DA YAYA SADEEQ

•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•

No editing

Chapter 33

_______zaune nike a dakin Ladiyo muna firar mu gunin ban sha'awa sai wasa da dan ta Mamman nike yi, tace "wai ke Siddeeqah yaushe zaki tare a dakin mijin ki ne?"

Nace "waya gaya miki zan tare? Nida nike jira ya bani takarda ta naje na auri wanda yake kauna ta".

Bakin Ladiyo bude tace "amma dai baki da hankali, a wannan zamanin ka samu miji irin yah Sadeeq ai ka more, ke sune fa irin mazan da ake bada labarin su a novel, amma kike nema kiyi fatali da damar ki".

Nace "bazaki gane bane, mubar maganar kawai" bayan na bata kyautar kudi nai mata sallama nace "taya kuri nazo mata da kaya sai na bude a kwati na zan kawo mata"

Gadiya tai min har bakin zaure ta rako ni

A hanya na hadu da wani mai naci tun na fara tafiya yake bina yana min magana amma ban kula shi ba.

Har bakin kofar gida ya rako ni inda yah Sadeeq da Yah Mubarak ke zaune suna fira, da gani na Sadeeq ya hade rai kamar ya hangi mutuwa, tasowa yai ya nufo mu kan ya karaso na shige gida ban san ya ya kare da mai bin nawa ba.

Koda shiga na gida Ammi ta hau yin sababi Momy na kare min nan na barsu nai cikin daki na inda na samu Fadeela na ta sharbar baccin ta. Jiddah na zaune na chat Khadija kuma na ninke kaya.

Bayan na cire mayafina na zauna kusa da Khadija ina taya ta ninkin kayan

Jiddah ce ke cewa "yau fa aunty Bilkeesu zata zo".

Khadija tace "au haba na dauka sai ranar Sallah"

"A a yau ne" ta bata amsa

* * * * * * * * * Yau take sallah bikin daya rana gidan mu cike yake da yan uwa da abokan arziki da makota, anci ansha yara nata har kokin su. Wa'inda suka san inna da dadewa suna ta taya ta murnar bayyanar diyar ta.

AUNTY balki sai tsokana ta take wai yayan su zai kamani.

Little Easha ce ta shigo tace "aunty Siddeeqah yah Sadeeq na kiran ki"

"To" nace amma ban tashi a lokacin ba sai da na gama shan kanshi na

Ina ta raba mutane har na wuto falon. Shima tsakar gidan cike yake da mutane suna cin abinci gunin burgewa.

Dakin yah Sadeeq na nufa bayan nayi sallama ai min izinin shiga na shiga.

Tasowa yai ya maida kofar ya rufe kana ya kama hannu na ya zaunar dani bakin katifar sa yace " na gaji ne shine na kira ki ki mun tausa".

Dago kai nai muka hada ido ya daga min gira gajeran wando ne a jikin sa sai rigar shan iska wato bes fuskar sa kuwa dauke take da saje ga dan gemu ya aje gunin burgewa.

Kwanciya yai yace " fara nana " ido na zaro waje nace "yaya me zan fara kuma? Wallahi ban iya ba"

Tashi yai ya zauna yace "to shikenan bari na gwada miki inyaso sai ki min yadda nai miki ".

Da sauri nace na iya ba sai ya min ba amma yace "Allahn kashe sa sai ya gwada min"

Ya na iya haka ya Sadeeq yai ta jagwalgwala ni, tun yana yi cikin hankalin sa har ya fara fita hayyacin sa dan kokari yake ya rabani da kayan jiki na.

Kuka na sa masa ina magiya akan ya rabu dani " ganin haka yasa ya sauka daga kai na yai gefe idon sa a rufe yana jin marar sa na murda masa, take ya fara juyi yana kiran sunan Allah, yanzu na fahimci dalilin wannan ciwan na yah Sadeeq da tun ina karama naga yana yi, amma gaskiya bazan iya basa kaina a wannan halin ba, ganin ciwan nasa na kara tsanan ta yasa na mike da hanzari na fita daga dakin, a tsakar gida na hadu da Ammi, ta ganni kamar bana cikin hayyaci na tace "lafiyan ki kuwa duk kin sukurkuce?"

Nace "Ammi ba lafiya ba yah Sadeeq ne gayican a daki sai hankoran mutuwa yake".

Ban gama rufe baki ba Ammi ta nufi dakin sa da sauri.

Ni kuma cikin hanzari na karasa falo, lokacin mutane sun ragu sosai a falon Cikin tashin hankali nace "Momy yah Sadeeq fa baida lafiya gayi can cikin wani hali".

Duk da tausayin Sadeeq ya kamata amma sai tace "shi ya sani ita babu ruwan ta "

Inna ce tai ta mata fada da kyar taje dakin sa, amma tana ganin sa taji yayi bala'in bata tausayi.

Mubarak Ammi ta kira ya kama shi akasa a mota Ammi da aunty Balki suka shiga don su kai shi asbiti. Suna zuwa aka amshe su cikin kulawa aka kai Sadeeq dakin da ake duba mara lafiya kai ka ce baya numfashi ne, bayan komai ya lafa Likatan yazo inda su Ammi ke zaune yace ta same shi a office.

Zaune take kan kujera likitan yai mata bayani kamar haka "Hajiya gaskiya idan ba so kuke ku salwantar da rayuwar yaron ku ba to kuyi masa aure dan banga dalilin da zaku aje matashi kamar wannan babu mata ba, ina tunanin ma ya girmeni, amma ni yanzu haka ina da mata da yarana guda biyu, kuma ba wannan ne karo ne farko da yake yin irin wannan ba, magunguna yake sha da zaran yaji irin yanayin, to ahalin yanzu ya ruga ya kai makura wa'innan magungunan sun daina masa aiki, aurar dashi ne mafita gaskiya ".

Kalaman dakta ba karamin rikita Ammi sukai ba, abinda yafi tsaya mata arai shine da doktan yace" zasu iya rasa shi" tabbas dole ta dauki mataki dan bazata zura ido haka ya faru ba, ta gama yanke hukuncin tana komawa gida zata kira Daddy ayi maganar tarewa.

Haka kuwa akai Ammi na zuwa gida ta kira sa a waya ta sanar mishi, ba tare da kowa ya sani ba yace "to shikenan zai shigo nan da kwana biyu su fara shirye shirye"

Bayan kwana biyu Sadeeq ya murmure sai dai ya dan fada kuma yayi wani iri dashi, yasha aiko Samaheer ta kirani sai nai watsi dasu, dan badani za'a dunga tsanan cewa ba

Yau ne Daddy zai zo sai shirye shiryen hada Abinci Ammi keyi Momy na taya ta.

Bayan Daddy yazo sun tsaida magana akan nan da sati buyu zan tare, sunce daga baya a saka ranar bikin Khadijan, amma kuma Ammi ta roki Alfarma akan tanaso ta kaini naga mahaifina kamin lokacin bikin, sosai Daddy yaji dadi kuma yayi farinciki da kanwar sa tayi wannan tunanin.

Wata ranar Juma'a muka shirya, Ammi tace naje na fada ma Yah Sadeeq dan shi zai kai mu, koda nagan sa ba karamin tausaya masa nai ba saboda yadda ya zama wani iri kamar ba yah Sadeeq dan gayu da kwalisa ba, nesa dashi na tsaya nace "Ammi tace idan ka shirya kazo ka kai mu"

Ban jira amsar sa ba nayo waje abi na

Unguwar barnawa a bakin wani katon farin get yah Sadeeq ke danna hon can mai gadi ya leko ganin bakin fuska ya ce su waye anan, koda yaji Muryar Ammi tayi magana tace "Nice Hajiya Amina ce" take ya shaida ta yana fadin "Allahu akbar Hajiya ashe zamu sake haduwa".

Bude mana get din yai muka sulala ciki

A dai dai lokacin wani dattijon mutum mai sanye da manyan kaya ya fito daga motar sa ganin bakuwar mota a cikin gidan sa yasa yai turus, Jim kadan ni da Ammi da Sadeeq muka fito, ido na ya sauka akan kyakkyawan dattijon da nike kyauta ta zaton shine mahaifina, nuna mu ya shiga yi yana daga hannu sai ya bude baki yai magana sai ya kasa, addu'ar neman tsari yai ta karantawa a cikin zuciyarsa kamin ya ce "Amina"

Ido cikin ido Ammi ta kallesa tace "Suleiman".

A kuma dai dai lokacin wata bushash-shiyar mata ta fito ganin mu tare da Abba na yasa ta cire dan kwalin ta ta fara ihu tana kururuwa cewa take "ta shiga uku yau asirin ta ya tonu Amina da Sulaiman sun hadu". kuma boka yace " muddin suka hadu to fa asirin kanta zai koma haka dai tai ta simbatu sai yaran gidan duk gasu sun fito, sunji uwar su na hauka.

Koda na daga kaina wa zan gani senior Jamlah ce rike da wannan me haukar tana daura mata dan kwalin da ta kwance.

Kallon Abban mu nayi sai naga yana kama da Jamlah, a cikin zuciya ta nake cewa "kenan Jamlah blood sister na ce shiyasa tun a makaranta naji na tsane ta, ashe ba banza ba mamar su ce ta tarwatsa min farinciki na ta hanani tasowa a gaban iyaye na"

Take Abban mu yai waya da masu kama mahaukata yace "an sumu a gidan sa".

Babu bata lokaci sai ga masu tafiyar da ita su zo, yaran ta guda biyar sai kuka suke Abba yace "duk wanda zai bita ya bita ga hanya nan" yana gama fadar haka ya ce "Amina kuzo mu shiga daga ciki "

NI DA YAYA SADEEQ kuwa kamar wa'inda ruwa ya cisu dan mamaki, wato dai inda ranka baka daina kallon abun al'ajabi ba, kuma Allah ba Azzalumi bane sai dai bawan da ya zalincin kansa.

A wani kayataccan falo muka zauna da ganin Abban mu yana cikin faran ciki dan ya kasa zaune ya kasa tsaye.

Jamlah ce ta shigo da yan kannan ta na biye da ita sai kuka suke kamar wa'inda akaiwa mutuwa, Abba ne ya daka musu tsawan yace "wai bana ce muku duk wanda bazai zauna ba ya bita? abinda ta Shuka ne ya koma kanta, kunga dole ta girbe shi. kuma dama ramin mugunta ka gina sa daidai da kai saboda wataran kaine zaka fada".

Sai a lokacin Jamlah ta lura dani, da alamar tayi mamakin gani na tace "Siddeeqah kece"

Ban bata amsa ba Abba yace" kunsan Juna ne?"

Ammi tace" eh duka daliban mu ne a makarantar Jibya ".

Kallon Jamlah Abba yai yace" gata nan kanwar ku ce sa'ar Sajida ce ".

Da mamaki ta kalli Abban mu dan ita tun da take a cikin gidan nan bata taba jin anyi labari ko makamancin wannan ba.

Ya nayin ta ya nuna bata fahimta ba don haka Abba ya gyara zama ya shiga basu labarin duk abun da ya faru, sunji babu dadi kuma sunji mahaifiyar su bata kyauta ba, hakuri suka shiga bawa Ammi harda Abba akan ta yafe musu tace "kada su damu komai ya wuce".

ABBA ya bukaci yaji labarin abinda ya faru lokacin da yaga ta fito zata bar gidan.

Take Ammi ta shiga labarta masa bata boye masa komai ba har labarin auran ta da Alhaji Imran ta basa.

Yaji babu dadi amma basu isa su gujema kaddarar ubangiji da tazo a rubuce ba .

Da zamu tafi Abba ya bukaci a barni amma nace "ni bazan zauna ba sai da Ammi na".

Abba yaji babu dadi hakan yasa yace "to shikenan Kuje zan zo da daddare insha Allah "

Da daddare Abba na yazo kamar yadda yai alkawari, anan cikin baranda akai mai shimfida ya zauna inda suke tattaunawa da Daddy yai ta basu hakuri akan abinda ya faru, kuma Daddyn ya hakura saboda sun san ba halinshi bane kuma Ammi tai musu bayanin abunda ya faru da ta dawo.

Bayan Inna tazo suka gaisa nan ma hakurin yai ta bata tace "babu komai ya wuce tunda ba'a cikin yaiyacin sa yai ba".

Bayan Inna ta koma ciki Abba ya kara gyara zama yace "dama kuma alfarma nike so na kuma roka"

Daddy yace "alfarma kuma Alhaji Suleiman ai ka wuce neman Alfarma fadi kawai kanka tsaye"

"dama inaso na maida Amina dakin ta ne"

Daddy yace "madallah haka akeso naji dadi sosai, amma nan da yaushe kake so ka maida ta?"

ABBA yace "ai ba wani lokaci za'a dauka ba nan da kwana biyu ma yayi, sai aiyi bikin Siddeeqah tana dakin ta itama Siddeeqan nasan zatai farinciki matuka"

"dan dakata ina zuwa" Daddy ya fad'a kana ya Mike, wurin kanwar tasa yaje suka shawarta kana ya dawo gurin Abba na suka Kare magana, a take a gurin Abba ya biya Sadaki, aka tsaida daurin aure ranar litinin.

Da ranar litinin tazo aka daura auran Ammi da Abba kuma a ranar Ammi ta tare da yaran ta, wato little Easha Dady karami Fadeela Jiddah dan ita ma tace Ammi zata bi sai kuma ni.

Gidan Abba na gida ne mai girman gaske bangare-bangare ba ruwan wani da wani, bayan wasu yan kwanaki a cikin gidan mun dan fahimci Juna da su Jamlah sukan zo bangaren mu ayi fira, ga maganar biki na ta taso gadan gadan dan bai wuce saura kwana goma ba. Sosai Ammi ke bani magun-guna ga wanka da lalle da ake min akai akai, ana saura sati daya Momy ta aiko mubarak yazo ya tafi dani gurin wata Hajiya kamshi aka kaini, kwana na uku a gurin ta ana gyara ni, kar kuso kuga yadda na koma, duk da abubuwa sun zo min a kurarran lokaci, ban samu gyaran da ya dace aiwa amare completeba amma na hadu in ka ganni bazaka gane ni ba, indai ba kamin farin sani bane dan na hadu nayi kyau iya kyau fatar jiki na tayi laushi ga haske da sheki gunin ban sha'awa.

Zaune nike da su Sadiya, magana suke akan dinner din da zasuyi ga kamu da Arabian night ni dai duk jin su nike, saida suka gama tsaf na ce "kun gama?". Kanwata Sajida ce ta daga min gira Alamar "eh".

Nace "lalle kam kuna ruwa danni wallahi babu wata bidi'ar da za'ai, idan bacci kuke gwara ku farka, dan walima ce kawai za'a ita ma kuma sai bayan na tare".

Ina gama fadar haka na tashi na barsu suna ta surutu wai ban isa ba. Su wannan ka kalan basu sanshi ba

Ana saura kwana biyu tarewa Yah Sadeeq yazo gidan mu, inda ya aiko kanwata Hannatu da muke uba daya ta kira ni, A falon saukar baki na same shi har yanzu bai gama murmurewa ba, tausayin sa ya kamani, sai naji zan zauna dashi kuma zan masa biyayya ko dan farincikin iyayen mu ya daure, bayan na gaishe shi na zauna dan nesa dashi.

tashi yai ya matso kusa dani yana cewa "ke wai dodo na koma miki ne kike gudu na? dama nazo ne na tambaye ki naji ko akwai wani events da zakuyi".

Kai na a kasa nace "babu wata bidi'ar da zanyi, walima ce itama sai bayan an kaini za'ia".

"to" yace yana mai jinjina wannan tsarin nawa.

Washe gari mai fulawa tazo ta mana amma ni ja nace ai min tayi kyau sosai abinka da farar mace, kuma a daran ranar aka sani a lalle.

Wa shegari ta kama asabar kuma yaune tarewa ta gidan mu cike yake makil da jama'ar Ammi har yan Katsina da suke mutunci da Ammi sunzo, haka dangin mahaifina suma sunzo gidan dai ya cika makil masha Allah amma babu wani kida da akai kaya kuwa na canza wannan na saka wancan ga sarkar gwal da Abba na ya siya min mai tsadar gaske, biki yayi biki. Ammi ma sai shiga take tana fita, abun dai ba'a cewa komai sai masha Allah anyi komai cikin tsari da burgewa. Harda yan makarantar mu sunzo, nayi mamaki da na gansu harda senior din mu, ashe duk Aunty Jamlah ce ta gaiyato su.

Da dare yai da misalin karfe 8:2 pm durkushe nike gaban Abba da Ammi nasiha suke min mai ratsa zuciya, kaina a lullube cikin alkabba mai ruwan danyan gwall kayan da nasa na ciki kuma farin leshi ne mai kyau da tsadan gaske ga kamshi sai tashi yake ni kaina nasan na hadu.

Bayan an gama min nasiha kannan Abba na da wasu kawayan Ammi suka tasani gaba sai kerarran gidan Sadeeq da yake a nan cikin sabuwar unguwar mu'azu, ginin gidan na zamani ne haka adon gidan ma. Ban gare ne guda buyu wato daya nasa daya nawa. Goggo Abida tace "nayi bismillah na shiga da kafar dama "

Har bedroom room dina suka kaini wanda ya gaji da haduwa komai na cikin dakin pink ne hatta da fentin dakin ma ga wasu akwatuna lodi lodi dana gani a here. wannan pink guda goma sha biyu wannan ja guda shida wannan me ruwan kasan guda ba kawai, nayi matukar mamaki dana gansu ko duk na waye?

Basu wani jima ba akace su fito a maida su dare na yi harda su Khadija aka tarkata aka tafi ya rage sai ni kadai ji na nike wani iri,

Tambayar kaina na shiga yi, Wai yanzu sabuwar rayuwa ce zanyi fa da Wanda bai so na da kauna ta, nasan bani yake so ba gangar jikina yake so, kuma nasan daya samu abunda yake so zai rabu dani, hawaye ne masu zafi suke zubar min, tunanin maganar sa ya fado min arai na cewa" na fara tunanin yadda zan rubuta littafi mai suna NI DA YAYA SADEEQ aduk sanda na tsinci kaina a gidan sa" tabbas lokacin yayi yanzu Allah yasa farinciki zan rubuta.

Comment Vote Share

NI DA YAYA SADEEQ

•●♥ بسم الله الرحمن الرحيم ♥●•

No editing

Chapter 34

_______bayan wasu shekaru. Zaman aure na nike mai kyau da tsafta da kuma tsantsar so da kulawa da junan mu, alhamdu lillah na kammala secondary school di na , amma ban samu na cigaba ba, saboda yah Sadeeq irin mazajannan ne masu bukatar iyalan su a kusa dasu, kuma yace "mai zanyi da karatu mai zurfi indai zan karanta na rubuta kuma na fadi a fahimta nima idan an fada min na fahimta ai shikenan" .

Mun samu fahimtar juna sosai tsakani na da yah Sadeeq zan iya cewa tundaga ranar da aka kaini har kawo yanzu da nike magana baiyi abunda zai cusguna min da gangan ba, saida bisa rashin sani da kuskure wanda dama dan Adam tara yake bai cika goma ba, yah Sadeeq mutum ne mai saukin kai da tausayin na kasa dashi yanzu haka mun bude gidauniyar da ake temakawa marayu da gajiyayyu. Ya rike mukamai da dama a bangaran aikin sa yanzu haka shine kwamishinan yan sanda na nan jahar kaduna, mun haifi yara yan biyu duka maza shekarun su uku yanzu, Sunan Abba da Daddy aka sa musu, saboda haka muke kiran Abba da Sudais Daddy kuma muke ce mai Taufeeq

Anyi auran Khadija da Yah Mubarak inda suke da yara biyu duka mata, kuma sun koma zama a Dubai, karkashin wani kamfani da suka dauke shi

Sai Ummi da ta auri wani ma'aikacin Jarida, itama ta haifi dan ta namiji

Fadeela kuwa yah Farooq take aure sun haifi yara uku maza biyu mace daya

Sai Jiddah da take auran Maheer wanda sun hadu ne a wajen bikin wata kawar Jiddan yayin da Maheer din shine babban abokin ango sun haifi diya mace

Tsaye muke a filin buga ball din. NI DA YAYA SADEEQ ne sai yaran mu da muke ta guje guje cikin so da kaunar junan mu yah Sadeeq na wurga ma kallon ya cafe da hannu yana dariya ya iso gareni ya shiga raira min wakar "zan rayu da ke zan mutu dake a abadan dani da ke zamu zauna" . ✍️

* * * * * * * * * *

Tammat bi hamdulla Alhamdu lillah duka duka anan na kawo karshen littafi na mai suna NI DA YAYA SADEEQ ina rokon Allah ya yafe min abunda na rubuta bisa kuskure wanda kuma nayi dai-dai Allah ya bani lada

Domin yin korafi ko kuma sharhi ko yabawa marubuciyar ko kuma bata shawara za'a iya yin magana da ita ta whatsapp only whatsapp ku TunTuben a wadannan numbobin.

Siddiqahtul Khairy Yahya +966591512794

End of current loaded text.