Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
Bahiyya Book One Complete Hausa Novel
Bahiyya Book One Complete Hausa Novel
By Oum Ameera
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
Bahiyya Book One Complete Hausa Novel

Bahiyya Book One Complete Hausa Novel

Author: Oum Ameera
Chapter 5 of 23
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters

Tsawon shekara bakwai da tayi a Nigeria bata fi zuwa huɗu ba Kaduna wurin Madinah, ita ma kuma Madinah ganin kalar matar da Farooq ɗin ya aura sai ta ja wa kanta layi da shiga al'amarin ta. Itama Madinah tunda aka kawo Hanifahr sau biyu ta taɓa zuwa Abuja gidan ta, a lokacin aurenta da kuma sanda ta buɗe Ɗan-Ali Decor and event center.

Daga haka sai dai ta waya idan sun samu sararin gaisawa.

Ci gaban labari.........

Zaune suke a palourn Daddyn da yamma suna tsara yadda tafiyar su zata kasance gobe. Hamrah ta kalli Hanifah tace.

“Fav Sis Yah Farooq ba zai zo bane?”

Zaro ido tayi tace.

“What! Inji wa, yana nan zuwa daga zaran mun isa in sha Allah”

Hamrah tace.

“Ah to, ai naga yah Farooq ɗin ne kamar anyi masa kafi a Nigeria duk sanda zamuyi waya na tambaye ki shi sai ki ce min yana office”

Hannunta Hanifah ta ɗauke daga kan system ɗin da take aiki a kai ta kalli Hamrah tace.

“But  I said he's coming, ba shi kenan ba”

Daga nan kuma ta kalli Daddy tace.

“Daddy please sai kayi magana da su na tura musu kalar furnitures ɗin da nike so ayi amfani da su”

Yace

“OK!”

Washe gari ƙarfe tara jirgin su ya ɗaga zuwa Dubai.

**************

Abuja

      Nigeria

Kusan watan Hanifah biyu da tafiya Farooq har yayi tafiye tafiye kusan sau huɗu zuwa Kenya da London. A duk lokacin da ya shigo gida ji yake can ƙasan ransa yana mugun jin kewar matarsa but bashi da abinda zai yi sai dai ya jira dawowar ta.

Yanzu ma kwance yake kawai a ɗakin ta yayi shiru yana ta karanta wasiƙar jaki.

Bayan ya kai kusan 1hour a kwance daga ƙarshe ya tashi kamar wanda aka tsikara ya je ya shirya ya nufi gidan Mahi.

Ganin shi tsaye a balcony ɗin gidan nasa yayi matuƙar bashi mamaki.

“Yaushe kama dawo ƙasar ban sani ba, har gaka tsaye a cikin gidana?”

Kallon sa yayi yace.

“Da safe, na kiraka baka ɗauka ba”

“Wallahi a lokacin tana hannun Amrah 'yar rigima. Juyawa yayi ya nufi Parlour yana faɗin....  Shigo ciki mana”

Parlour suka shiga yaje ya kira Husnah matarsa ta fito ta gaishe sa, Zarah da Amrat ma suka gaishe sa cikin ladabi ya amsa duk da maganar Amrat ba wani fita sosai ta ke yi ba because she's just 3years, Zarah Kuma itace babba wadda zatayi 6years.

Cikin shaƙiyanci Mahi yace.

“Husnah kawo wa gauron nan abinci dan Allah, nasan akwai yunwa tare da shi”

Harararsa Farooq yayi yace.

"You are not serious, Yanxu Haka na baro abincin da aka jera min a gida ko taɓawa banyi ba”

Mahi yace.

“Saboda mai gidan bata nan shiyasa komai ya fita a ranka ko?”

Maganar suke amma kallon Yaran da ke wasa jikin Mahi shi ya ɗauke masa hankali. Amrah ce da ƙaramin ƙanin ta Haidar wanda he's just 8 month now.

Zarah Kuma tana gefe da littafanta tana rubuta. Wannan yanda ake ta drama da Amrah da Haidar shine abinda ya burgesa, Amrah ta kafe akan Lallai sai Haidar ya sauka itama ta hau, shi kuma daga zaran an ɗaga shi sai ya fara kuka, ganin taƙi samun yadda ta ke so kawai sai ta fasa ihu ta faɗi ƙasa zata fara birgima.

Lokaci guda Farooq ya ɗaga ta sama ya ɗora ta akan thigh ɗinsa yana murmushi ya gyara mata tsorayen kalbanta da suka sha bit zuwa baya yace.

"Is ok.....”

Kuka kawai take tana nuna Mahi da Haidar tana faɗin.

" Abbah... Abbah ne, Haidar...”

“Shiihhh! It OK! Sai na yiwa Abbah duka”

Mahi kuwa sai dariya yake yana jefa Haiydar sama suna ƙyaƙyata dariya.

Husnah ce ta katse su da faɗin.

“Abbahn Zarah na gama shirya abincin”

“Owk, thank you, zo ki shiga da yaran nan ciki ya samu ya ci abincin.”

Zarah najin haka ta miƙe ta kwashe tarkacenta ta shige ciki. Husnah ta zo cikin nutsuwarta  ta karɓi Haiydar da ƙyar ta amshi Amrah daga jikin Farooq shi kuma sai murmushi yake yana lallaɓa ta har ta tafi.

Suna kan cin abincin ya ajiye spoon ɗin hannunsa ya kalli Mahid cikin damuwa yace.

“Mahi am missing Hanifah so much. Sai mu yi kusan kwana biyu bamuyi waya ba idan taga na matsa mata da kira sai ta ɗauka ta fara bani excuses ɗin cewa she's busy shi yasa bata samun cikakken lokacin magana dani ba.”

Ganin damuwa kwance ƙarara akan fuskar sa yasa a hankali Mahi ya shiga kwantar masa da hankali yace.

"Haba Farooq kamar ba ka san sha'anin kasuwa ba,kafi kowa sanin irin wahala da gwagwarmayar da ake shiga musamman idan zaka kafa branch in da ba ƙasar ka ba yafi komai wahala kafi kowa sanin haka. Is a matter of time kayi mata uzuri nasan itama ba don tana jin daɗin hakan ba da ta riga ta gama shikenan. Yanzu a ina aka tsaya da zancen”

Ajiyar zuciya ya sauke because sai yanxu yaji ɗan sauƙi sauƙin abinda ya taru ya danne masa zuciya. Yace.

“she spend almost 6weeks a Cairo Sai last two weeks suka Isa Dubai ɗin amma ta faɗamin Friday ne bukin zai gudana.”

Mahi yace.

“To ai shi kenan, kaga zuwa Friday komai ya ƙare za kuma iya dawowa tare”

Farooq yace

“Hmmm! Allah yasa”

Mahi yace

“Amin”

Miƙewa yayi tare da kallon Mahi yace.

“Thank you for the food. Ina so zan tafi Kaduna gobe da safe in sha Allah tun last month da naje har yanxu bata sake gani na ba”

“Owk! Allah ya tsare ka gaida min ita”

****************

Malali

Kaduna state

           Nigeria

Washe gari ƙarfe goma na safe a gidan Madinah tayi masa kamar yadda ya tsara.

Zaunawa yayi kusa da ita ya ɗora kansa akan gefen shoulder ɗinta for almost 15mnt relaxing him self from all the stress that he's going through. He used to feel safe and secure when ever he's with his amazing Grandma.

Sai da ya jima a haka Daga baya yayi taking deep breath sannan ya ɗago ya kalle ta yace.

“madinah zaki zo tare dani wurin taya Hanifah murna?”

Murmushi tayi tace.

“Satin nan ne gaba ɗaya busy nake gaskiya, kawai ka faɗa mata ina gaishe da ita ina mata fatan nasara”

“Owk!, zata ji in sha Allah. Ki tashi ki samamin wani abin yunwa ni keji”

“To ai kai ne baka sanar dani zuwan naka ba da yanzu ka isko komai a shirye, amma karka damu yanzun nan in sha Allah zaka samu abinda kaci”

Tashi tayi ta nufi kitchen shi kuma ya wuce ɗakin ta ya kwanta a kan gadonta.

Dakatar da masu aikinta tayi akan su bata wuri idan ta kambala sai su dawo su gaba da abinda suke.

**************

BAHIYYA

  Kamar yadda Malama Rabi ta alƙawartamin, kwatsam muna zaune da safe ina niƙa kamar kullum Nuhaira na kan sana'ar ta ta kayan miya ta shigo tace min. Ina Mama na ce mata tana ɗaki, ɗakin ta wuce ni ban ji mi suka tattauna akai ba kawai dai mama ta kira ni tace in zo maza in shirya mu tafi zanyi wa wata hajiya kitso da lalle ita da 'ƴa' ƴan ta. Nan da nan na shirya muka tafi.

Duk yadda naji ana ambatar kyau irin na garin babban birnin Abuja ban taɓa zaton kyaun shi da tsarin shi ya kai haka ba sai yau.

Gidan ma da muka shiga da Malama Rabi tunda uwata ta haife ni ban taɓa gani gida irin wannan ba. Ya haɗu iya haɗuwa ya tafi da Imani na.

A yadda naga tsarin cushion ɗin parlorn da abinda ke cikinsa a baki-baki na ɗan ɗosana ɗuwawu na zuciya ta sai bugu take tamkar ace kyat in zura da gudu.

Munfi kusan minti talatin sannan naga wata ƙofa ta buɗe wata kyakkyawar matashiyar mata ta fito wadda aƙalla zatayi arba'in zuwa arba'in da biyar tare da yara mata guda uku mabiyan juna, farare tas masu kyau da su anyi musu parking dogon gashin su da yasha gyara.

Da sauri na sauka ƙasa kamar yadda naga malama Rabi tayi nace.

"Ina kwana”

Zaunawa tayi tana mai sakin tattausan murmushi ta kalleni tace.

“Lafiya lau, kece mai Lallen kenan”

Ɗan ƙara yin ƙasa da kaina nayi nace.

“Eh nice”

Matar ta kalli Malama Rabi tace.

“To Malama sai ta fara musu Lallen ina zuwa yanzu, Ku koma can Main parlour kuyi a can”

Tashi mukayi kamar yadda tace muka koma wurin da tayi mana umurni, ware ido nayi da kyau na ƙarewa Parlourn kallo a raina nace masu kuɗi sunji daɗin su yanzu shi wannan Parlourn daban da wancan kuma a nan zamuyi zaman lalle.

“Bahiyya Ki haɗa Lallen ki fara kin san lokaci ba wahala yayi nisa”

Aikin lalle Indai na saka kaina nan da nan nike zane sa in tashi domin ni daman ina da zahin nama wurin yin abu.

Kafin kace mi har na gama tsantsare su da Lalle, kuma a yadda naga  yaran na farin ciki shi ya tabbatar min da cewa lallen ba ƙaramin  burgesu yayi ba. Ina gama musu nayi sallahr zuhr aka kawo abinci mai rai da lafiya naci nayi hani'an sannan na hau yarfa musu kitso, Ina cikin yi musu kitson ne wasu yara maza suka shigo guda biyu matasa haka ganin kamannin su da yaran da nike wa kitso shi ya tabbatar min da cewa yayyunsu ne.

Ɗayan wucewa yayi ya buɗe wata ƙaramar locker ya ɗauki takardu ya fice shi kuma ɗayan ya tsaya yana ta santin lallen wadda naji ya kira da Nimrah yana tsokanarta.

Bayan an kambala komai na wanke musu lallen matar ta fito tana ta godiya tace itama da bada ita ba amma dan Allah zuwa Friday ta kawo ni in zo in yi mata domin ta yaba da aiki na yafi burge ta fiye da na Maryam. Kasancewar yamma ta riga tayi dole zamu tafi gida.

End of Chapter 5Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next