Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
By Billyn Abdul
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

Author: Billyn Abdul
Chapter 99 of 122
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.
Free access is active. You can keep reading and download during this access window.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters
Chapter 1 1,645 words Chapter 2 1,690 words Chapter 3 1,680 words Chapter 4 1,637 words Chapter 5 1,676 words Chapter 6 1,594 words Chapter 7 1,597 words Chapter 8 1,655 words Chapter 9 1,192 words Chapter 10 1,647 words Chapter 11 1,678 words Chapter 12 1,698 words Chapter 13 1,656 words Chapter 14 1,617 words Chapter 15 1,693 words Chapter 16 1,658 words Chapter 17 1,692 words Chapter 18 1,521 words Chapter 19 1,684 words Chapter 20 1,600 words Chapter 21 1,688 words Chapter 22 1,589 words Chapter 23 1,692 words Chapter 24 1,344 words Chapter 25 1,685 words Chapter 26 1,699 words Chapter 27 1,685 words Chapter 28 1,660 words Chapter 29 1,664 words Chapter 30 1,468 words Chapter 31 1,665 words Chapter 32 1,699 words Chapter 33 1,682 words Chapter 34 1,587 words Chapter 35 1,689 words Chapter 36 1,687 words Chapter 37 1,610 words Chapter 38 1,677 words Chapter 39 1,679 words Chapter 40 1,632 words Chapter 41 1,698 words Chapter 42 1,661 words Chapter 43 1,690 words Chapter 44 1,277 words Chapter 45 1,514 words Chapter 46 1,679 words Chapter 47 1,689 words Chapter 48 1,694 words Chapter 49 1,623 words Chapter 50 1,616 words Chapter 51 1,618 words Chapter 52 1,499 words Chapter 53 1,697 words Chapter 54 1,686 words Chapter 55 1,630 words Chapter 56 1,694 words Chapter 57 1,548 words Chapter 58 1,682 words Chapter 59 1,389 words Chapter 60 1,613 words Chapter 61 1,497 words Chapter 62 1,686 words Chapter 63 1,669 words Chapter 64 1,675 words Chapter 65 1,613 words Chapter 66 1,697 words Chapter 67 1,627 words Chapter 68 1,670 words Chapter 69 1,638 words Chapter 70 1,682 words Chapter 71 1,543 words Chapter 72 1,563 words Chapter 73 1,611 words Chapter 74 1,680 words Chapter 75 1,616 words Chapter 76 1,629 words Chapter 77 1,662 words Chapter 78 1,575 words Chapter 79 1,507 words Chapter 80 1,608 words Chapter 81 1,674 words Chapter 82 1,651 words Chapter 83 1,516 words Chapter 84 1,631 words Chapter 85 1,699 words Chapter 86 1,652 words Chapter 87 1,633 words Chapter 88 1,651 words Chapter 89 1,674 words Chapter 90 1,606 words Chapter 91 1,688 words Chapter 92 1,593 words Chapter 93 1,654 words Chapter 94 1,396 words Chapter 95 1,655 words Chapter 96 1,599 words Chapter 97 1,693 words Chapter 98 1,665 words Chapter 99 Reading now Chapter 100 1,658 words Chapter 101 1,700 words Chapter 102 1,639 words Chapter 103 1,651 words Chapter 104 1,671 words Chapter 105 1,547 words Chapter 106 1,695 words Chapter 107 1,585 words Chapter 108 1,675 words Chapter 109 1,641 words Chapter 110 1,674 words Chapter 111 1,509 words Chapter 112 1,615 words Chapter 113 1,674 words Chapter 114 1,691 words Chapter 115 1,694 words Chapter 116 1,688 words Chapter 117 1,681 words Chapter 118 1,656 words Chapter 119 1,670 words Chapter 120 1,698 words Chapter 121 1,689 words Chapter 122 1,691 words

"Hala ba ki ji abin da Mommah ta faɗa ba?.." Ƙwanƙwasa ƙofar da aka yi shi ne ya dakatar da ita daga maganar da ta soma. Baba Atine ta shigo ta sanar da su saƙon Mommah a kan su fito za a yi dinner. Amsawa suka yi da "toh" Didi ba ta sake cewa komai ba ta miƙe cike da fatan Lulun ta ƙyaleta. Se kuwa ba tace mata komai ba, se ɗaukar mayafin abayar jikinsu da suka yi suka yafa sannan suka fice daga ɗakin. Daidai lokacin da suka fito daga ɗakin ya yi daidai da lokacin da Gwani da Bad Man suka shigo cikin ɗakin. Haka kuma ya yi daidai da lokacin da Iftihal ta fito daga cikin ɗakin da yanzu ita kaɗai ce a ciki, saboda en uwanta da suka tafi saura ita ɗaya da za ta koma ranar da su Mommah za su je gidan. Cikin jin daɗin ganinsu ta tafi da sauri cikin iyayi tace

"Sannunku da zuwa en uwa." Ta faɗa tana murmushi.

"Yawwah." Suka amsa kusan a tare.

"Mu je koh?" Ta faɗa kamar ita ce me gidan. Suna fara takawa ta yi yanda ta yi ta jera da Gwani. Kallan juna Lulu da Didi suka yi kafin suka maida dubansu gaba ba tare da sun ce komai ba. Se suka cigaba da takawa daidai lokacin da Iftihal ta ja kujerar kusa da wadda ta ga Gwani ya riƙe da alama a ita ze zauna. Se dai shi ba abin da yake nufi kenan ba, ya janyota ne dan Lulu ta zauna, se dai kuma har yanzu yana jin kunyar Mommah, wasu abubuwan dole ya dinga haƙura har su bar gabanta. Kafin ma ya gama tunanin da yake ya lura da Iftihal da ke ƙoƙarin zama a kusa da kujerar da ya riƙe ɗin. Kawai se ya zauna a kan kujerar yana ɗaga kansa ya kalli su Lulu da suka kusa ƙarasowa. Daidai lokacin da ya kalleta ya yi daidai da lokacin da ita ma ta kalle shi, ya sakar mata murmushi yana lumshe idanunsa cikin nata. Janye idanunta ta yi tana ɗan rufe idanunta kafin ta buɗe suka cigaba da tafiya. Tun tahowarsu ya kafeta da idanun nan nasa. Tun daga nesa ta tabbatar da lallai yana cikin ɗakin kuma kallanta yake yi. Dan kuwa idanunsa na da matuƙar tasirin da in dai ze kalleta se ta ji hakan, duk kuma se ya saka ta rasa sukuni. Sake gaisar da Mommah Gwani da Bad Man suka yi, ta amsa cikin kulawa. Ita da kanta ta shiga serving na kowa.

"Mommah kawo na.." Tun kafin Didi ta ƙarasa Mommah ta katseta da faɗin

"Yi zamanki Daughter.. babu damuwa." Se ta koma ta zauna. Se da Mommah ta gama da kowa sannan ta koma ta zauna. Se a lokacin sannan kowa ya ja abincin ya fara ci. Se dai ban da Bad Man, da ko kallan abincin be yi ba, se zubawa Didi ido da ya yi. Abin da Mommah ta faɗa ɗazu kawai shi yake tunawa. Maganganun da suka hana shi sukuni kenan, har ya kasa nutsuwa. Yanzu ma kiran nan ma Mommah yq ɗauka wani abun ne, se da suka zo sannan ya ji hankalinsa ya kwanta, da ya fahimci maganar ba a kan Didi ba ce. Gyara zama ya yi yana ɗora hannayensa a kan dinning ɗin kafin ya ɗora tafin hannunsa a haɓarsa. So yake Mommah ta haƙura, ta yadda da shi ta kuma ba shi matarsa dan wallahi ya yi nadama. Kwata kwata ta kasa sukuni, se gyara zama kawai da take yi. Ita kam ta ga ta kanta. Wai yaushe ya yi wannan muguwar chanjawar? Se kace wanda aka chanja? Gaba ɗaya ya zama wani iri. A hankali kuma se abin da Mommah ta faɗa mata ɗazun a ɗaki suka shiga dawo mata. Kenan da gaske yanzun yana sonta? Yana sonta sosai? Irin son da har za ta iya amfani da shi wajen sauya shi?

"Afrah lafiya kuwa?" Mommah da ta lura da ita ta faɗi haka. Kamar za ta yi kuka tace

"Mommah.." Se kuma ta yi shiru ba tace komai ba. Ganin Mommah na shirin kallansa ne ya sanya shi gyara zamansa ya basar. Se a lokacin Didi ta sauke numfashi. Ita kam har yanzu ba ta san ta ina za ta fara ba. Se take jin tsoron yin abin da Mommahn tace mata ta yi saboda gudun ɓacin rana. Kar ta je ba yanda Mommahn ke tunani ba ne ita kuma ta zo ta zaƙe. Se dai ko ma mene ne za ta yi ƙoƙarin yin hakan ko ma me ze biyo baya. A hankali ya kai hannunsa ze ɗauki ruwan da ke ajje kusa da plate nasa. Iftihal ta yi saurin riƙewa tana faɗin

"Haba.. bari na taimaka maka.." Ta yi maganar cikin muryarta da tafi kama da tsantsar iyayi a cikinta. Cokalin da Lulu ke amfani da shi cikin abincin da ke gabanta tana caccakawa kawai ba tare da ta kai ko loma ɗaya ba ne ta dakatar lokacin da ta ji abin da Iftihal ɗin ta faɗa. Haka nan kawai ta ji tana son ganin da wanda take. Ba ma ita kaɗai ba hatta Mommah da Didi se da suka ɗaga kai suka kalleta. Daidai lokacin da ta ɗaga idanun nata se suka sauka a kan Iftihal lokacin da take tsiyaya ruwa cikin wani glass cup. Se ta kasa ɗauke idanunta daga kanta. Har zuwa lokacin da Iftihal ta miƙawa Gwani kofin tana faɗin

"Ga shi.." Ta ƙare tana binsa da wani kallo lokaci ɗaya kuma tana sakar masa wani tattausan murmushi..

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO76*

____ Kaasa ɗauke idanunta Lulu ta yi, se ta ji tana son gani ze karɓa ne ko kuwa ya ya? Hannu Gwani ya miƙa ya karɓa bayan ya ɗan yi wani yaƙe saboda murmushin da ya ga tana sakar masa kar ya yarfata.

"Na gode.." Ya yi maganar a nutse. Wani sabon murmushin ta sake saki tana wani buɗe baki tace

"Ahh me ye na godiya kuma Yayana?" Ta ƙarasa maganar tana ɗaukar cokali ta soma cin abincin, murmushi ya ƙi barin fuskarta. Da alama za ta yi nasara a wannan wasan. Yanzu dai duk wani burinta shi ne ta samu numbersa ta ƙarasa ragowar aikin ko da a gida ne. Ba ta san lokacin da ta sauke idanunta da sauri ba tana jin yanda zuciyarta ta shiga harbawa. A hankali kuma bugun zuciyarta ya soma saituwa, mamaki na kamata. Me ye musabbabin hakan? Tun da ta sauke idanunta ƙasa har suka gama dinner ba ta sake ɗagowa ba. Duk kuwa da tana jin magana sama sama amma ta kasa ɗaga idanunta. Duk yana lura da ita, hatta abincin da ba ta ci ba duk yana lura da ita. Be kawo komai a ransa ba, ya ɗauka ko abincin ne be mata ba.

"Afaaf me za a dafa miki?" Mommah ta tambaya tana kallanta. Se a lokacin sannan ta ɗaga kai ta kalleta ta girgiza kai kafin tace

"Na ƙoshi."

"Ya za ki ce kin ƙoshi? Me kika ci?"

"Ba komai amma na ƙoshi."

"Ba ki isa ba.. Je ki ɗaki zuwa an jima zan aiko kiranki." Kamar jira take, ta tura kujerar da take kai baya ta miƙe ta wuce ɗaki ba tare da ta kalli kowa ba. Binta da kallo Gwani ya yi yana mamakin abin da ya chanjata haka cikin ƙanƙanin lokaci.

.. Washegari tun safe Mommah ta ɗauki Lulu da Didi suka fice daga gidan, ba su suka dawo ba se wajen ƙarfe 3. Daidai lokacin da suke ƙoƙarin shiga sashen Mommah Gwani da Bad suka ƙaraso.

"Sannunku da zuwa Mommah.." Suka haɗa baki wajen faɗar hakan.

"Yawwah sannunku dai.." Ta amsa da murmushi tana kallansu. Tuni Didi da Lulu sun yi gaba dan sun gaisa da safe. Ita ma Mommah bin bayan nasu ta yi, kafin su Gwani ma suka rufa mata baya. Shi dai Bad a ɗarare yake kar ya je Mommahn tace ya juya, be sani ba damar da aka ba shi ko iya ta jiya ce kawai. Se be ji Mommahn tace komai ba har suka isa palournta.

"Afaaf tsaya ki gaisa da mijinki.. Ke kuma Afrah wuce mu tafi.." Mommah ta yi maganar tana kama hannun Didi suka wuce ɗaki. Kamar wani dolo haka ya bisu da kallo. Ya ɗan runtse idanunsa yana buɗewa a lokaci guda. Shi kam jikinsa gaba ɗaya ya yi sanyi da lamarin. Be san girman laifin da ya aikata babba ba ne se Mommah ta masa abu. Duk soyayyar da take masa ajeta gefe take ta masa abin da ta ga dama. A nutse ya juya ya kalli Gwani yace muryarsa kamar wanda ya ƙware

"Se ka fito." Be jira yace komai ba ya fice daga ɗakin, be kuma nufi ko ina ba se wajen motarsa, ya hau ya fice daga gidan.

"Mu je ki zauna koh?" Gwani ya faɗa yana kallan Lulu. Se a lokacin sannan ta ɗaga ƙafafunta kamar me jin tsoron ƙasa ta shiga takawa. Kan kujera ta zauna har lokacin ba tace komai ba. Shi ma neman waje ya yi ya zauna a gefenta, se dai in da ya san ze din ga ganinta.

"Ki na lafiya?" Tambayar da ya soma mata kenan. A hankali ta ɗan ɗaga kanta ta kalle shi, daidai lokacin da yake kallanta, se idanunsu suka shige cikin na juna. Maimakon a da da daga zarar sun haɗa ido za ta ɗauke nata, yanzu se ta kasa janyewa. Se kace wadda take son karanto wani abun cikin idanunsa. Sun kai wajen minti 1 a haka kafin Lulu ta sauke kai da sauri. Ajiyar zuciya ya sauke yana lumshe idanunsa, ya daɗe be mata irin wannan kallon ba. Yau ɗin da ya mata shi se yake jinsa zam zam. A hankali ya ɗan matsa kusa da ita, ya ɗan rage tazarar dake tsakaninsu. Ya saka hannunsa ya ɗan janye rigar jikinta kafin ya ɗora hannunsa a kan cikinta yace

End of Chapter 99Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next