Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
By Billyn Abdul
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

Author: Billyn Abdul
Chapter 77 of 122
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.
Free access is active. You can keep reading and download during this access window.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters
Chapter 1 1,645 words Chapter 2 1,690 words Chapter 3 1,680 words Chapter 4 1,637 words Chapter 5 1,676 words Chapter 6 1,594 words Chapter 7 1,597 words Chapter 8 1,655 words Chapter 9 1,192 words Chapter 10 1,647 words Chapter 11 1,678 words Chapter 12 1,698 words Chapter 13 1,656 words Chapter 14 1,617 words Chapter 15 1,693 words Chapter 16 1,658 words Chapter 17 1,692 words Chapter 18 1,521 words Chapter 19 1,684 words Chapter 20 1,600 words Chapter 21 1,688 words Chapter 22 1,589 words Chapter 23 1,692 words Chapter 24 1,344 words Chapter 25 1,685 words Chapter 26 1,699 words Chapter 27 1,685 words Chapter 28 1,660 words Chapter 29 1,664 words Chapter 30 1,468 words Chapter 31 1,665 words Chapter 32 1,699 words Chapter 33 1,682 words Chapter 34 1,587 words Chapter 35 1,689 words Chapter 36 1,687 words Chapter 37 1,610 words Chapter 38 1,677 words Chapter 39 1,679 words Chapter 40 1,632 words Chapter 41 1,698 words Chapter 42 1,661 words Chapter 43 1,690 words Chapter 44 1,277 words Chapter 45 1,514 words Chapter 46 1,679 words Chapter 47 1,689 words Chapter 48 1,694 words Chapter 49 1,623 words Chapter 50 1,616 words Chapter 51 1,618 words Chapter 52 1,499 words Chapter 53 1,697 words Chapter 54 1,686 words Chapter 55 1,630 words Chapter 56 1,694 words Chapter 57 1,548 words Chapter 58 1,682 words Chapter 59 1,389 words Chapter 60 1,613 words Chapter 61 1,497 words Chapter 62 1,686 words Chapter 63 1,669 words Chapter 64 1,675 words Chapter 65 1,613 words Chapter 66 1,697 words Chapter 67 1,627 words Chapter 68 1,670 words Chapter 69 1,638 words Chapter 70 1,682 words Chapter 71 1,543 words Chapter 72 1,563 words Chapter 73 1,611 words Chapter 74 1,680 words Chapter 75 1,616 words Chapter 76 1,629 words Chapter 77 Reading now Chapter 78 1,575 words Chapter 79 1,507 words Chapter 80 1,608 words Chapter 81 1,674 words Chapter 82 1,651 words Chapter 83 1,516 words Chapter 84 1,631 words Chapter 85 1,699 words Chapter 86 1,652 words Chapter 87 1,633 words Chapter 88 1,651 words Chapter 89 1,674 words Chapter 90 1,606 words Chapter 91 1,688 words Chapter 92 1,593 words Chapter 93 1,654 words Chapter 94 1,396 words Chapter 95 1,655 words Chapter 96 1,599 words Chapter 97 1,693 words Chapter 98 1,665 words Chapter 99 1,653 words Chapter 100 1,658 words Chapter 101 1,700 words Chapter 102 1,639 words Chapter 103 1,651 words Chapter 104 1,671 words Chapter 105 1,547 words Chapter 106 1,695 words Chapter 107 1,585 words Chapter 108 1,675 words Chapter 109 1,641 words Chapter 110 1,674 words Chapter 111 1,509 words Chapter 112 1,615 words Chapter 113 1,674 words Chapter 114 1,691 words Chapter 115 1,694 words Chapter 116 1,688 words Chapter 117 1,681 words Chapter 118 1,656 words Chapter 119 1,670 words Chapter 120 1,698 words Chapter 121 1,689 words Chapter 122 1,691 words

"Da ma a kan maganar Areef ne na zo in ji ko ka yanke shawarar barinsa ya fita ƙasar wajen. Ka ga dai haka na so ya fita tun a secondary amma ba ka amince ba. Toh a wannan karon ina roƙonka da Allah da ka amince ya fita.." Ajiyar zuciya Daddy ya sauke, shi kam sam ya rasa dalilin Mom ɗin na dagewa a kan fitar Areef ɗin waje karatu. Ko da yake ya san hakan na da nasaba da ganin da take 'ya'yan abokansa duk a wajen suke karatu.

"Shi kenan.. Amma ki sani duk wani tsari da na fito da shi za ki bi shi matuƙar ki na so na yadda Areef ya bar ƙasar nan."

"Babu damuwa.. Na amince ma." Ta faɗa tana murmushi cike da farin ciki da jin daɗi. Abu na farko da ya fara faɗo mata shi ne nisa da Areef ɗin ze yi da Mommah, ta san tabbas ze mantata kafin ya dawo. Abu na biyu kuma da ma burinta kenan kar ya yi karatu a ƙasar nan dan tana ganin a matsayinsa na ɗan gidan hamshaƙin me kuɗi kamar Alhaji Matawalle be dace a ce ya yi karatu a ƙasar nan ba. Haka dai bayan gama shirye shirye aka tura Areef U.S bayan dogon gargaɗin da Daddy ya gindaya masa. Be kuma bar shi ya tafi ba se da ya haɗa shi da waɗanda za su din ga kula da shi. A lokacin Mommah ji ta yi ina ma tana da ƙarfin faɗa a jin da za ta iya hana Areef tafiya ƙasar waje. Sanin da ta yi ba ta da shi ne ya sanyata kama bakinta. Ta bi shi da addu'a lokacin da ze tafi ɗin.

Duk da yanda Daddy ya tsaya tsayin daka wajen tarbiyyar Areef ɗin duk da ba ya ƙasar nan, amma hakan be yi wa Mom ba, ita se take gani ma kamar wannan ɗin ai takura ce. A bar yaro mana ya wataya ko dan kasancewarsa ɗan me kuɗi mana. Amma kullum yana tare da masu ba shi kariya da tsaro ai wannan ma takura ce da rashin yadda da shi. Shi kam Daddy ko a jikinsa, idan ma tana irin waɗannan maganganun ko kallanta ba ya yi. Dan kuwa be taɓa yadda da abin da take faɗa ba. Abin da ya sani kawai shi ne tun da Areef ɗin ya bar gabansu ya bar gabansu kenan, babu wani me kwaɓarsa a can ɗin. Dan haka tura masa masu kula da shi shi ne kaɗai mafita. Duk da ya san Allah ne kaɗai me karewa, amma ko babu komai hakan ze taimaka ainun.

_CIGABAN LABARI_

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO66*

___ Shiru ɗakin ya ɗauka na fiye da tsawon minti 5, babu wanda yace komai tun bayan da Maimuna ta gama faɗar abin da suka aikata ita da Mom. Bad Man dake zaune a gefen side chair yanzun haka yana zaune ne a kanta gaba ɗaya, hannunsa na kan goshinsa idanunsa a lumshe, ba za ka iya fahimtar yanayin da yake ciki ba. Se dai za ka iya ganin yanda jijiyoyin kansa suka tashi, suka fito raɗa raɗa har a kan goshinsa. Zuciyarsa babu abin da take yi se wani irin harbawa da ya wuce na misali. Ya ma rasa abin da ya kamata ya yi. Tunanin me ze yi? Me ya kamata yace? Me ya kamata ya aikata? Gaba ɗaya kansa ya kulle, ƙwaƙwalwarsa ta toshe, ta yadda ya kasa ko da yunƙurin yin wani tunanin ne. Daddy kam hular da ke kansa ɗazun yanzun tana gefensa, kansa yana kallan ƙasa lokaci zuwa lokaci yana bubbuga ƙafarsa a ƙasa, se dai shi ma har zuwa shuɗewar waɗannan mintunan be ce komai ba. Ammi da Talatuwa da basu san da zaman labarin ba su kansu sun jijjiga bayan da suka ji abin da Maimunan da Mom suka aikata. Kuka kawai Talatuwa ta fashe da shi, dan ba ta taɓa tunanin rashin imanin Maimunan ya kai har ta yadda a haɗa baki da ita su aikata wannan mummunan aikin ba. Mom da tun ɗazu take yunƙurin magana Daddy na hanata, a karo na barkatai ta sake buɗe baki jikinta na wani mugun karkarwa, ba ma ta taɓa tunanin idan ta buɗe baki za ta iya magana ba. Se dai cikin ƙarfin hali ta buɗe bakin da ƙyar ta soma faɗin

"Wallahi ƙarya take yi, ƙarya take yi. Sharrin Sa'adatu ne kawai. Duk yadda aka yi nauyinta ta ɗauka dan ta zo ta ƙala min wannan sharrin. Da ma tun da na sallameta a aiki na lura ta ƙullace ni ashe abin da suka shirya kenan. Kar ka yadda da ita, kar ka yadda da ita.. ƙarya take min.." Ta ƙare muryarta na karkarwa. Se a lokacin sannan Daddy ya ɗaga idanunsa da shi kansa suka sauya kala ya sauke su a kan Mom, wata irin tsanarta na zuwa ta mamaye zuciyarsa. Haushi, takaici da kuma tsananin mamaki sun ƙi barinsa. A karo na farko tun bayan gama bayar da labarin da Maimuna ta yi yace

"Kin gama?" Ya faɗa muryarsa a wani irin kaurare. Se ta yi maza ta jijjjiga kai a tunaninta ko ya yadda da abin da ta faɗa ne, tace

"Ehh wallahi ƙarya take min.." Ta sake wallacewa ba tare da damuwa ba, a cewaeta ai ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba. Se da Maimuna ta goge hawayen da ya ƙi tsayawa a kan fuskarta saboda danasani da nadama sannan tace

"Ina me rantsewa da girman Allah abin da na faɗa gaskiya ne. Ban ƙara ba kuma ban rage ba. Idan dai har ƙarya na yi mata Allah ya wulaƙanta ni tun kafin na bar gidan nan.. Za kuma ku iya zuwa ku yi gwaji dan tabbatar da abin da na faɗa.." Se a lokacin Mommah da tun da aka fara maganar ba ta iya ko da ƙwaƙwƙwaran motsi ba ne. Illah kafe Maimuna da ta yi da ido tana jin abin da take faɗa ɗin kamar almara. Lokacin da ta kai ƙarshe kuwa tuni jikinta ya ɗauki rawa, har ta numfashinta se da ya soma yi mata barazanar ɗaukewa, dalili kenan da ya saka bugun zuciyarta ya ƙaru, ta shiga fuzgo shi da ƙyar idanunta a lumshe. Har lokacin babu abin da kunnuwanta ke jiye mata se maganar Maimunan. Kamar wadda kunnanta ya yi recording haka take ji. Cikin lokaci ƙanƙani ta ji wani jiri na ɗibarta duk da kasancewarta a zaune. Ba tare da ta shirya ba kuwa ta yi maza ta riƙe kanta da ya mugun sara mata, a take a gun kuma ta zube kan kujerar sumammiya.

"Sa'adah.." Daddy da ke lura da ita ya faɗa yana miƙewa da sauri. A karo na farko ya buɗe idanunsa da ƙyar kuma da sauri, sun yi wani irin ja kamar gauta. I zuwa lokacin ban da zafi babu abin da numfashinsa ke fitarwa. Be san lokacin da ya miƙe ba kai tsaye ya wuce kujerar da Mommah ke kai.

"Areef ɗorata kan waccan kujerar.." Daddy ya faɗa duk da yanda yake jin wani tsoro na kama shi. Se dai ta gefe ɗaya ya san dole ne Mommah ta shiga irin wannan yanayi, jin abin da ba ta taɓa tsammani ba. Shi kansa ya rasa a wanne yanayi ze saka wannan al'amari, ballantana kuma ita da ta haifa. Babu musu Bad Man ya saka hannunsa ya ɗauki Mommahn ya soma takawa dan kwantar da ita kan wata kujera da ke cikin palourn wadda ta yi shigen kama da gado, se dai ita ma irin yadin kujerun gareta.

"Ka sauketa Areef.. Ka da ka yadda da abin da suke faɗa.. Sharri ne.." Mom ta yi ƙarfin halin faɗin hakan, dan kuwa a lokacin ita kaɗai ta san tsoron da take ji. Kawai dai tana yin magana ne dan kar zargin ya yi yawa. Wani kallo da ya watsa mata da gigitattun idanunsa shi ne ya sanyata saurin sauke kanta ƙasa hantar cikinta na kaɗawa. Kaddai har ya amince da abin da aka faɗa? Yau kam ta shiga uku idan haka ɗin ne.

Kai tsaye kwantar da ita ya yi a nutse. Be jira Daddy ya ce komai ba ya ɗauko ruwa da kansa ya ƙaraso ya shiga shafawa Mommahn a fuskarta. Cikin ƙanƙanin lokaci ta ja wani gauron numfashi kafin ta sauke ajiyar zuciya, se ta shiga buɗe idanunta kamar me neman wani abu. Ba ta jira komai ba ta miƙe zaune da kanta a kan kujerar. Hawaye ne suka shiga zubowa a kan fuskar Mommahn, ranta babu daɗi sam, ta rasa me ya kamata ta yi. Cikin kulawa Daddy ya kamo hannunta idanunsa a kan fuskarta yace

"Ki na lafiya?" Jinjina kai ta yi daidai lokacin da wasu hawayen suka zubo a kan kuncinta. Da ƙyar ta buɗe baki tace

"Da gaske en biyu na haifa? Da gaske Areef ɗana ne? Da gaske ne Yallaɓai?" Mommah ta yi maganar gwanin ban tausayi. Rufe idanunsa Daddy ya yi yana jin wani mugun tausayin Mommahn na ratsa shi. Kaff cikin ɗakin cike da tausayawa suke kallan Mommah, idan ka cire Mom da Aunt Makiyy da suke tsoron kar asirinsu ya tonu. Juyawa Daddy ya yi ya kalli Mom da har lokacin su take kalla, ban da gumi babu abin da ke tsatstsafowa daga jikinta.

"Za ki buɗe baki ki faɗi gaskiya ko kuma se na yi miki abin da har ki mutu ba za ki manta da shi ba?" Ya yi maganar a kaurare yana kafeta da idanunsa. Shiru Mom ta yi a ranta tana ji kamar ta buɗe baki ta sake maimaita ƙarya Maimunan take yi. Se dai gefe guda kuma tana tsoro kar ya gano ƙarya take ya yi mata abin da yake iqrari, dan ta san tabbas ba ze wuce saki yake nufi ba. Kai amma duk da haka ba za ta bari asirinta ya tonu ba, dan haka ta buɗe baki da niyyar sake ƙaryata Maimuna a karo na barkatai se jin muryar Aunt Makiyy dake gefenta ta yi tace

End of Chapter 77Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next