Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
By Billyn Abdul
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

Author: Billyn Abdul
Chapter 61 of 122
About 7 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.
Free access is active. You can keep reading and download during this access window.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters
Chapter 1 1,645 words Chapter 2 1,690 words Chapter 3 1,680 words Chapter 4 1,637 words Chapter 5 1,676 words Chapter 6 1,594 words Chapter 7 1,597 words Chapter 8 1,655 words Chapter 9 1,192 words Chapter 10 1,647 words Chapter 11 1,678 words Chapter 12 1,698 words Chapter 13 1,656 words Chapter 14 1,617 words Chapter 15 1,693 words Chapter 16 1,658 words Chapter 17 1,692 words Chapter 18 1,521 words Chapter 19 1,684 words Chapter 20 1,600 words Chapter 21 1,688 words Chapter 22 1,589 words Chapter 23 1,692 words Chapter 24 1,344 words Chapter 25 1,685 words Chapter 26 1,699 words Chapter 27 1,685 words Chapter 28 1,660 words Chapter 29 1,664 words Chapter 30 1,468 words Chapter 31 1,665 words Chapter 32 1,699 words Chapter 33 1,682 words Chapter 34 1,587 words Chapter 35 1,689 words Chapter 36 1,687 words Chapter 37 1,610 words Chapter 38 1,677 words Chapter 39 1,679 words Chapter 40 1,632 words Chapter 41 1,698 words Chapter 42 1,661 words Chapter 43 1,690 words Chapter 44 1,277 words Chapter 45 1,514 words Chapter 46 1,679 words Chapter 47 1,689 words Chapter 48 1,694 words Chapter 49 1,623 words Chapter 50 1,616 words Chapter 51 1,618 words Chapter 52 1,499 words Chapter 53 1,697 words Chapter 54 1,686 words Chapter 55 1,630 words Chapter 56 1,694 words Chapter 57 1,548 words Chapter 58 1,682 words Chapter 59 1,389 words Chapter 60 1,613 words Chapter 61 Reading now Chapter 62 1,686 words Chapter 63 1,669 words Chapter 64 1,675 words Chapter 65 1,613 words Chapter 66 1,697 words Chapter 67 1,627 words Chapter 68 1,670 words Chapter 69 1,638 words Chapter 70 1,682 words Chapter 71 1,543 words Chapter 72 1,563 words Chapter 73 1,611 words Chapter 74 1,680 words Chapter 75 1,616 words Chapter 76 1,629 words Chapter 77 1,662 words Chapter 78 1,575 words Chapter 79 1,507 words Chapter 80 1,608 words Chapter 81 1,674 words Chapter 82 1,651 words Chapter 83 1,516 words Chapter 84 1,631 words Chapter 85 1,699 words Chapter 86 1,652 words Chapter 87 1,633 words Chapter 88 1,651 words Chapter 89 1,674 words Chapter 90 1,606 words Chapter 91 1,688 words Chapter 92 1,593 words Chapter 93 1,654 words Chapter 94 1,396 words Chapter 95 1,655 words Chapter 96 1,599 words Chapter 97 1,693 words Chapter 98 1,665 words Chapter 99 1,653 words Chapter 100 1,658 words Chapter 101 1,700 words Chapter 102 1,639 words Chapter 103 1,651 words Chapter 104 1,671 words Chapter 105 1,547 words Chapter 106 1,695 words Chapter 107 1,585 words Chapter 108 1,675 words Chapter 109 1,641 words Chapter 110 1,674 words Chapter 111 1,509 words Chapter 112 1,615 words Chapter 113 1,674 words Chapter 114 1,691 words Chapter 115 1,694 words Chapter 116 1,688 words Chapter 117 1,681 words Chapter 118 1,656 words Chapter 119 1,670 words Chapter 120 1,698 words Chapter 121 1,689 words Chapter 122 1,691 words

"Na haɗaka da Allah fa.." ta faɗa kamar ba Lulu ba. Saboda yanda hatta muryarta ta koma ta waɗanda za a tausayawa. Se a lokacin ya saketa yana sake riƙe dariyarsa ya sauka daga kan gadon. Yana sakin nata ta yi saurin komawa gefe ta takure waje ɗaya kamar me jin sanyi. Duk wani tsoron Gwanin da ta ji a ranar nan ya sake dawo mata sabo. Amma duk da haka da ta ga ya saketan se da ta saci kallansa ta jefa masa harara tana sake jan bargo ta lulluɓe ilahirin jikinta. Sarai yana lura da duk wani abu da take yi. Shi dai har yanzu ya kasa dena dariya saboda tsoron nan nata ya ba shi dariya ainun.

... Da sallama Baba Atine ta shigo ɗakin. Didi ta amsa sallamar da murmushi kan fuskarta.

"Sannu da zuwa Baba Atine.." Didi ta faɗa.

"Yawwah ɗiyata.." Ta yi maganar tana neman waje ta zauna. Suka gaisa cike da sabo.

"Ina kwana..?" Little ya faɗa yana kallan Baba Atinen. Hannu Baba Atine ta saka ta janyo Little ɗin da murmushi kan fuskarta tace

"Lafiya ƙalau yarona.. ka na lafiya..?"

"Ehh.." ya faɗa yana gyara zamansa a kan cinyarta.

"Kin shirya ne 'Yata?" Baba Atine ta tambaya bayan ta maida dubanta kan Didi. Ɗan ɓata fuska Didi ta yi sannan tace

"Ki yi haƙuri Baba.. kin ga yanzu nake so na shirya." Murmushi Baba Atine ta yi kana tace

"Ai babu koma 'yata. Bari kawai na ɗauki Areef mu je sashen Hajiya. Idan kin gama se ki iskemu a can."

"Tohm shi kenan.." Didi ta faɗa. Miƙewa Baba Atine ta yi hannunta riƙe da na Little.

"Didi se mun dawo." Little ya faɗa yana ɗaga mata hannu bakinsa kamar ze faɗo dan dariya. Duk saboda za a fita.

"Toh Little.." ta ba shi amsa ita ma tana ɗaga masa hannu. Daga haka Baba Atine ta ja hannun Little ɗin suka fice daga ɗakin. Hango Bad Man da ya yi kafin su fice daga ɗakin ya sanya shi sakin hannun Baba Atine ya tafi da gudu wajen shi. Ita sam ba ma ta lura da Bad Man ɗin ba. Dan haka da sauri tace

"Areef!!" Dakatawa ya yi daga inda yake. Ya ɗaga idanunsa ya sauke su kan Baba Atine da yake da tabbacin ita ce ta kira sunan shi. Daidai lokacin kuma da Little ya riƙo hannunsa yana faɗin

"Uncle.." Se a lokacin Baba Atine ta lura da shi. Cike da girmamawa ta ƙaraso kanta a ƙasa tace

"Barka da wannan lokaci Yallaɓai.."

"Barka.." Ya amsa a taƙaice. Se ta maida dubanta kan Little tace

"Taho mu tafi.." Maƙe kafaɗa ya yi yana wani cuno baki lokaci ɗaya kuma yana sake riƙe hannun Bad Man ɗin da kyau. Sauke idanunsa Bad Man ya yi a kansa yace

"Me ye sunanka?"

"Areef.." Murmushi ne ya wanzu a kan fuskarsa jin da ya yi sunansu iri ɗaya. Karon farko kuma da ya ji yaron ya burge shi. Se ya saka hannunsa ya riƙo shi, daidai lokacin da ya maida dubansa kan Baba Atine yace

"Ki je kawai.." Babu musu ta amsa da

"Toh Rankayadaɗe.." Daga haka ta fice daga ɗakin. Shi ma ficewa ya yi daga ɗakin har lokacin hannunsa riƙe da na Little. Kai tsaye parking space ya wuce inda yake da tabbacin Kaseem na jiransa. Aikuwa yana tsaye hannunsa sarƙe a ƙirjinsa yana jiran fitowar Bad Man ɗin. Tun daga nesa yake sake buɗe idanunsa yana kallan yaron da ke hannun Bad Man. Har dai zuwa lokacin da suka kusa ƙarasowa.

"Laaa!!" Little ya faɗa yana kallan Kaseem bayan ya dakata. Se kuma ya ƙarasa da gudu ya rungume shi. Tabbatar da lallai wannan ɗin Little ne ya sanya Kaseem saka hannu ya rungume shi. Kafin ya buɗe baki yace

"Areef.. Ya na ganka a nan?"

"Wajen Didi na zo.." Ya faɗa bayan ya ɗago yana kallan Kaseem ɗin.

"Didi kuma?" Kaseem ya faɗa cike da mamaki. Cike da mamakin dai Bad Man ke kallansu. Se dai hakan be nuna ba a kan fuskarsa. Tambayar da ke ta masa lugude cikin kai ita ce ta sanya shi gyara tsayuwa yace yana kallan Kaseem

"Da ma ka sansu ne?" Se da ya kalli Bad Man ɗin sannan ya soma faɗin

"Ehh.. na sansu sosai.. Musamman ma yayar tasa. Dan mun yi soyayya da ita a da, amma Allah be yi zan aureta ba. Se dai kuma a yanda na sani yanzu haka ta yi aure shi ya sa ban fahimci maganar Areef ba." Harɗe hannayensa a ƙirji Bad Man ya yi yana kallan Kaseem kamar me son gano wani abu daga kan fuskar tasa. Kaseem na shirin sake yin magana Bad Man ya katse shi da faɗin

"Ni ne mijin nata.." Ya faɗa cikin basarwa. Ɗaga ido Kaseem ya yi ya kalli Bad Man irin kallan mara hankalin nan. Duk da be san Bad Man ɗin na shaye shaye ba amma tabbas yau yana da yaƙinin ya sha wani abu. Ta yaya ma shi ɗin ze kasance mijin Afrah? Ta yaya ma hakan za ta faru? Cigaba da masa kallan tuhumar nan ya yi yana jira ya sake jin wani abu ya fito daga bakinsa. Se dai shi ma ɗin kawai kallansa yake yi ba tare da yace uffan ba. Daidai nan Didi ta fito daga sashensu sanye cikin doguwar riga da hijab ɗinta madaidaici. Ta yi wani shahararren kyau kamar wadda ta kwashe awanni tana shiryawa. Kamar wanda aka ce ya ɗaga kai yana ɗagawa kuwa idanunsa suka sauka a kan Didin da ke cigaba da takawa. Haka nan kawai ya ji zuciyarsa ta buga. "Ka da fa a ce da gaske Bad Man ɗin yake masa?" Ya tambayi kansa cike da fargaba. Haka nan kawai ta ji ido na yawo a kanta. Duk se ta ji ta tsargu, dan haka ta ɗaga kanta dan ganin me kallan nata. Cikin sakannin da basu wuce 5 ba suka yi 4 eyes ita da Kaseem. Babu shiri ta dakata a inda take zuciyarta na soma gudu. Kawai se aka shiga kallan kallo tsakaninsu, kowa da abin da yake saƙawa a ransa..

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO56*

___ A hankali Bad Man ya ɗaga idanunsa ya kalli inda Kaseem ɗin ke kallo, dan shi sam be san da wanzuwar Didi a wajen ba. Se kuwa idanunsa suka sauka a kan Didi wadda zuwa yanzun ta sauke idanunta daga kan Kaseem ɗin. Ya yin da shi kam Kaseem ko gezau har zuwa lokacin idanunsa na kan Didin. Wato lokacin da Bad Man ya maido da dubansa kan Kaseem. Haka nan kawai ya ji ransa ya sosu, ba kuma dan komai ba se dan yanda ta kasance matar aure. Duk da shi dai ya san ba sonta yake yi ba, amma kuma abin da Kaseem ɗin yake yi sam be dace ba. Ya kuma zama dole ya taka masa burki tun kafin ya ƙarasa fusata shi. Ya ɗan runtse idanunsa kafin ya buɗe su. Cikin takun nan nasa ya soma takawa zuwa inda Didi take. Ba tare da ta lura da hakan ba. Se kawai tsintar shi ta yi dab da ita kamar wanda ke shirin rungumeta. Cike da fargaba ta yi saurin yin baya a ranta tana jin haushin kanta da ta tsaya kallan Kaseem ɗin. Yanzu idan ya ganta da wane ido za ta kalle shi? Duk da ta san be ɗauketa matsayin matarsa ba amma ko babu komai hakan da ta yi be dace ba. Sake matsawa ya yi kusa da itan, daidai lokacin da ƙirjinta ya wani irin bugawa ta ji ina ma ƙasa ta tsage kawai ta shige da dai wannan mutumin yace ze hukuntata. Ba ta yi tsammani ba se jin tattausan hannunsa ta yi a tsintsiyar hannunta ya riƙe da ƙarfin gaske. Ba ta san lokacin da ta ɗaga kai ta kalle shi ba. Ya watsa mata wani kallo da ba ta taɓa ganin ya yi kalarsa ba. Duk se ta sake jin jikinta ya yi mugun sanyi har ba ta san lokacin da ta tara ƙwalla cikin idanunta ba. Ba tare da yace komai ba ya sake riƙe hannun gam yanda ya san za ta ji zafi. Aikuwa se da ta runtse idanunta tana ji kamar ta fashe da kuka. Se ya soma takawa zuwa sashensu. Ba tare da ya sake kallan inda Kaseem ke tsaye ba suka shige cikin ɗakin. Se a lokacin ya saki hannun nata sannan ya juya da niyyar ficewa. Se kuma ya juyo ya kalleta kamar wanda aka wa dole yace

"Idan na sake ganin ƙafarki a wajen sashen nan za ki ga abin da zan miki.." Ya ƙare yana yin ƙwafa. Be jira tace komai ba ya fice dan zuwa ya ji da Kaseem. Hannunta ta riƙe tana ji kamar har yanzu be saketa ba saboda zafi. Ta kwaɓe fuska kamar za ta yi kuka. Duk haushin kanta ya ƙi sakinta. Tuna abin da ya faɗa ne ya sanyata wucewa ɗakinta ba tare da sake tunawa da inda za ta je ba.

End of Chapter 61Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next