Ramadan Promo!All users that send a manual request for premium upgrade on sallah day will be granted for 1 month free.
Soyayyanovels
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel
By Billyn Abdul
Login to keep your reading position saved.
Book Page Chapters
A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

A Jini Take Izzata Part Two Complete Hausa Novel

Author: Billyn Abdul
Chapter 31 of 122
About 8 min read
Chapter progress: 0%
Listen Mode
Listen to this chapter using your device voice.
Ready to listen from this chapter.
Free access is active. You can keep reading and download during this access window.

Book chapters

Choose a chapter and continue reading.

Start chapters
Chapter 1 1,645 words Chapter 2 1,690 words Chapter 3 1,680 words Chapter 4 1,637 words Chapter 5 1,676 words Chapter 6 1,594 words Chapter 7 1,597 words Chapter 8 1,655 words Chapter 9 1,192 words Chapter 10 1,647 words Chapter 11 1,678 words Chapter 12 1,698 words Chapter 13 1,656 words Chapter 14 1,617 words Chapter 15 1,693 words Chapter 16 1,658 words Chapter 17 1,692 words Chapter 18 1,521 words Chapter 19 1,684 words Chapter 20 1,600 words Chapter 21 1,688 words Chapter 22 1,589 words Chapter 23 1,692 words Chapter 24 1,344 words Chapter 25 1,685 words Chapter 26 1,699 words Chapter 27 1,685 words Chapter 28 1,660 words Chapter 29 1,664 words Chapter 30 1,468 words Chapter 31 Reading now Chapter 32 1,699 words Chapter 33 1,682 words Chapter 34 1,587 words Chapter 35 1,689 words Chapter 36 1,687 words Chapter 37 1,610 words Chapter 38 1,677 words Chapter 39 1,679 words Chapter 40 1,632 words Chapter 41 1,698 words Chapter 42 1,661 words Chapter 43 1,690 words Chapter 44 1,277 words Chapter 45 1,514 words Chapter 46 1,679 words Chapter 47 1,689 words Chapter 48 1,694 words Chapter 49 1,623 words Chapter 50 1,616 words Chapter 51 1,618 words Chapter 52 1,499 words Chapter 53 1,697 words Chapter 54 1,686 words Chapter 55 1,630 words Chapter 56 1,694 words Chapter 57 1,548 words Chapter 58 1,682 words Chapter 59 1,389 words Chapter 60 1,613 words Chapter 61 1,497 words Chapter 62 1,686 words Chapter 63 1,669 words Chapter 64 1,675 words Chapter 65 1,613 words Chapter 66 1,697 words Chapter 67 1,627 words Chapter 68 1,670 words Chapter 69 1,638 words Chapter 70 1,682 words Chapter 71 1,543 words Chapter 72 1,563 words Chapter 73 1,611 words Chapter 74 1,680 words Chapter 75 1,616 words Chapter 76 1,629 words Chapter 77 1,662 words Chapter 78 1,575 words Chapter 79 1,507 words Chapter 80 1,608 words Chapter 81 1,674 words Chapter 82 1,651 words Chapter 83 1,516 words Chapter 84 1,631 words Chapter 85 1,699 words Chapter 86 1,652 words Chapter 87 1,633 words Chapter 88 1,651 words Chapter 89 1,674 words Chapter 90 1,606 words Chapter 91 1,688 words Chapter 92 1,593 words Chapter 93 1,654 words Chapter 94 1,396 words Chapter 95 1,655 words Chapter 96 1,599 words Chapter 97 1,693 words Chapter 98 1,665 words Chapter 99 1,653 words Chapter 100 1,658 words Chapter 101 1,700 words Chapter 102 1,639 words Chapter 103 1,651 words Chapter 104 1,671 words Chapter 105 1,547 words Chapter 106 1,695 words Chapter 107 1,585 words Chapter 108 1,675 words Chapter 109 1,641 words Chapter 110 1,674 words Chapter 111 1,509 words Chapter 112 1,615 words Chapter 113 1,674 words Chapter 114 1,691 words Chapter 115 1,694 words Chapter 116 1,688 words Chapter 117 1,681 words Chapter 118 1,656 words Chapter 119 1,670 words Chapter 120 1,698 words Chapter 121 1,689 words Chapter 122 1,691 words

.. Har wajen ƙarfe 9 na safe babu Didi babu dalilinta, ya yi tsammanin zuwanta tun ɗazu amma har yanzu shiru. Ya ja tsaki a karo na barkatai yana tunanin kalan rashin darajar da ze mata. Kenan iskanci ne ya hanata zuwa tunda dai har ya bada saƙo a bata, ita wace ce da ze sakata yin wani abu ta ƙi yi? Jinjina kai ya yi yana kama lips ɗinsa na ƙasa ya shigar da shi cikin bakinsa ya ɗan tauna yana neman waje ya zauna. A karo na babu adadi ya sake jan tsaki yana miƙewa a fusace ya fice daga ɗakin. Bin inda yake da tabbacin nan ne da mutum a ciki ya yi yana yatsine fuska. A nutse se dai cike da kuzari, mazantaka da kuma wani irin kyawu ko a tafiyar tasa ya shiga takawa zuwa ƙofar ɗakin. Babu jira ya saka hannunsa ya tura ƙofar ɗakin idanunsa a cikin ɗakin yana tunanin ta inda ze ganta. Tana kwance a kan gado ta ji motsin buɗe ƙofar ba kuma irin na Baba Atine ko Mommah ba. Hakan ne ya sanyata ɗagowa dan ganin wanda ya yi hakan. Tozali da shi da ta yi se da ya wani irin kaɗa mata 'ya'yan hanji, ta tashi zaune a zabure tana kallan yanda yake watsa mata wani irin kallo da ta gaza gane inda za ta ajje shi. Cigaba da takawa ya yi zuwa cikin ɗakin, ya yin da ta ji wani irin rauni ya ziyarceta. Se ta soma ƙoƙarin tashi a miliyan dan barin ɗakin, ya katseta da faɗin

"Hey young lady.. Me ke a cikin kanki? Kina da motsi ne?" Ya faɗa without minding yanda maganar za ta mata. Ita ba ma ta wani fahimci abin da ya faɗa ba saboda ruɗewa da ganinsa cikin ɗakin, abin da ba ta taɓa gani ba.

"Am i ur mate?" Ya tambaya yana kallanta. Da sauri ta jinjina kai tana jiran jin abin da ze sake fitowa daga cikin bakinsa.

"Me ya hana ki kawo min Coffee?" Inda inda ta soma yi dan ba ta da amsar bayarwa, dan kuwa tana sane ta ƙi yi ba tare da wani dalili ba. Kafin tace komai yace

"Kafin lokacin zamanki ya ƙare a gidan nan zan faɗa miki abin da za ki dinga yi.." ya ɗan dakata a nan, lumsassun idanunsa sun ɗan sake lumshewa kamar me jin bacci

"Ƙarfe 8 ki tabbatar kin kawo na safe.. And na dare ma hakan take.. Idan kika kuma yin tsallake ba ki yi ba wallahi zan fito miki na nuna miki waye ni.. Kin ji?" Ya ƙare da sigar tambaya. Da sauri Didi ta jinjina kai dan kasancewarsa a wajen duk shi ne ya ruɗata. Ga yanda yake magana kamar ze kai mata duka. Ita ta kasa gane dalilin da yasa har yanzu idan ta ji muryarsa se ta ji tana mata kama da wata muryar, amma har yanzu ta kasa ganewa. Bata ankara ba se nemarsa ta yi cikin ɗakin ta rasa har ya fice.

"Wayyo Allah na.." ta faɗa tana dafe ƙirjinta. A fili ta cigaba da faɗin

"Da kana jin daɗinsa amma girman kai ya hanaka faɗa? Yacin da ba ka faɗa ba se dai ka bushe ba zan kuma yi ba." Ta ƙare tana murguɗa baki.

... "Ka yi haƙuri Hero ina ganin kawai mu ƙare wannan harkar yanzun nan, na gaji wallahi. Na gaji da saka kuɗina da amfani da jikina duk dan ganin na samu yarinyar nan, amma kullum sake yin wani abun da ze nisantani da ita ne ke faruwa."

"Kin ga ki fito min a mutum kawai.. me kike nufi?" Ya tambaya yana kallanta da wani irin kallo.

"Na haƙura. Ba zan iya cigaba da wannan harkar ba. Ka yi haƙuri kawai.." Dariyar yaƙe Hero ya yi yana kallanta hannunsa a kan gemunsa yana shafawa.

"Kike cewa me? Kwantar da hankalinki.. ko da kin rabu da wannan maganar tana nan tare dake, don wallahi ba ki isa ki bar ni a ruwa ni kaɗai ba. Se da na gama yin burgima na yi nashe_nashe cikin wannan harƙallar sannan za ki ce kin haƙura? Yanda aka farata dake har kika janyo ni cikinta, haka za a cigaba da tafiya. Kin saka na rungume yarinya babu gaira babu dalili, na ɓata da abokina duk a kan ki, kin saka na yadda an haɗa baki da ni wajen ɓatawa yarinyar nan suna. Sannan kuma yanzu ki zo ki ce min kin haƙura? Ba ki isa ba wallahi, idan kuma ba haka ba uban kowa ma ya mutu.. wallahi ki tabbatar duk lokacin da lamarin nan ya caɓe ki shirya karɓar gaba ɗaya laifukan da na aikata, dan kuwa wallahi babu abin da ya dame ni tona miki asiri zan yi, kar ki wani duba muna mutunci, babu ruwana.."

A yi manage da wannan pls ☹️ wallahi bacci nake ji.☹️

✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO40*

__Tsayawa Ladi ta yi tana kallan Hero jin abin da ya faɗa. Kafin ta kai ga cewa komai ya sake faɗin

"Tabbatar min da da gasken kike kin haƙura?" Ya yi maganar yana kallanta. Gyara zamanta ta yi tace bayan ta sauke ajiyar zuciya

"Ya zan yi Hero? Wallahi da gaske na haƙura.. Idan kuma za ka sama min damar da zan je har cikin gidan nata toh hakan ya min. Tunda dai na ga ba fitowa za ta yi ba. Bar wannan ma idan ta fito ɗin abin da nake tsarawa be yiwu ba fa?" Ta ƙare da sigar tambaya. Dariyar gefen baki ya yi duk da a fusace yake yace

"Kin ɗauka ni yaron ki ne ko Ladi? Wallahi daga yau na gama yi miki aiki.. A je a kin haƙuran, se anjima." Daga haka ya juya ya fice daga cikin ɗakin. Binsa ta yi da kallo kamar za ta bi shi ta masa magana se kuma ta fasa, dan idan ita ze nunawa duniyanci ita ma gwana ce a wajen, dan za ta iya cewa ita degree ne ma da ita a wannan fannin. Hakan ne ya sanyata jan tsaki a fili ta furta

"Ka daɗe ba ka yi fushin ba.. Haba.." ta ƙare tana tauna chewing gum ɗin bakinta yana ba da sautin "ƙaras"

... Ko da ta idar da Sallah kai tsaye banɗakin ta faɗa ta yi wanka da ruwan da ta jona a heater. Har zuwa lokacin ta kasa dena tunanin abin da ya faru, ta kasa dena tunanin wanda ya aikata mata haka, ta kuma kasa dena kuka, wanda shi ne musabbabin saka mata ciwon kan da ta tashi da shi. Har zuwa lokacin da ta gama shiryawa be shigo ɗakin ba, karon farko ta ji ya kamata ta fita ta je ta gaida Ummeey ba se ya sakata ta yi hakan ba. Dan haka se ta fice zuwa ɗakin Ummeeyn tana ɗan lumshe idanunta saboda ciwon da kanta yake mata, ga shi kuma har lokacin cikinta be dena mata ciwo ba. Cikin siririyar dashashshiyar muryarta ta yi sallama cikin ɗakin, Ummeey da Gwani suka amsa sallamar tata. Ƙarasawa ta yi ta nemi waje ta zauna a hankali tace kanta a ƙasa

"Barka da wannan lokaci.."

"Barka dai ɗiyata.. ya jikin naki?" Ummeey ta faɗa fuskarta ɗauke da murmushi.

"Alhamdulillah.." Lulu ta amsa da hakan. Haka kawai ya tsinci kansa da mamakinta, wanda har se da ya kalleta kamar me son gane da gasken ita ce? Se dai be ƙare mamakin ba, ya tsinto muryarta tana faɗin

"Ina kwana?" Ta faɗa a raunane cike da matsananciyar kunya. Dan tunda ta zo gidan ba ta taɓa ko da kuskuren gaishe da shi ba. Se dai yau ɗin se ta kasa yin shiru, ta kasa ɗauke kai ba tare da ta gaishe shi ba. Cigaba ya yi da kallanta da mamaki kwance a kan fuskarsa. Se dai tuna a inda suke ya sanya shi amsa gaisuwar tata lokaci ɗaya yana miƙewa.

"Ka tashi kenan?" Ummeey ta tambaya tana kallansa.

"Ehh.. bari na je" ya bata amsa.

"Toh ba damuwa.." Ummeey ta faɗa, shi kuma ya fice daga ɗakin.

Yau ɗin kawai se ta ji tana son cigaba da zama a ɗakin Ummeeyn, hakan ne ya sanyata cigaba da zama har kusan azahar. Se dai har zuwa lokacin ta kasa saka komai a bakinta. Hankalinta gaba ɗaya ya ƙi kwanciya har lokacin, so take ta ji Gwani yace mata ya binciko gaskiyar al'amarin nan. Ba ta jin idan dai har hakan be faru ba hankalinta ze iya kwanciya.

Wajen ƙarfe 3 Ummeey ta shigo ɗakin, ta ƙarasa ta buɗe kwanan da ta zubo mata shinkafa da miya. Kamar yanda ta tsammata kuwa yana nan yanda yake ba a taɓa komai ba.

"Afaaf.." Ummeey ta kira sunanta tana kallanta. Idanunta dake a lumshe ta buɗe lokacin da suka chanja kala.

"Subhanallahi.. jikin ne dai?" Ummeey ta faɗa tana matsowa kusa da ita. Jinjina kai kawai ta yi saboda yanda kanta ke wani irin juyawa. Taɓa jikinta Ummeey ta yi ta ji zafi zau, ta girgiza kai tana faɗin

"Ya salaam.. Sannu kin ji. Tashi mu je ɗakin naki ai akwai maganin da kuka siyo jiya." Ummeey ta yi maganar kamar tambaya se dai ba jiran amsar Lulun take yi ba. Kwata kwata jikinta babu ƙwari, hakan ne ya sa se da Ummeey ta kamata sannan ta miƙar da ita. Kai tsaye ɗakin Gwanin ta nufa har lokacin riƙe take da hannunta. A kan gadon ta zaunar da ita tana ta jera mata uban sannu, ita kam Lulu babu baki, gaba ɗaya ya mutu. Zamewa ta yi ta kwanta a kan gadon saboda duk da yanda take a zaune amma jiri take ji. Duba maganin Ummeey ta yi ta ɗakko shi, ta fito da shi. Ta fita ta ɗebo ruwa sannan ta dawo dan ɓallo mata ta sha. Se dai tana duba fuskar Lulun se ta ga har bacci ya ɗauketa. Tausayinta ya kamata, ta girgiza kai tana faɗin

"Allah sarki.." Se kawai ta ajje maganin ta ja mata zanin gadon ta lulluɓeta da shi sannan ta fice daga ɗakin.

End of Chapter 31Continue to the next chapter or choose another story below.

More Hausa novels

Browse all books →
Previous Login to Save Next