Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
By Billyn Abdul
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

Author: Billyn Abdul
Chapter 74 of 122
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.
Free access is active. You can keep reading and download during this access window.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters
Chapter 1 1,645 words Chapter 2 1,690 words Chapter 3 1,680 words Chapter 4 1,637 words Chapter 5 1,676 words Chapter 6 1,594 words Chapter 7 1,597 words Chapter 8 1,655 words Chapter 9 1,192 words Chapter 10 1,647 words Chapter 11 1,678 words Chapter 12 1,698 words Chapter 13 1,656 words Chapter 14 1,617 words Chapter 15 1,693 words Chapter 16 1,658 words Chapter 17 1,692 words Chapter 18 1,521 words Chapter 19 1,684 words Chapter 20 1,600 words Chapter 21 1,688 words Chapter 22 1,589 words Chapter 23 1,692 words Chapter 24 1,344 words Chapter 25 1,685 words Chapter 26 1,699 words Chapter 27 1,685 words Chapter 28 1,660 words Chapter 29 1,664 words Chapter 30 1,468 words Chapter 31 1,665 words Chapter 32 1,699 words Chapter 33 1,682 words Chapter 34 1,587 words Chapter 35 1,689 words Chapter 36 1,687 words Chapter 37 1,610 words Chapter 38 1,677 words Chapter 39 1,679 words Chapter 40 1,632 words Chapter 41 1,698 words Chapter 42 1,661 words Chapter 43 1,690 words Chapter 44 1,277 words Chapter 45 1,514 words Chapter 46 1,679 words Chapter 47 1,689 words Chapter 48 1,694 words Chapter 49 1,623 words Chapter 50 1,616 words Chapter 51 1,618 words Chapter 52 1,499 words Chapter 53 1,697 words Chapter 54 1,686 words Chapter 55 1,630 words Chapter 56 1,694 words Chapter 57 1,548 words Chapter 58 1,682 words Chapter 59 1,389 words Chapter 60 1,613 words Chapter 61 1,497 words Chapter 62 1,686 words Chapter 63 1,669 words Chapter 64 1,675 words Chapter 65 1,613 words Chapter 66 1,697 words Chapter 67 1,627 words Chapter 68 1,670 words Chapter 69 1,638 words Chapter 70 1,682 words Chapter 71 1,543 words Chapter 72 1,563 words Chapter 73 1,611 words Chapter 74 Reading now Chapter 75 1,616 words Chapter 76 1,629 words Chapter 77 1,662 words Chapter 78 1,575 words Chapter 79 1,507 words Chapter 80 1,608 words Chapter 81 1,674 words Chapter 82 1,651 words Chapter 83 1,516 words Chapter 84 1,631 words Chapter 85 1,699 words Chapter 86 1,652 words Chapter 87 1,633 words Chapter 88 1,651 words Chapter 89 1,674 words Chapter 90 1,606 words Chapter 91 1,688 words Chapter 92 1,593 words Chapter 93 1,654 words Chapter 94 1,396 words Chapter 95 1,655 words Chapter 96 1,599 words Chapter 97 1,693 words Chapter 98 1,665 words Chapter 99 1,653 words Chapter 100 1,658 words Chapter 101 1,700 words Chapter 102 1,639 words Chapter 103 1,651 words Chapter 104 1,671 words Chapter 105 1,547 words Chapter 106 1,695 words Chapter 107 1,585 words Chapter 108 1,675 words Chapter 109 1,641 words Chapter 110 1,674 words Chapter 111 1,509 words Chapter 112 1,615 words Chapter 113 1,674 words Chapter 114 1,691 words Chapter 115 1,694 words Chapter 116 1,688 words Chapter 117 1,681 words Chapter 118 1,656 words Chapter 119 1,670 words Chapter 120 1,698 words Chapter 121 1,689 words Chapter 122 1,691 words

Cike da takatsantsan ta sake tura ƙofar a hankali. Kamar yanda ta bar Mommahn yanzun ma tana kwance kan gadon kai ba za ka taɓa cewa akwai rai a tattare da ita ba. Amma saboda shegiyar zuciya irinta Maimuna ko kaɗan hakan be dameta ba, ita burinta ɗaya shi ne ta cika umarnin uwar ɗakinta. Ƙarasawa ta yi inda jinjirayen suke cikin zanin gado. Ta ƙarasa tana kallansu. Se ta yi maza ta ajje jaririn Mom a gefensu bayan ta gyara su ta haɗe su waje ɗaya, dan kuwa tun ɗazu da ta zo ta same su kowanne yana inda yake. Duk da yanda take sauri ta fice daga ɗakin, hakan be hanata ƙare musu kallo ba. Ɗaya idanunsa a rufe yake da alama ya yi kuka har ya gaji bacci ya ɗauke shi. Ya yin da ɗayan idanunsa biyu yana kukan da ba ya fita sosai. Dan ko sautinsa ba a iya ji sosai se ka matso kusa da shi. Ta jinjina kai lokacin da ta ga wani tsantar kyau a tattare da jariran, duk da ko a yanzun za ka fahimci babu kama ko kaɗan a tare da su amma kowanne Allah ya zuba kyau a tare da shi. Kuma ba za ka iya tantance wanda ya fi kyau ba, dan kuwa kowanne kyawunsa daban yake. Duk da a lokacin aka haife su hakan be hana komai fitowa ba tarr tarr ba, kamar misalin siririn dogon hanci, mitsitin baki da kuma manyan idanu. Ta kalli ɗan gidan Mom a fili ta furta

"Ikon Allah!!" Dan kuwa yaron ba dai hanci ba. Hancinsa irin na en gidansu Mom ne kamar an saka guduma an maida shi ciki. Duk da ko kaɗan be ɗauko kamar Mom ba amma a fizge yana kama da en gidansu Mom ɗin, har warɓeɓen bakin. (Astagfirullah)

Tuna kasassaɓar da take ƙoƙarin aikatawa ne ya sanyata juyawa ta kalli ƙofar ɗakin, kafin ta dawo da dubanta cikin ɗakin. Hannunta na wani irin karkarwa ta saka ta ɗauke su. Ta sanya su cikin hijab duk da yanda ƙafarta ta yi sanyi hakan be hanata ficewa daga ɗakin ba ƙirjinta na bugawa. Amma haka ta daure, ba tare da ta juya ba ta shige sashen Mom. Wata ƙatuwar ajiyar zuciya ta sauke lokacin da ta ganta cikin ɗakin Mom ɗin. Da sauri da sauri ta ƙarasa tana cigaba da sauke numfashi ta buɗe hijab ɗinta ta fito da su. Kawai miƙawa Mom da tun da ta shigo take kallanta ta yi ba tare da tace komai ba. Mom ta saka hannu ta karɓe su tana wata irin dariya saboda tsananin farin cikin da ta ji. Ta kalli yaran, irin kyawun da Allah ya basu kaɗai ya isa ya sa ta ji abin da ta aikata shi ne daidai. Kawai se ta rungumesu a ƙirjinta a fili tana furta

"Uwar biyu.." Ta ƙare tana murmushi.

"Kar ki yi haka Hajiya. Kar ki bar wata kafa da za ta kawo zargi a kan wannan haihuwar. Ki maida mata da yaro ɗaya, ko kuma ki san yanda za ki yi da shi. Amma dai kar ki riƙe su duka a matsayin kin haifi 'ya'ya biyu." Shiru Mom ta yi tanaa nazarin maganar Maimunan. Ta wani ɓangaren kamar ta faɗi gaskiya ne. Kar ta je hakan ya janyo zargi, ko kuma dai can wata matsalar daban. Ta sauke ajiyar zuciya tana juyawa ta kalli Maimuna

"Ya za a yi yanzu?" Shiru Maimuna ta yi tana tunanin abin da za tace. Kafin ta gama tunanin Mom ta sauko da jinjirayen tana kallansu. Ɗayan wanda yanzun ya yi shiru har kuma lokacin idanunsa a buɗe suke, se dai yana ta mutsu mutsu alamar ze iya cigaba da kukan da ya yi shiru yanzun shi Mom ta sake riƙewa. Ta kalli ɗayan da har lokacin yake bacci abinsa. Se ta miƙawa Maimuna shi tana faɗin

"Riƙe shi ki ga.." Babu musu ta saka hannu ta karɓe shi.

"Ki fitar da shi daga gidan nan. Duk inda za ki je ki je da shi. Yanzu ban san abin da zan ce a masa ba, zuwa anjima idan hankalina ya dawo jikina za ki ji kirana."

"Hakan mafita ce kuwa Hajiya?"

"Sosai kuwa.. Ke dai ɗauke shi kawai ki je." Se da ta sake sauke ajiyar zuciya sannan ta saka hannu ta ɗauke shi ta fice daga ɗakin duk da har lokacin tsoro ne fall a cikin ranta. Ba ta fita daga cikin gidan ba se da ta tabbatar babu wanda ya lura da jinjirin da ta ɓoye cikin hijab, kafin ta fice daga cikin gidan. Fitarta ke da wuya Baba Atine ta shigo cikin gidan, kai tsaye ɗakin Mommah ta wuce dan ta sanar da ita saƙon matar da ta aiketa wajenta. Se dai ta ji shiru cikin ɗakin. Hakan nan kawai ta ji hankalinta be kwanta ba, dan kuwa idan dai har sashen Mommahn a buɗe yake toh idanunta biyu, tana sallama za ta amsa ta fito, se kuma yau ta ji shiru Mommahn ba ta amsa ba, ga kuma ƙofar bedroom ɗin kusan a buɗe. Se ta ji tamkar ta shiga cikin ɗakin. Amma kuma hakan ba huruminta ba ne. Se kawai ta nemi waje ta zauna bayan ta sake yin sallama ba a amsa ba. Ta ɗauki wajen minti 10 zaune a palourn kafin daga bisani ta miƙe saboda yanda zuciyarta ta ƙi na'am da shirun Mommahn. A hankali ta tura ƙofar ɗakin ta shiga. Se kuwa ta hangi Mommahn kwance, ga wani abu da take hanga kamar jinjiri cikin jini. Da sauri ta ƙarasa tana kiran sunan Allah. Kamar yanda idanunta suka nuna mata haka ɗin ne kuwa. Tsoro ya kamata ganin daga jinjirin har Mommahn babu wanda ke da alamar rai a tattare da shi. Jikinta na wani irin rawa ta fice daga ɗakin, sam ta ma manta akwai wasu halittun cikin gidan bayan su, kawai ta faɗa wani gida dake kusa da su. Bayan wajen minti 2 se ga ta sun dawo tare da maƙociyar tasu. Babu ɓata lokaci driver ya ɗauki Mommahn da Baba Atine se asibiti. Tun a mota Baba Atine ta karɓi wayar drivern babu ɓata lokaci ta kira Daddy ta sanar da shi abin da ke faruwa. Cikin tashin hankali ya baro inda yake, ko neman wani be yi ba da kansa ya hau mota dan wucewa asibitin. A kan hanya ya kira wayar Mom. Se dai ita ɗin ma se take sanar da shi babu lafiya. Tsoro ya kama shi, kawai se ya chanja akalarsa zuwa gidan, tun da ko babu komai ita yanzu Mommah za ta samu kulawar likitoci. Ita kuma Mom ta shaida masa babu kowa cikin gidan. Hakan ne ya sa ya wuce can ɗin. Da kukan jariri ya soma cin karo, be san lokacin da murmushi ya ƙwace masa ba. Ya ƙarasa yana karɓarsa daga hannun Mom ɗin. Se kuwa ta koma ta kwanta tana sauke numfashi a wahalce. Duk da dai da gasken jikinta babu daɗi, amma tana sane take ƙarawa dan Daddyn ya tausaya mata.

"Sannu Yallaɓiya.." Daddy ya faɗa yana kallanta. Se ta jinjina kai kawai ba tare da tace komai ba. Daddy ya rungume jinjirin duk da jikinsa babu kaya kuma ba a gyara shi ba, yana jin wata irin ƙaunarsa na ratsa shi. Be ɓata lokaci ba ya taimakawa Mom ɗin ya sanyata cikin mota se asibiti.

.. Kai tsaye lokacin da su Baba Atine suka isa asibitin ɗaki na musamman aka wuce da Mommah. Cikin lokaci ƙanƙani aka shiga bata taimakon gaggawa. Ya yin da tun gwadawar farko da likita ta yi wa jaririn ta tabbatar babu rai a tare da shi. Babu daɗewa su Daddy suka isa asibitin. Ita ma Mom ɗin karɓarta aka yi daga ita har jaririn dan duba lafiyarsa shi ma.

... "Ya jikin wife ɗin tawa?" Daddy ya faɗa yana kallan Likitar.

"Alhamdulillah jikinta da sauƙi.. Kuma In Sha Allah nan ba da jimawa ba za ta warke ma gaba ɗaya. Abin ne ya zo mata a juye.. Ga shi haihuwar fari, ga shi kuma a gida babu kowa. Hakan ya taka muhimmiyar rawa. Gaskiya dai Yallaɓai ba zan ɓoye maka ba ta ji jiki.. Se dai muna mata fatan samun lafiya ingantacciya nan ba da jimawa ba." Likitar ta ƙare tana jinjina kai. Fesar da iska Daddy ya yi daga bakinsa kafin ya sauke ajiyar zuciya yace

"Allah Ya amince.. Zan iya ganinta?"

"Ehh babu damuwa Yallaɓai za ka iya ganinta.." ta ba shi amsa tana murmushi.

"Toh godiya nake.. Abin da ta haifa fa?" Daddy ya yi tambayar. Se ta ɗan yi shiru kamar ba za tace komai ba, se kuma ta ɗaga kai ta kalli Daddyn tace

"A yi haƙuri Alhaji.. Amma Allah ya yi masa rasuwa gaskiya tun da daɗewa kafin zuwansu asibiti."

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un..!" Shi ne abin da Daddy ya faɗa har cikin ransa yana jin babu daɗi. Ya ɗan zame hularsa yana shafa kansa a hankali. Duk da yanda ya so ganin ɗan Mommahn da rai da lafiya, yanzu kuma ake faɗa masa ya rasu, hakan be kai yanda ya ji tausayin Mommahn ya kama shi ba.

"Allah Ya sa me ceto ne." Likitar ta faɗa tana kallan Daddy lokacin da ya miƙe.

"Ameen." Ya amsa da hakan yana ficewa daga Office ɗin.

A hankali ya ƙarasa cikin ɗakin yana kallan Mommahn da ke kwance idanunta a rufe tana bacci, kai da ka ganta ka san babu ƙarya ta sha wahala. Dan kuwa hatta a baccin da take za ka iya ganin yanda idanunta suka yi ciki, baccin kuma da ka gani za ka fahimci kawai tana yinsa ne ba dan tana jin daɗinsa ba. Wani sabon tausayinta ya kama shi, ya ƙarasa ya nemi waje ya zauna yana cigaba da kallanta cike da tausayawa. Ya kai wajen minti 5 cikin ɗakin kafin ya tashi ya fita daga ɗakin. Se a lokacin da ya ga gawar yaron ma sannan ya sake tausayawa Mommah. Ya sumbaci goshin yaron a fili ya furta

"Allah Ya bata wani me albarka.. Ya kuma ba ta lafiya.. Kai kuma Allah Ya sa me ceto ne."

End of Chapter 74Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next