Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
Bahiyya Book One Complete Hausa Novel
Bahiyya Book One Complete Hausa Novel
By Oum Ameera
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
Bahiyya Book One Complete Hausa Novel

Bahiyya Book One Complete Hausa Novel

Author: Oum Ameera
Chapter 19 of 23
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters

“Ban san wace kalar ƙaddarar ce ta haɗaku ba Bahiyya,Don wannan haɗuwar taku da ƙaddara zan kira ta, na san ba don tana neman komai daga gare ki ba sai dai don tayi niyyar ta taimaka miki kawai because you have nothing to pay her in return, banga abinda zaki bata ba a duniyar nan domin tafi ƙarfin ki ta ko ina, in ma masu aiki ta ke nema nasan dole sai masu kwalin karatu mai zurfi don ko a gidan hajiya Rasi'at da bata kai ta ba suma haka tsarin su ya ke. Allah ne kaɗai masanin abinda yake zuciyarta akan neman ki da tayi ɗin nan har na tsawon shekara ɗaya, abinda zan faɗa miki na ƙarshe shi ne Bahiyyah ki tsare mutuncin ki komai wuya komai tsanani, ki yi musu biyayya daidai yadda zaki iya.”

Gyaɗa kaina nayi tare da jinjina girman lamarin a kaina nace.

"In sha Allah Malama zan kiyaye”

Zaman mu a nan munfi 2hours, bayan an cika mu da kayan ciye ciye abinci kala da kala muka ci muka ƙoshi sannan daga baya sai ga wata matashiyar mata da hausarta bata fita sosai ta zo tace mu tashi mu biyo ta. Haka muka yita bin ta mu shiga nan mu wuce nan ko ina gwanin burgewa tamkar duniyar da ba'a mutuwa a cikin ta, sai daga ƙarshe muka isa wani parlour na alfarma mai wani sanyi da ƙamshin rahama mai kwantar da zuciya.

Ko a nan ma sai da muka shafe kusan mintuna talatin sannan sai gata ta iso cikin takun ta na ƙasaita da girma na manyan mata ta samu wuri cikin ɗaya daga cikinsu cikin lumtsatstsun kujerunta ta hakimce.

Tuni ni da Malama muka shiga miƙa gaisuwa ni kuma a zuciyata ina ta mamakin yadda malama ta wani baje a ƙasa tana faman kwasar gaisuwa yayinda ni na san cewa itace ya kamata ace ta gaidata domin ko bata haife ta ba saura kiris.

Murmushi tayi sannan ta kalli Malama tace.

“Na gode”

Murmushin itama Malama tayi tace.

“Ba komai Hajiya, Daman cewa nayi bari na rakota domin in ƙara tabbatar da cewa a hannu na gari zata faɗo, Allah ubangiji ya baki lafiya ya kuma zaunar da ku lafiya”

Murmushi Hanifah ta sake yi hannun ta riƙe da wayar ta tana latsawa ba tare da ta kalle ta ba tace.

“Kar ki damu In sha Allah babu wata damuwa”

“To nayi murna da jin haka, ni zan koma sai Allah ya sake haɗamu da alheri”

Daga haka Malama ta miƙe nima na yunƙura da nufin miƙewa tayi saurin dakatar da ni tace in zauna ba sai na rakata ba, amma fir na ƙi saurarenta Sai da na biyo ta har mota, kaya ne ake ta tula mata niƙi niƙi Wai gashi nan in ji Hajiya, Malama kuma daga gefe sai faman ƙara jaddada min take cewa in bi matar nan sau da ƙafa bata da wata matsala, a raina har abin ya soma bani Mamaki ni dai toh kawai nike kira mata har ta shige mota ta wuce. Hawayen da suka silalo min na goge tare da yin sauri na bi bayan matar nan da ta ɗazu domin ba lallai ne na sake maida kaina wurin ba.

Wani irin tsoro ne ya dirar min a zuciya ta wanda ban san dalilin hakan ba, ko don yanzu ya rage parlourn daga ni sai ita ne Oho! Tunda na zauna bata sake kallon in da nike ba tamkar Allah bai yi ruwana a wurin ba haka tayi min wanda sam banji daɗin hakan ba, ko ba komai atleast ya kamata tace min wani abu don ta nuna tasan cewa ina wurin kai ko kallona tayi ni hakan ya wadatar, amma tayi da ni kashi duk ɗaya wanda maman Khadijat baya daga cikin halayyar ta, shiyasa ni ke sonta.

Ba abin da nike sai tubka da warwara ni kaɗai a cikin zuciya ta, daga ƙarshe na ɓige da tunanin Mama da Nuhaira wanda ba san lokacin da Hawaye suka shiga kwaranya daga cikin idanuwa na ba. Bayan na gama hawayena na tsayar da su don kaina, sai na sake ɗago kaina da nufin sake kallon wannan ishashshiyar matar sai dai wurin wayam ba kowa ban san lokacin da ma ta tashi tayi tafiyar ta ba, wasu sabbin hawaye ne suka sake zubomin raina ya hau wani ƙuna kamar in tashi in tafiya ta gida. Ina nan na zuba ma sarautar Allah ido sai ga wannan matar ta ɗazu ta sake dawowa ta kalle ni da sakin fuska tace.

"Oya ta shi ki biyo ni”

Ba musu na tashi na bita tamkar wasu akala da raƙumi har muka kai wata killatattar ƙofa haka duk a cikin rufi ɗaya. Shiga tayi nima nabi bayan ta.

Parlour ne mai kyau wanda ke ɗauke da set ɗin cushion ash and black, komai na parlourn haka kalar take komai an jerashi a tsari. Baki na saki kawai ina bin ko ina da kallo kamar wata wawiya.....

“Nan shi ne in da zaki zauna...”

Daga haka kuma ta jani muka shiga bedroom wanda ko toilet ɗin kaɗai abin kallo ne, muka dawo ta sake nuna min wai inda kitchen yake duk a cikin wannan ɗan madaidaicin part ɗin, komai yayi kyau ba ƙarya. Bayan ta gama nuna min ta jani toilet ta shiga koyamin yadda zan yi amfani da komai na toilet ɗin bayan mun gama  muka koma kitchen nan ma ta nuna min, muka dawo Parlour ta nuna yadda a kunna TV da AC da sauran su. Daga haka tace min zata je ta dawo.

Kan kujera na zauna tare da ƙurawa TV ido ina kallo, a raina ina mamaki wai yau nice a nan wai a gaban wannan tangamemen TV ace wai ƙarƙashin iko na yake. Allah mai yadda ya so kenan.

Nan na ƙaraci zamana daga ƙarshe da na duba agogon da ke manne a bangon parlourn nan na gane cewa har lokacin sallar Asr yayi gashi ko zuhr ban yi ba. Da sauri na wuce toilet ɗin daman can na saba amfani da irin su a irin gidajen su Maman Khadijat, so sai ban sha wata wahala ba

nayi alwala na zo na tayar da Sallah na gabatar da salloli na. Bayan na gama na sake komawa parlourn naci gaba da kallo har magrib tayi.

Bayan na idar da sallahr magrib ne sai matar dai ta ɗazu ta sake dawowa hannayenta ɗauke da warmers ɗin abinci sai wata matar a bayan ta sanye da kalar wani uniform a jikin ta ta ajiye kayan hannun ta ta fice.

Murmushi na sakar mata kamar yadda itama naga tayi min, tace min sannu. Nima sannun na mayar mata tare da kafe ta da ido ina jira in ji mi kuma zata faɗa mun.

“Wannan abincin Dinner ɗin ki ne, wannan kuma kayan amfani ne yanzu zan nuna miki yadda zaki yi amfani ko wane abu a nan”

Ni dai babu abinda nike sai binta da kallo, kaya ne tundaga na sanyawa har zuwa kayan gyaran jiki su mayukka da na gyara gashi da takalmi da sauran su. Komai sai ta tayi min bayanin shi ɗaya bayan ɗaya daga ƙarshe tace min duk abinda ban gane ba na riƙa tambayar ta don kada a samu matsala,ni ko a raina na tambayi kai na nace matsala? Wace irin matsala to? Ganin bani da amsar ta yasa na sake mayar da hankali na ga kallon ta yayin da taci gaba da yi min bayani. Komai da aka kawo min mai kyau ne, kayan dai ne nagan su wasu iri domin ni ba kayan da sukayi daidai da tsari na bane, gaba ɗaya kayan daga riga da wando sai riga da skirt, sai kuma Abayas sun kai shida, to suka ɗai ne nikejin a raina cewa zan iya sanyawa amma su kam waɗancan haram shan giya a gidan Malam, mamaki na babu atamfa ko kala ɗaya a ciki.

Da dare ma haka na kwanta a kan gadon tare da janyo bargo na rufe jikina saboda sanyin ACn da yake ratsani.

Sati ɗaya na kwashe a gidan ba tare da na sake sanya Hajiya Hanifah a ido na ba, wannan matar da a yanzu na saba da ita Nafisat itace kaɗai ni ke gani, ta dage sosai wurin koyar da ni abubuwa waɗanda tuni nayi nisa sosai a iya wasu abubuwan wasu kuma sai dai a hankali, ni kaina idan na kalli madubi na kan yarda da cewa jiki na ya canza sosai ba kamar yadda na zo ba, tsabar hutu da cin kayan daɗi iri iri,ko gashin kai na ban san cewa ina da dogon gashi sosai mai santsi ba sai yanzu da ya ke shan gyara a wurin Aunty Nafisat domin haka tace in riƙa kiranta.

A kwana na takwas ne ina zaune, bayan na gama sallar azahar ina tunanin su Mama a raina sai ga Aunty Nafisat ta shigo tacemin in shiryo mu tafi madam tana nemana. Lokaci guda annurin fuskata ya ɓace tare da jin wani irin faɗuwar gaba take na hau karanto addu'o'i. Daman nayi wanka already, wata Abaya ce maroon colour na ɗauko na saka tare da ɗaura ɗan kwalin na sake zura hijabi na a kai na cimma Aunty Nafisat Parlour muka tafi.

Wani parlourn ne na daban mai faɗi gaske ta nuna min yayin da ta juya daga bakin ƙofar ta koma abinta. Sai da na tsaya na gama sai ta kaina sannan na shiga ɗauke da sallama a baki na.

Ganin ta yau tare da wani wanda da alama mijinta ne yasa na tsaya tun daga nesa na tsuguna a ƙasa gaba na sai tsananta faɗuwa yake tamkar wadda za'a yanka naman jikin ta.

Na jima tsugune a wurin yayin da sukayi tamkar basu ganni ba suna ta maganar su a ƙasa ƙasa. Sai daga baya ta kalle shi tace.

“Farooq she's our surrogate...”

Sai kuma ta kalle ni tace.

"Hey! Look here. Kallo nan, tashi tsaye ya ganki”

End of Chapter 19Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next