Bahiyya Book One Complete Hausa Novel
Book chapters
Choose a chapter and continue reading.
“I'm Shuraim Tafidah by name”
Ganin na maƙale hannun na ya sashi sakin dariya yace.
"OK! I understand, please can we be friends... Yeah, friends only...”
Tsinkayo muryar Hanifah nayi cike da masifa tana faɗin.
" Malama zaki zo mu tafi ne ko kuma mubarki a nan tare da shi?”
Zare ido nayi tare da yin gaba da sauri na bar shi a baya. Biyo bayan mu yayi yana murmushi yace.
" Haba Aunty! Kin ce ba mijin ku ɗaya ba kuma yanzu kin hana ta saurare ni hakan ba dai-dai ba ne....”
Sai kuma ya juya ga Farooq yace.
“Yayah please zan iya samun numbern ta? numbernta kawai”
Ina ga tunda ƙaddarar tafiyar nan ta haɗamu ban san ya waigo ko sau ɗaya ya kalleni ba sai yanzu. Kallo na yayi sama da ƙasa kallon da ke sakani ina jin matuƙar haushin sa domin sai inga tamkar kashi ya ɗauke ni marar amfani bayan su ne suka ɗauko ni don ƙashin kansu.
Sai da ya gama kallona sannan yace.
“I don't have any business with her, ruwanta tayi abinda take so”
Wani kallon tsana na bishi da shi a raina nace wato shi gani mai zaman kanta na fito yawon Bariki kenan ko? Lallai mutumin nan ban san ƙiyayyar tasa da ni ta kai haka ba sai yau.
Hanifah kuma dariya ce ta so suɓuce mata, yanzu ace classy guy kamar wannan ya tsaya wai zai karɓi numbern wannan village girl ɗin. Bai san ta ba ne shiyasa da zaran yasan wacece ba zai taɓa marmarin haɗa class ɗin shi da ita ba.
Daga ƙarshe sukayi gaba abin su suka barni nima ba shiri na bi bayan su raina cike da tsanar halayyar da suka nuna min ni ba baiwar su ba domin ba saya ta sukayi ba. Wannan tafiya wannan tafiya ta zame min ƙarfen ƙafa nikam Bahiyya. Allah ka nuna ranar da zan yasar da ƙwallon mangoro in huta da ƙuda.
Shuraim ma cikin rashin fahimtar wannan hargitsatstsiyar tafiya tasu kawai ya juya ya kama gaban sa. A ransa yace in dai da rabon ya sa meta in sha Allah watarana za su sake haɗuwa.
*************
Finchley Road, Hampstead.
London, United Kingdom.
Tun a mota nike ta kalle kallen gine-ginen benaye masu tsawo da kuma bala'in kyau, ga garin yayi duhu sai Fitilu kake gani masu azabar kyau da ɗaukar hankali. Ba ƙaramin burgeni garin yayi ba.
A hankali naga munyi parking a dai-dai wani bene mai masifar kyau ko a ta fuska.
Suna fita nima nabi su baya, bayan mun shiga gidan wani parlour ne babba na gammu a ciki wanda yaji kayan alatu iri da iri.
A nan na samu wani cushion mai laushi na ɗosana ɗuwawu na yayin da su kuma suka shiga ciki.
Kalle kalle kawai nike ina ta mamaki a raina cewa banga kowa a gidan ba kawai sa kai sukayi suka shigo, ko gidan waye wannan oho?
Sun ɓata kusan minti yafi talatin sannan daga ƙarshe ta shigo kamar ba zata min magana ba sai kuma tace min in biyo ta.
Ba musu na tashi na bi bayanta, wata hanya ce muka bi daga cikin parlourn sai gashi ta sadamu da wani katafaren ɗaki mai ɗauke da komai na more rayuwa.
“Nan shi ne ɗakin ki daga yau har ranar da contract ɗin mu zai ƙare.”
Daga haka ta fice ni kuma na taɓe baki, domin a yadda ta ɗauke ni nima haka na ɗauke ta, duk yadda suke ɗaukata yarinya dole ina da hankali da tunani dai-dai irin wanda Allah ya bani, a hakan nasan kyautatawa kuma nasan musgunawa. duk da cewa wata zuciyar na faɗin a irin taimakon da tayimin ta cancanci girmamawa da mutuntuwa sosai daga wuri na. To amma halin da take nuna min ne bana so.
Kan gadon na faɗa rub da ciki. Ina ta tunanin wannan sabuwar rayuwar da na tsinci kaina a cikin ta, ko wace kalar rayuwar zamu gurza a nan? Allah ma sani.
Nocking naji anyi, hakan yasa ni miƙewa da sauri naje na buɗe, wani mutum na gani fari ɗauke da tiren abinci a hannun sa. Jin yayi min wani kalar yaren da ban gama tantance cewa turanci ba ne ko yaya yasa na juya abina na koma ciki. Baya na ya biyo tare da ajemin tiren ya na sake yi min magana. Kamar in tartse shi da mari haka naji, banzaye kawai marasa aikin yi. Wata zuciyar ta ce min ko laifin mi sukayi min Oho!
Yana fita na sauko na bubbuɗe abincin, daman can yunwa na ciciyata. Hmmm! Kawai Kallon kalar abinci nike a raina ina faɗin uban waye zai ci muku wannan abun.
Naman kajin na zage na cinye duk da ba magin albarka a ciki, na shanye madarar da na fiso na ɗora da shan fruit da akayi slizing ɗin su a wani haɗaɗɗen bowl. Nan naji cikina ya ɗauka sannan na tashi na shige toilet na yi wanka na fito na buɗe kayana da aka shigo min da shi na ɗauki wasu riga da wando masu taushi ga faɗi na saka sannan na sanya hijabi na tayar da sallah.
Bayan na gama salloli na na daɗe ina Addu'a daga bisani na tashi na kwanta akan gadon, ganin bacci ya kasa ɗaukata yasa na tashi na janye labulen kantamemin windown na tsaya a kai, Ina ta kallon sabuwar duniyar da tsinci kaina a ciki. Daga kallon sararin samaniya ne kaɗai zaka gane cewa duhun dare ne, amma daga ka mayar da kallon ka ƙasa zaka ga hasken Fitilu mabanbanta masu walwali da ɗauke hankali suna ta aikin bada haske, ga motoci suna wucewa gwanin burgewa.
*************
FAROOQ
Bayan ya kambala duk wani muradinsa na daren yau, zaunawa yayi ya janyo system ɗin sa yana duba aikin da Mahi ya tura masa tun daren jiya.
Yana cikin aiki ne ta turo ƙofar ta shigo, sanye take cikin wasu night wears masu bala'in santsi da walwali pink color, kallon ta yayi tare da sakin murmushi yace.
“You look beautiful dear”
Haye jikin sa tayi tana murmushi itama tace.
“Really?”
Lumshe idanuwansa yayi yace.
“Yeah!. So can we get down to business? I'm always ready and available for that...”
Dariya tayi tace.
"Nifa wani zubin sai inga kwata kwata baka da kunya at all”
Zaro ido yayi da mamaki kwance a fuskar sa yace.
“Oh! A haka kika ɗauki abin Hanifah? Don't forget that you are my wife,I mean my Halal, to miye abin rashin kunya a ciki bayan sunnah ce mai ƙarfi, ni dai matuƙar za'a bani to zan karɓa in yi godiya ba da wasa ba....”
Miƙewa tayi ta koma kan gadonsa ta kwanta tana faɗin.
"That's not what brought me here, Wallahi a matuƙar gajiye ni ke, kawai ina so in faɗamaka mungama arrangement da Doctor Nicho gobe zamuje hospital ɗin.....”
Wayarsa ce tayi ƙara da sauri ya ɗaga tare da sakin murmushi duk da cewa baya gabanta. Sallama ya fara mata sannan ya gaishe ta daga can ɓangaren tace.
“Faruku ya kuka isa? Da fatan kuna lafiya”
Yace.
“We are fine Madinah, ya gida ya kike”
Tace.
“Komai Alhamdulillah. Allah ya taimaka ya bada sa'ar abinda aka je nema, ka gaisar da matar taka”
Cikin daɗin addu'ar ta yace.
“Amin Madinah, thank you so much, Hanifah zata ji in sha Allah”
Suna gama wayar Hanifah ta kalle shi tace.
“Farooq what did you tell madinat??”
Cikin mamaki yace.
“What did I tell her? Kawai na gaya mata cewa we are going for a business trip for one year, and you know it cewa Madinah is an understandable and supporting woman, fatan alheri kawai tayi mana.”
"While that's good to hear...”
Daga haka ta miƙe tana zabga hamma tace.
“I'm feeling sleepy, good night love, gobe zamu tattauna ko a mota ne”
Da sauri ya kalleta kafin ta iyarda ficewa yace.
“Why! Why Hanifah? Miyasa kullum kike son ɓatamin ne, ko tausayi na bakya yi, Hanifah sex is life....”
Da sauri ta saka hannunta ta toshe kunnen ta tare da yin waje da sauri tana dariya.
Kallon ta kawai yake har ta ɓacewa ganin sa. Ya ma rasa wane kalar tunanin zaiyi akan Hanifah, she's always always busy, Bayan Kuma yasan auren su shine kan gaban komai, amma idan zai kwana ya na faɗa mata ba zata amince ba,gani take kawai wannan kawai ra'ayin sa ne.
**************
BAHIYYA
Ganin duhun dare da wayewar gari da kuma tafiyar lokaci a agogon bangon da ke manne a ɗakin kaɗai ke nuna min shigowar dare da wayewar gari. Wani abu ne ajiye a side bed drawer Kamar alarm yake bugawa daga zaran lokacin sallah yayi sai ya fara kiran sallah.
Nafi kwana goma ban sanya kowa a ido na ba, tun ranar da muka zo ban sake ganin ko ɗaya daga cikin su ba. Abinci ne kawai wannan kukun ke kawo min ko wane lokaci wanda tun bana iya ci har yanzu dole na koyawa kaina don dole gudun yunwa amma kam shan madara da cin nama bana wasa da shi.
Fatar jiki na sai ƙara sheƙi ta ke tana ƙara luwui luwui tsabar hutu da shan sanyin AC mai daɗi. Can ƙasan zuciyata kuma kewar Mama ce ta addabeni, idan abin yayi min yawa har kuka nake. Ga kaɗaici duk yabi ya ishe ni, tashoshin da ke cikin wannan TV ɗin duk ba masu daɗi bane kamar na gida Nigeria. Shiyasa ban damu da kunna TVn ba.
.......... Ina tsaye jikin window kamar kullum ina kalle kalle na ta murɗa handle door ɗin ta shigo.
Kallonta kawai nayi tare da kau da kaina nace mata ina kwana sama sama naci gaba da kallon wajen da nike ba tare da sanin taji ko bata ji ba. Kallona tayi sama da ƙasa tamkar mai nazartar wani abu sannan tace.
“Zamuyi magana ne”
Juyowa nayi na kalle ta da kyau nace.
“Ina jinki”
Taɓe baki tayi sannan ta fara magana kamar haka.
More Hausa novels
Abban Sojoji Book 2 Complete Hausa Novel
By Hafsat Bature
Aljanar Fatima Book 1 Complete Hausa Novel
By Bilyn Abdul
Hayatul Mahayeen Part One Complete Hausa Novel
By Npeedy
Hibbatullah Book 1 Complete Hausa Novel
By Real Maman Teddy
Fadeelah Book 1 Complete Hausa Novel
By Bilyn Abdul
A Babban Gida Part 1 Complete Hausa Novel
By M Shakur
Search across the available chapters.