Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
By Billyn Abdul
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

Author: Billyn Abdul
Chapter 1 of 122
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.
Free access is active. You can keep reading and download during this access window.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters
Chapter 1 Reading now Chapter 2 1,690 words Chapter 3 1,680 words Chapter 4 1,637 words Chapter 5 1,676 words Chapter 6 1,594 words Chapter 7 1,597 words Chapter 8 1,655 words Chapter 9 1,192 words Chapter 10 1,647 words Chapter 11 1,678 words Chapter 12 1,698 words Chapter 13 1,656 words Chapter 14 1,617 words Chapter 15 1,693 words Chapter 16 1,658 words Chapter 17 1,692 words Chapter 18 1,521 words Chapter 19 1,684 words Chapter 20 1,600 words Chapter 21 1,688 words Chapter 22 1,589 words Chapter 23 1,692 words Chapter 24 1,344 words Chapter 25 1,685 words Chapter 26 1,699 words Chapter 27 1,685 words Chapter 28 1,660 words Chapter 29 1,664 words Chapter 30 1,468 words Chapter 31 1,665 words Chapter 32 1,699 words Chapter 33 1,682 words Chapter 34 1,587 words Chapter 35 1,689 words Chapter 36 1,687 words Chapter 37 1,610 words Chapter 38 1,677 words Chapter 39 1,679 words Chapter 40 1,632 words Chapter 41 1,698 words Chapter 42 1,661 words Chapter 43 1,690 words Chapter 44 1,277 words Chapter 45 1,514 words Chapter 46 1,679 words Chapter 47 1,689 words Chapter 48 1,694 words Chapter 49 1,623 words Chapter 50 1,616 words Chapter 51 1,618 words Chapter 52 1,499 words Chapter 53 1,697 words Chapter 54 1,686 words Chapter 55 1,630 words Chapter 56 1,694 words Chapter 57 1,548 words Chapter 58 1,682 words Chapter 59 1,389 words Chapter 60 1,613 words Chapter 61 1,497 words Chapter 62 1,686 words Chapter 63 1,669 words Chapter 64 1,675 words Chapter 65 1,613 words Chapter 66 1,697 words Chapter 67 1,627 words Chapter 68 1,670 words Chapter 69 1,638 words Chapter 70 1,682 words Chapter 71 1,543 words Chapter 72 1,563 words Chapter 73 1,611 words Chapter 74 1,680 words Chapter 75 1,616 words Chapter 76 1,629 words Chapter 77 1,662 words Chapter 78 1,575 words Chapter 79 1,507 words Chapter 80 1,608 words Chapter 81 1,674 words Chapter 82 1,651 words Chapter 83 1,516 words Chapter 84 1,631 words Chapter 85 1,699 words Chapter 86 1,652 words Chapter 87 1,633 words Chapter 88 1,651 words Chapter 89 1,674 words Chapter 90 1,606 words Chapter 91 1,688 words Chapter 92 1,593 words Chapter 93 1,654 words Chapter 94 1,396 words Chapter 95 1,655 words Chapter 96 1,599 words Chapter 97 1,693 words Chapter 98 1,665 words Chapter 99 1,653 words Chapter 100 1,658 words Chapter 101 1,700 words Chapter 102 1,639 words Chapter 103 1,651 words Chapter 104 1,671 words Chapter 105 1,547 words Chapter 106 1,695 words Chapter 107 1,585 words Chapter 108 1,675 words Chapter 109 1,641 words Chapter 110 1,674 words Chapter 111 1,509 words Chapter 112 1,615 words Chapter 113 1,674 words Chapter 114 1,691 words Chapter 115 1,694 words Chapter 116 1,688 words Chapter 117 1,681 words Chapter 118 1,656 words Chapter 119 1,670 words Chapter 120 1,698 words Chapter 121 1,689 words Chapter 122 1,691 words

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO23*

.. Cakk Abba ya ɗauketa a hannunsa, ya soma takawa zuwa cikin ɗakin Ammi. Be ajjeta ba, se da ya ƙarasa kan gadon ya ajjeta. Juyawa ya yi zuwa side fridge ɗin Ammin dake gefe, ya saka hannu ya buɗe ya ɗauko ruwa me ɗan sanyi sannan ya matsa kusa da Lulun. Ɗan zubawa ya yi a hannunsa kafin ya kai kan fuskarta a hankali ya shafa, ba ta motsa ba, kamar wadda ba a shafawa komai ba. Ƙirjin Ammi ya sake bugawa, se ta ƙarasa hawa kan gadon, ta ɗauki kan Lulu ta ɗora a kan cinyarta, daidai lokacin da Abba ya sake kai ruwan fuskarta a karo na biyu. Ƙatuwar ajiyar zuciya ta sauke sannan ta soma buɗe jiƙaƙƙun idanunta. A kan Abba idanunta suka fara sauka, Abba ya lumshe idanu yana sauke ajiyar zuciya lokaci ɗaya yana furta

"Alhamdulillah.." Daga haka se kawai ya miƙe ya fice daga ɗakin, dan tun yanzu zuciyarsa na neman karyewa a kan 'ya'yan nasa, ba kuma ya so ya cigaba da zama anan ɗin har hakan ya janyo ya fara tunanin ya aikata ba daidai ba. Tsam Ammi ta rungumeta cikin jikinta cikin matuƙar farin ciki mara misaltuwa. Didi ma kasa sukuni ta yi se da ta ƙarasa ta rungume su. Ammi ta haɗa 'ya'yan nata waje ɗaya ta rungume. Se a lokacin Lulu ta sake tuna abin da ya faru ɗazun, zuciyarta ta buga da ƙarfin gaske, se ta ɗago da sauri muryarta na sake yin rawa fiye da yadda take, wata ƙwalla kwance a cikin kyakykyawar ƙwayar idanunta. Hannunta na wani irin rawa tace bayan ta tashi daga jikin Ammi

"Ammi mafarki na yi koh? Ammi wani mummunan mafarki na yi koh? Ammi don Allah ki ce min mafarki ne wannan ɗin ba gaske ba. Don Allah Ammi kin ji.." ta ƙarashe tana girgiza kai, gami da fashewa da wani sabon kuka. Janta Ammi ta sake yi cikin jikinta, itama tana jin wata sabuwar ƙwalla na taho mata.

"Ki yi haƙuri Afaaf.. ki dena wannan kukan, babu abin da ze ja miki se ciwon kai.."

"Ammi ba ki ce min ehh ba. Ammi ba ki faɗa min ba gaskiya bane. Wannan wane irin mafarki ne? Wannan wane irin mummunan mafarki ne? Ta yaya ma wannan abin ze yiwu? Ammi sake ni na je wajen Abba ya tabbatar min da wasa yake mana. Ammi wallahi har abada ba zan sake wani laifi a makaranta ba. Ammi na dena wallahi. Na dena bazan sake ba. Na san abin da Abba ke buƙatar ji kenan daga bakina, kuma gashi na faɗa. Don Allah Ammi ki sanar da shi na dena, wallahi na tuba na bi Allah.." yanzun ma ƙarasawa ta yi tana sakin kuka. Gaba ɗaya Didi se ta ji kamar ita ba a faɗa mata an ɗaura mata aure da wani ba, gaba ɗaya se ta ji kamar bata da wata damuwa idan banda ta er uwarta. Yanayin da take ganinta a ciki a yanzun ya danne komai. Wannan kukan da take ta yi ita kanta shi ke ɗaga mata hankali, gashi se magana take kamar wadda bata a hayyacinta.

"Ya isa haka.. Ki yi shiru nace koh?" Ammi ta faɗa tana goge idanunta. Ba dan taso ba haka ta haƙura ta cigaba da zama a jikin Ammin. Tun tana kukan a fili har tazo ta gaji ta koma sheshsheƙa har daga ƙarshe baccin wahala ya kwasheta. Se a lokacin Ammi ta sauke ajiyar zuciya, ta ɗaga kai ta kalli Didi dake zaune kusa da ita. Idanunta duk sun yi face_face da hawaye, gaba ɗaya kamar ba Didin ba, se ta miƙa mata hannu, babu ɓata lokaci ta ƙarasa Ammin ta haɗasu ta rungume. Se a lokacin ta samu damar fashewa da kuka gwanin ban tausayi.

"Kema karya min zuciyar za ki yi Afrah?" Ammi ta faɗa a sanyaye. Girgiza kai Didi ta yi se dai ta kasa tsaida hawayen, da ƙyar ta iya buɗe baki tace

"Ammi Abba...!" Se kuma ta yi shiru, sannan ta ɗora da

"Ammi ban san wanda Abba ya aura min ba.. Abba be faɗa min ba Ammi.." Ɗan runtse idanunta Ammi ta yi, kafin a hankali ta ɗora hannunta a kan Didi tace

"Ina saka ran samun sassauci daga gare ki Didi. Don Allah ko wane ne Abbanku ya aura miki ki yi haƙuri, ba ze taɓa zaɓa muku abin da ze ce cuceku ba. Idan har kika damu, toh shi kenan Afaaf kuma ta samu dama. Kin ga kenan ta duka ɓangarori biyun Abba ze yi nadamar abin da ya yi, bayan kuma hakan ba laifi bane. Idan kuwa kika haƙura, ke zaki ɗora er uwakki a kan hanya, kamar yanda kika saba. Dan haka ki dena kukan nan, kin san dai yanzun nan kanki ze soma ciwo.." Ammi ta ƙarasa maganar cikin rarrashi. Ba ta iya cewa komai ba, illa zuciyarta da ta cigaba da bugawa. Ta yi shiru tana tunanin yadda rayuwarsu ta gaba zata fara. Aure a ƙananun shekaru irin nasu, da kuma mijin da basu sani ba, baya sonsu basa son shi.

"Allah ze kawo mana mafita.." Ammi ta faɗa kamar ta san abin da Didin ke tunani.

... "Ina ɗana yake Yallaɓai? Me ya same shi haka? Ya ka yi aka kawo shi wannan asibitin?" Mom ta yi duka waɗannan tambayoyin a lokaci guda. Ajiyar zuciya Daddy ya sauke kafin yace

"Duka waɗannan tambayoyin a lokaci ɗaya?" Daddy ya faɗa yana kallanta.

"Don Allah so nake na ga ɗana, yana ina?"

"Mu je.." Daddy ya faɗa yana yin gaba. Babu ɓata lokaci Mom ta bi bayansa hankali tashe, burinta kawai ta ga shalelenta ta kuma san abin da ke damunsa.

"My boy.." ta faɗa tana kai hannunta kan fuskar Bad ɗin dake kwance har lokacin kamar matacce. Ganin da ta yi be motsa ba ya sanyata kallan Daddy tace

"Bacci yake yi ne? Wai me ya same shi?"

"Ki kwantar da hankalinki. Ze farka zuwa anjima In Sha Allah."

"Har yanzu ba ka faɗa min abin da ya same shi ba Yallaɓai.." Kafin Daddyn yace komai, likita ya shigo cikin ɗakin. Bayan sun gaisa da Daddy cikin girmamawa sannan ya ƙarasa inda Bad ke kwance, ya duba shi sosai sannan ya kalli Daddy har lau dai cike da girmamawa yace

"Har yanzu be motsa ba?"

"Ehh.." in ji Daddy.

"Ohk a cigaba da addu'a. Kamar dai yadda muka faɗa zuwa anjima In Sha Allah ze farka.."

"Allah ya yadda.."

"Likita me ke damun ɗana?" Mom ta faɗa tana kallan Doctor ɗin. Kallanta Daddy ya yi, kafin ya maida dubansa kan Doctor ɗin yace

"Za ka iya wucewa.."

"Ohk Sir.." Daga haka ya fice daga ɗakin.

"Abin da yafi dacewa ki zauna ki masa addu'a ya samu ya farka, ba tambaye tambaye ba.." Daddy ya faɗa yana kallan Mom.

"Wai abun har ya kai haka?" Mom ta faɗa a sanyaye.

"Kar ki ɗaga hankalinki.." Se ta sauke ajiyar zuciya tunda dai ta ga ba faɗa mata za a yi ba, se ta nemi waje ta zauna kawai tana kallan ɗan nata cike da tausayawa.

... "Sannu da zuwa.." Ummeey ta faɗa tana kallan Abeey.

"Yawwah.." ya yi maganar yana neman waje ya zauna. Murmushi Abeey ya yi kafin yace

"Na san kin ƙagu ne ki ji abin da zan faɗa.." Ɗan yaƙe ta yi tace

"Ƙwarai kuwa Malam.. Ka fita kai ba cikakkiyar lafiya ba.. ga kuma wannan zancen da yafi kama da almara.."

"Kwantar da hankalinki.. Ni kam garau nake jina musamman ma da yau ɗaya daga cikin burina ya cika. Wato na aurar da Affan.." Cike da mamakin dai Ummeey tace

"Wai Malam dama da gasken ne?" Girgiza kai Abeey ya yi kafin yace

"Ban da abinki, wannan ɗin ai ba maganar da za a yi wasa a kanta bace. Da gaske a yau ɗin na aurar da shi. Kin ga kema burinki ya cika, ko dama ba abin da kike so ba kenan?" Ya tambaya yana kallanta.

"Ikon Allah.." Ummeey ta faɗa cike da mamaki. Se kuma ta ɗora da

"Toh Alhamdulillah.. Allah ya sanya alkhairi.. ya basu zaman lafiya.. ya haɗa kansu. Ni kuma ina nan ina jiran zuwan sirikata.." ta ƙarashe tana murmushi. Murmushi Abeey ya yi yace

"Ameen Ameen.."

"Amma Malam.. kana ganin Affan ze iya riƙe mata kuwa? Duk uban hidindimun nan na aure da ake yi.. abubuwan kamar da yawa, kuma na san dai mutane ba zasu ɗauki ɗiyarsu su bamu ba tare da an gabatar da abubuwa na al'ada ba.."

"Haka ne.." Abeey ya faɗa bayan ya sauke ajiyar zuciya. Se kuma ya ɗora da

"Allah ze hore yadda za a yi In Sha Allah.."

"Toh Allah ya yadda.."

"Ameen.." Abeey ya amsa kafin yace

"Har yanzu be shigo ba?"

"Wallahi kuwa.. dama yace ze daɗe.." Ummeey ta bashi amsa.

"Ko yaushe ya dawo, ki faɗa masa ina son ganinsa ko da bana nan.."

"Toh Malam.."

... Kamar a mafarki ta ji tarinsa ƙasa_ƙasa. Da sauri ta miƙe ta ƙarasa inda yake tana faɗin

"Areef.." Cigaba da tarin ya yi se dai har lokacin a hankali.

"Na gode maka Allah.." Mom ta faɗa cikin matuƙar farin ciki tana kai hannunta ta riƙo Bad ɗin. Fara miƙewa ya yi cike da kasala yana cigaba da yamutse fuska. Mom ta taimaka masa ya tashi zaune. Jin kansa yake gaba ɗaya wani gingirin kamar wani sabo aka ɗora masa bayan na shi. Hannu ya kai ya ɗan dafe kansa daidai lokacin da ya ɗan saki ƙaramin tsaki.

"Sannu ka ji yarona..?" Mom ta faɗa tana kallansa. Kamar be ji ta ba, dan kuwa bece komai ba. Se da ya ɗan lumshe idanunsa sannan ya soma ƙoƙarin sauka daga kan gadon.

"Ina zaka je?" Mom ta tambaya.

"Pls Mom.." ya faɗa da dashashshiyar muryarsa.

"Don Allah ka koma ka zauna. Ba ka da lafiya fa.."

"Mom.." ya sake faɗa cikin kaushi. Girgiza kai ta yi tana faɗin

End of Chapter 1Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Login to Save Next