Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
By Billyn Abdul
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

Author: Billyn Abdul
Chapter 87 of 122
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.
Free access is active. You can keep reading and download during this access window.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters
Chapter 1 1,645 words Chapter 2 1,690 words Chapter 3 1,680 words Chapter 4 1,637 words Chapter 5 1,676 words Chapter 6 1,594 words Chapter 7 1,597 words Chapter 8 1,655 words Chapter 9 1,192 words Chapter 10 1,647 words Chapter 11 1,678 words Chapter 12 1,698 words Chapter 13 1,656 words Chapter 14 1,617 words Chapter 15 1,693 words Chapter 16 1,658 words Chapter 17 1,692 words Chapter 18 1,521 words Chapter 19 1,684 words Chapter 20 1,600 words Chapter 21 1,688 words Chapter 22 1,589 words Chapter 23 1,692 words Chapter 24 1,344 words Chapter 25 1,685 words Chapter 26 1,699 words Chapter 27 1,685 words Chapter 28 1,660 words Chapter 29 1,664 words Chapter 30 1,468 words Chapter 31 1,665 words Chapter 32 1,699 words Chapter 33 1,682 words Chapter 34 1,587 words Chapter 35 1,689 words Chapter 36 1,687 words Chapter 37 1,610 words Chapter 38 1,677 words Chapter 39 1,679 words Chapter 40 1,632 words Chapter 41 1,698 words Chapter 42 1,661 words Chapter 43 1,690 words Chapter 44 1,277 words Chapter 45 1,514 words Chapter 46 1,679 words Chapter 47 1,689 words Chapter 48 1,694 words Chapter 49 1,623 words Chapter 50 1,616 words Chapter 51 1,618 words Chapter 52 1,499 words Chapter 53 1,697 words Chapter 54 1,686 words Chapter 55 1,630 words Chapter 56 1,694 words Chapter 57 1,548 words Chapter 58 1,682 words Chapter 59 1,389 words Chapter 60 1,613 words Chapter 61 1,497 words Chapter 62 1,686 words Chapter 63 1,669 words Chapter 64 1,675 words Chapter 65 1,613 words Chapter 66 1,697 words Chapter 67 1,627 words Chapter 68 1,670 words Chapter 69 1,638 words Chapter 70 1,682 words Chapter 71 1,543 words Chapter 72 1,563 words Chapter 73 1,611 words Chapter 74 1,680 words Chapter 75 1,616 words Chapter 76 1,629 words Chapter 77 1,662 words Chapter 78 1,575 words Chapter 79 1,507 words Chapter 80 1,608 words Chapter 81 1,674 words Chapter 82 1,651 words Chapter 83 1,516 words Chapter 84 1,631 words Chapter 85 1,699 words Chapter 86 1,652 words Chapter 87 Reading now Chapter 88 1,651 words Chapter 89 1,674 words Chapter 90 1,606 words Chapter 91 1,688 words Chapter 92 1,593 words Chapter 93 1,654 words Chapter 94 1,396 words Chapter 95 1,655 words Chapter 96 1,599 words Chapter 97 1,693 words Chapter 98 1,665 words Chapter 99 1,653 words Chapter 100 1,658 words Chapter 101 1,700 words Chapter 102 1,639 words Chapter 103 1,651 words Chapter 104 1,671 words Chapter 105 1,547 words Chapter 106 1,695 words Chapter 107 1,585 words Chapter 108 1,675 words Chapter 109 1,641 words Chapter 110 1,674 words Chapter 111 1,509 words Chapter 112 1,615 words Chapter 113 1,674 words Chapter 114 1,691 words Chapter 115 1,694 words Chapter 116 1,688 words Chapter 117 1,681 words Chapter 118 1,656 words Chapter 119 1,670 words Chapter 120 1,698 words Chapter 121 1,689 words Chapter 122 1,691 words

"Ba kya buƙatar komai?" Ɗan jim ta yi kafin ta jinjina kai tana ji kamar ta yi ficewarta. Se ta kasa yin hakan, kawai ta cigaba da zama. Idan ta tuhumi kanta dalilinta na yin hakan, se ta kawo uzurin yau ɗin Gwanin abun tausayi ne sosai, shi ya sa ta zauna saboda kuma yace mata ta zauna. Sosai kuma hakan ya taimaka masa, dan babu ƙarya Lulun ta zame masa sanyin idaniya, musamman a yau ɗin da ya sake gasgata hakan. Abu ɗaya ne ya rage, shi ne sauyawar halin Lulun gaba ɗaya, duk da cikin ikon Allah a hankali a hankali take chanjawa, dan yanzu an samu kaso me yawa ya ragu daga cikin halayenta.

A ɗaya ɓangaren kuwa da sallama ta shiga ɗakin ɗauke a bakinta. A Zuciyarta tana fatan Allah ya sa ya yi bacci, ko kuma dai ma kar ta same shi cikin ɗakin gaba ɗaya. Se dai addu'arta ba ta karɓu ba, dan kuwa samunsa ta yi kishingiɗe a kan gadon, ya ɗora kansa a kan hannunsa idanunsa a lumshe kamar me bacci. Se dai ba baccin yake ba, tunanin abubuwan da suka dinga faruwa kamar a mafarki ɗazun yake yi. Ya kasa dena tunanin, duk kuwa da abin da ya sha ɗazun amma har yanzu be manta abin da ya faru ba. Sallamar da ta sake yi ne ya sanya shi buɗe idanunsa da suka fi kama da na wanda ya tashi daga bacci. A hankali ta cigaba da takawa zuwa cikin ɗakin, kai tsaye ta ƙarasa inda ta saba ajewa ta ajiye sannan ta juyo. Kamar ta fice daga ɗakin ba tare da tace masa komai ba, se kuma ta ga rashin dacewar hakan, dan haka cikin siririyar muryarta tace

"Barka da wannan lokaci.." Se a lokacin sannan ya miƙe zaune. Maimakon ya ji kamar a da yana son shareta ko kuma sake mata gargaɗin kar ta sake shigo masa ɗaki, se ya ji yau ɗin ba haka ba ne. Ta wani ɓangaren ma kamar jin daɗin zuwanta ya yi. Ya ɗan sauke numfashi a gajiye sannan yace

"Barka." Ko a iya sautin muyarsa ya isa a fahimci yanayin da yake ciki a halin yanzu. Dan ita kanta Didi se da ta ɗaga kai ta kalle shi saboda yanda ta ji muryarsa ta sauya. Abin da dai ba ta sani shi ne, ko baccin da ya yi ne ya sanya muryarsa sauyawa ko kuma har yanzu a kan al'amarin da ya faru ɗazu ne?.

"Duk da dai ka ce na dena shiga harkarka amma da ka ɗauki Qur'an ka karanta.." Be san dalilin da ya sa yanzu idan ta yi makamanciyar maganar nan yake jin haushin hakan ba. Ya ɗan ja ƙaramin tsaki yana miƙewa tsaye a hankali. Ba ta yi tunanin ma ze tanka mata ba, se jin cunkushashshiyar muryarsa ta yi yace

"Kamar na ce ki bar min wannan maganar koh?" Ya yi maganar yana kafeta da idanunsa. Se ta yi saurin kauda kai tana ɓata fuska. Ƙasa-ƙasa ta furta

"Ai dai gwara na kama kaina.. kafin ka shuka min rashin kirkinka.." Sarai ya ji abin da ta faɗa, dan tun da ta fara maganar yake kallan bakinta dan fahimtar abin da ta faɗa. Ya ja ƙwafa yana cigaba da kallanta, ba tare da ya bari ta ankara ba ya ɗan soma rage tazarar da ke tsakaninsu. Ita dai tun da ta kawo abincin ta kuma gaida shi babu abin da ya rage mata. Dan haka ta ɗaga ƙafa da niyyar takawa dan ficewa daga ɗakin, ba tare da ta lura ba se jin hannunsa ta yi a kan hannunta, kafin ta yi ƙoƙarin yin komai ya jata gaba ɗaya zuwa jikinsa.

"Me kika ce?" Ya faɗa yana kafeta da lumsassun idanunsa. Ba ta san lokacin da jikinta ya kama rawa ba, musamman yanda ba ta yi tsammani ba. Se ta rasa ma abin da za ta ce. Ita burinta ɗaya ya ɗauke waɗannan idanun nasa daga kanta, idanun da suke sakawa ta ji tsoronsa ya kamata.

"Me kika ce..?" Ya faɗa yana riƙe hannunta sosai.

"Ni ba abin da na ce.."

"Kin faɗa.." Ya katseta da faɗin hakan yana sake janta cikin jikinsa. Da sauri ta girgiza kai tuna abin da ya faru rannan. Tsoron kar a sake maimaita abin da ya faru ya sanyata faɗin

"Allah ba da kai nake ba.. Don Allah ka yi haƙuri." Har ga Allah ta ba shi dariya, amma be yi ba ya maaze, ya sake tamke fuska. Yanayin yanda tsoro ya bayyana a kan fuskarta ba ƙaramin kyau ta yi ba. Se ya ji tamkar kar ya saketa, su cigaba da kasancewa a haka.

"Ashe mara kunyar ƙarya ce.." Ya faɗa yana sakinta, dan yau ɗin kusan duk hankalinsa na kan abin da ya faru ne ɗazun. Ba ta jira ta sake cewa komai ba, ko ya ce wani abu ba ta fice daga ɗakin kamar za ta yi tuntuɓe. Sam ba ma ta lura da waye a palour ba, Lulu ta koma ko ba ta koma ba duk ba ta lura ba. Ita dai burinta kawai ta ganta a sashen Mommah.

Komawa ya yi ya zauna a kan gadon, ya lumshe idanunsa tunani barkatai na zuwa masa cikin ƙwaƙwalwa. Se dai waɗanda suka fi tasiri su ne tambayar da ke ta masa yawo cikin kwanya.
"Shin me ke damunsa ne? Me ye ya sa yanzu yake kasa controlling kansa ne idan yarinyar na gabansa? Duk me ye hakan?" Ya tambayi kansa hannunsa cikin kwantacciyar sumar kansa.

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO71*

___Ba ta daɗe da shiga ɗakin ba Lulu ta shigo ɗakin ita ma. Ta bi Didi da kallo tana mamakin yanda ta ganta.

"Ya na ganki kamar a zabure?"

"A zabure kuma?" Didi ta faɗa tana harararta. Se ta yi dariya tana faɗin

"Ehh yasin. Kamar wadda ta wa sarki ƙarya." Dariya ita ma Didin ta yi. Ta saka hannu ta janyo hannun Lulu tace

"Wai ni kam ki na kallan kanki a mudubi kuwa Lulu?"

"Na shiga 3 me na yi?" Lulu ta faɗa tana waro ido waje.

"Dillah kyau kika yi fa.. Kin ga har da ƙiba ma fa duk kin yi wallahi, kamar ba ke ba. Ke idan Ammi ta ganki ma ba za ta gane ki ba." Dariya Lulu ta yi jin ta ƙare zancen nata da barkwanci ya sa ta fahimci da wasa take. Tace

"Didina."

"Lulun Gwani." Buɗe baki Lulu ta yi tana kallan Didin. Se ta fuzge hannunta tana faɗin

"Allah ba na son kalar haka Didi.. Ni ba na so."

"Iyee.." Didi ta faɗa tana kallanta. Ita dai ba ta ga alamar har yanzu Lulun na cigaba da takun saƙa da Gwani ba, ba kuma ta ga alamun tsanar nan tasa da ta yi ba. Se dai abin da ba ta sani ba yanzun ta fara son shi ne ko kuwa a'ah? Se dai ba ta so ta gwada tambayarta kuma ta zo ta ɓaro wani aikin. Shi ya sa ta yi maganar nan ko za ta fahimci wani abun. Ba ta ankara ba se ganin Lulun ta yi ta fice daga ɗakin. Ta bita da kallo tana murmushi.

"A dai juri zuwa rafi.." Daga haka ita ma ta miƙe ta fice daga ɗakin zuwa palour. A nan suka sami Mommah, suka sake gaisawa. Ta kalli Baba Atine da shigowarta kenan tace

"Kin gama komai?"

"Ehh Hajiya.." Maida dubanta kansu Mommah ta yi tace

"Ya kamata ku je ku huta haka nan.. Ta kai muku abinci ku tabbatar kun ci sannan ku kwanta se da safe." A tare suka miƙe, Baba Atine ma ta miƙe dan musu rakiya zuwa ɗakin duk da a cikin palourn Mommahn yake.

"Se da safe Mommah.." Didi ta faɗa.

"Se da safe." Ita ma Lulu ta faɗa a hankali saboda rashin sabo a tsakaninta da Mommahn.

"Allah Ya tashe mu lafiya Yarana.." Ta yi maganar tana murmushi. Kai tsaye bin bayan Baba Atinen suka yi zuwa cikin ɗakin, ya yin da Mommah kuma ta miƙe ta faɗa ɗakinta.

.. Washegari da safe, fitowar Mommah daga cikin ɗakinta kenan suka yi sallama cikin ɗakin. Ta amsa sallamar tana kallan en biyunta da ta kwana tana musu addu'a a kan Allah Ya kare mata su. Se ta ƙaraso cikin ɗakin daidai lokacin da su ma suka ƙaraso. Dukkansu zamewa suka yi suka zauna a ƙasa. Mommah ta yi murmushi daidai lokacin da take amsa barka da safiyar da suka mata.

"Kun tashi lafiya?" Ta tambaya cikin kulawa.

"Alhamdulillah.." Gwani ya amsa da hakan, ya yin da Bad Man ya amsa da

"Ehh Mommah."

"Bari na ɗan amsa waya." Bad Ya faɗa yana miƙewa. Se duk suka bi shi da kallo, Gwani har yanzu ganin abin yake kamar a mafarki. Se kawai ya jinjina kai yana sake kaɗaita Allah a cikin zuciyarsa. Maganar Mommah ita ce ta katse masa tunani lokacin da take faɗin

"Don Allah ka din ga saka min ido sosai a kan Areef.. Ban san waye babba cikinku ba, amma haka nan zuciyata ke ba ni kai ne babba.. Dan haka ga ɗan uwanka nan ina fata za ka taya ni kula da tarbiyyarsa, duk wani abu da za ka gani be dace ba a wajensa ka yi ƙoƙarin hana shi ko tunasar da shi. Kai ne za ku din ga kasancewa tare shi ya sa nake faɗa maka haka." Jinjina kai Gwani ya yi kafin yace

"In Sha Allah Mommah.."

"Ku wuce sashen Daddy.. Za mu taho yanzun." Da "toh" ya amsa yana miƙewa ya fice daga ɗakin. Ta bi shi da kallo wannan farin cikin da ya kasa barinta na cigaba da ratsata. Kafin ta fita se da ta sake tura Baba Atine ta duba mata su Lulu. Nan take shaida mata bacci suke yi, se ta umarceta da ta ƙyale su kawai. Ita kuma ta wuce zuwa sashen Daddyn.

End of Chapter 87Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next